< Farawa 46 >

1 Saboda haka Isra’ila ya kama hanya da dukan abin da yake nasa, sa’ad da ya kai Beyersheba, sai ya miƙa hadayu ga Allah na Ishaku, mahaifinsa.
Востав же Израиль сам и вся сущая его, прииде ко кладязю Клятвенному и пожре жертву Богу отца своего Исаака.
2 Allah kuwa ya yi magana ga Isra’ila a wahayi da dare ya ce, “Yaƙub! Yaƙub!” Yaƙub kuwa ya amsa ya ce, “Ga ni.”
Рече же Бог ко Израилю в видении нощию, глаголя: Иакове, Иакове. Он же рече: что есть?
3 Sai Allah ya ce, “Ni ne Allah, Allah na mahaifinka. Kada ka ji tsoron zuwa Masar, gama zan mai da kai al’umma mai girma a can.
Он же рече ему: Аз есмь Бог отцев твоих, не убойся изыти во Египет: в язык бо велий сотворю тя тамо:
4 Zan gangara zuwa Masar tare da kai, tabbatacce zan sāke dawo da kai. Kuma hannun Yusuf zai rufe idanunka.”
и Аз сниду с тобою во Египет, и Аз возведу тя до конца: и Иосиф возложит руки своя на очи твои.
5 Sa’an nan Yaƙub ya bar Beyersheba,’ya’yan Isra’ila maza, suka ɗauki mahaifinsu Yaƙub da’ya’yansu da matansu a cikin wagonun da Fir’auna ya aika don a kawo shi.
Воста же Иаков от кладязя Клятвеннаго, и взяша сынове Израиля отца своего, и стяжание, и жены своя на колесницы, яже посла Иосиф, взяти его:
6 Suka kuma ɗauki dabbobinsu da mallakarsu, da suka samu a Kan’ana, Yaƙub kuwa da dukan zuriyarsa suka tafi Masar.
и вземше имения своя и все стяжание, еже стяжаша в земли Ханаанстей, внидоша во Египет Иаков и все семя его с ним:
7 Ya ɗauki’ya’yansa maza da jikokinsa da’ya’yansa mata da jikokinsa mata, dukan zuriyarsa zuwa Masar.
сынове и сынове сынов его с ним, дщери и дщери дщерей его, и все семя свое введе во Египет.
8 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza (Yaƙub da zuriyarsa) waɗanda suka tafi Masar, Ruben ɗan farin Yaƙub.
Сия же имена сынов Израилевых вшедших во Египет купно со Иаковом отцем своим: Иаков и сынове его: первенец Иаковль Рувим.
9 ’Ya’yan Ruben maza su ne, Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.
Сынове же Рувимли: Енох и Фаллос, Асрон и Харми.
10 ’Ya’yan Simeyon maza su ne, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar da Sha’ul ɗan mutuniyar Kan’ana.
Сынове же Симеони: Иемуил и Иамин, и Аод и Ахин, и Саар и Саул, сын Хананитидин.
11 ’Ya’yan Lawi maza su ne, Gershon, Kohat da Merari.
Сынове же Левиини: Гирсон, Кааф и Мерарий.
12 ’Ya’yan Yahuda maza su ne, Er, Onan, Shela, Ferez da Zera (amma Er da Onan sun mutu a ƙasar Kan’ana).’Ya’yan Ferez maza su ne, Hezron da Hamul.
Сынове же Иудины: Ир и Авнан, и Силом и Фарес и Зара: умроша же Ир и Авнан в земли Ханаани. Быша же сынове Фаресу: Есром и Иемуил.
13 ’Ya’yan Issakar maza su ne, Tola, Fuwa, Yoshub da Shimron.
Сынове же Иссахаровы: Фола и Фуа, и Асум и Самвран.
14 ’Ya’yan Zebulun maza su ne, Sered, Elon da Yaleyel.
Сынове же Завулони: Серед и Аллон и Ахоил.
15 Waɗannan su ne’ya’yan Liyatu maza da ta haifa wa Yaƙub a Faddan Aram, ban da’yarsa Dina.’Ya’yansa maza da mata duka, mutum talatin da uku ne.
Сии сынове Лиини, ихже роди Иакову в Месопотамии Сирстей, и Дину дщерь его: всех душ сынов и дщерей тридесять три.
16 ’Ya’yan Gad maza su ne, Zafon, Haggi, Shuni, Ezbon, Eri, Arodi da Areli.
Сынове же Гадовы: Сафон и Ангис, и Саннис и Фасован, и Аидис и Ароидис и Ареилис.
17 ’Ya’yan Asher maza su ne, Imna, Ishba, Ishbi da Beriya.’Yar’uwarsu ita ce Sera.’Ya’yan Beriya maza su ne, Heber da Malkiyel.
Сынове же Асировы: Иемна и Ессуа, и Иеул и Вариа, и Сара сестра их. Сынове же Вариины: Ховор и Мелхиил.
18 Waɗannan su ne’ya’yan da Zilfa ta haifa wa Yaƙub, ita ce Laban ya ba wa’yarsa Liyatu.’Ya’yan duka, su sha shida ne.
Сии сынове Зелфины, юже даде Лаван Лии, дщери своей, яже роди сих Иакову, шестьнадесять душ.
19 ’Ya’yan Yaƙub maza waɗanda Rahila ta haifa su ne, Yusuf da Benyamin.
Сынове же Рахили, жены Иаковли: Иосиф и Вениамин.
20 A Masar, Asenat’yar Fotifera, firist na On ta haifi Manasse da Efraim wa Yusuf.
Быша же сынове Иосифу в земли Египетстей, ихже роди ему Асенефа, дщи Петефриа жреца Илиопольска, Манассию и Ефрема. Быша же сынове Манассиины, ихже роди ему наложница Сира, Махира. Махир же роди Галаада. Сынове же Ефраима, брата Манассиина: Суталаам и Таам. Сынове же Суталаамли, Едом.
21 ’Ya’yan Benyamin maza su ne, Bela, Beker, Ashbel, Gera, Na’aman, Ehi, Rosh, Muffim, Huffim da Ard.
Сынове же Вениамини: Вала и Ховор и Асфил. Быша же сынове Валовы: Гира и Ноеман, и Анхис и Рос, и Мамфим и Офимим. Гира же роди Арада.
22 Waɗannan su ne’ya’yan Rahila maza waɗanda ta haifa wa Yaƙub, dukansu mutum goma sha huɗu ne.
Сии сынове Рахилины, ихже роди Иакову, всех душ осмьнадесять.
23 Yaron Dan shi ne, Hushim.
Сынове же Дановы: Асом.
24 ’Ya’yan Naftali maza su ne, Yazeyel, Guni, Yezer da Shillem.
Сынове же Неффалимли: Асиил и Гони, и Иссаар и Селлим.
25 Waɗannan su ne’ya’ya mazan da Bilha ta haifa wa Yaƙub, ita ce Laban ya ba wa’yarsa Rahila.’Ya’yan suka su bakwai ne.
Сии сынове Валлины, юже даде Лаван Рахили дщери своей, яже роди сих Иакову: всех душ седмь.
26 Dukan waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub, waɗanda suke zuriyarsa kai tsaye ban da matan’ya’yansa maza, su mutum sittin da shida ne.
Всех же душ вшедших со Иаковом во Египет, яже изыдоша из чресл его, кроме жен сынов Иаковлих, всех душ шестьдесят шесть.
27 In aka haɗa da’ya’yan nan maza guda biyu waɗanda aka haifa wa Yusuf a Masar, membobin iyalin Yaƙub, waɗanda suka tafi Masar, duka su saba’in ne.
Сынове же Иосифовы, иже быша ему в земли Египетстей, душ девять: всех душ дому Иаковля, яже приидоша со Иаковом во Египет, душ седмьдесят пять.
28 To, Yaƙub ya aiki Yahuda yă yi gaba yă sadu da Yusuf, don yă nuna musu hanyar da za su bi zuwa yankin Goshen. Da suka isa yankin Goshen,
Иуду же посла пред собою ко Иосифу срести его у Иройска града в земли Рамессийстей.
29 sai Yusuf ya kintsa keken yaƙinsa ya haura zuwa Goshen don yă taryi mahaifinsa, Isra’ila. Nan da nan da isowar Yusuf a wurin mahaifinsa, sai ya rungumi mahaifinsa, ya yi kuka na dogon lokaci.
Впряг же Иосиф колесницы своя, изыде во сретение Израилю, отцу своему, ко Ироону граду: и явився ему, нападе на выю его и плакася плачем великим.
30 Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Yanzu ina a shirye in mutu, da yake na gani da kaina cewa har yanzu kana da rai.”
И рече Израиль ко Иосифу: да умру отныне, понеже видех лице твое: еще бо ты еси жив.
31 Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa da gidan mahaifinsa, “Zan haura in yi magana da Fir’auna, zan kuwa ce masa, ‘’Yan’uwana da gidan mahaifina, waɗanda suke zaune a ƙasar Kan’ana, sun zo wurina.
Рече же Иосиф ко братии своей: шед повем фараону и реку ему: братия моя и дом отца моего, иже быша в земли Ханаани, приидоша ко мне:
32 Mutanen fa, makiyaya ne; suna kiwon dabbobi, sun kuma zo tare da garkunansu da shanunsa da kuma kome da suka mallaka.’
они же суть мужие пастуси, мужие бо скотопитателие быша: и скоты, и волы, и вся своя приведоша:
33 Sa’ad da Fir’auna ya kira ku ciki, ya yi tambaya, ‘Mece ce sana’arku?’
аще убо призовет вас фараон и речет вам: что дело ваше есть?
34 Ku amsa, ‘Bayinka suna kiwon dabbobi ne, tun muna samari har zuwa yanzu, kamar yadda kakanninmu suka yi.’ Ta haka za a bar ku ku zauna a yankin Goshen, gama Masarawa suna ƙyamar makiyaya.”
Рцыте: мужие скотопитателие есмы, раби твои, издетска даже до ныне, и мы и отцы наши: да вселитеся в земли Гесем аравийстей: мерзость бо есть Египтяном всяк пастух овчий.

< Farawa 46 >