< Farawa 46 >

1 Saboda haka Isra’ila ya kama hanya da dukan abin da yake nasa, sa’ad da ya kai Beyersheba, sai ya miƙa hadayu ga Allah na Ishaku, mahaifinsa.
HELE mai la o Iseraela me kana mau mea a pau loa, a hiki mai la i Beereseba, a mohai aku la ia i na mohai i ke Akua o kona makuakane o Isaaka.
2 Allah kuwa ya yi magana ga Isra’ila a wahayi da dare ya ce, “Yaƙub! Yaƙub!” Yaƙub kuwa ya amsa ya ce, “Ga ni.”
Olelo mai la ke Akua ia Iseraela ma ka hihio i ka po, i mai la, E Iakoba, e Iakoba. I aku la keia, Eia no wau.
3 Sai Allah ya ce, “Ni ne Allah, Allah na mahaifinka. Kada ka ji tsoron zuwa Masar, gama zan mai da kai al’umma mai girma a can.
I mai la kela, Owau no ke Akua, o ke Akua o kou makuakane: mai makau oe ke iho ilalo i Aigupita; no ka mea, e hoolilo au ia oe i lahuikanaka nui malaila.
4 Zan gangara zuwa Masar tare da kai, tabbatacce zan sāke dawo da kai. Kuma hannun Yusuf zai rufe idanunka.”
A e iho pu aku no au me oe i Aigupita; e oiaio no hoi, e lawe hou mai au ia oe malaila mai, a e kau no o Iosepa i kona lima ma kou mau maka.
5 Sa’an nan Yaƙub ya bar Beyersheba,’ya’yan Isra’ila maza, suka ɗauki mahaifinsu Yaƙub da’ya’yansu da matansu a cikin wagonun da Fir’auna ya aika don a kawo shi.
Ala mai la o Iakoba mai Beereseba mai, a lawe ae la na keiki a Iseraela ia Iakoba, ko lakou makuakane, a me na kamalii, a me ka lakou mau wahine maluna o na kaa a Parao i hoouna aku ai e lawe ia lakou.
6 Suka kuma ɗauki dabbobinsu da mallakarsu, da suka samu a Kan’ana, Yaƙub kuwa da dukan zuriyarsa suka tafi Masar.
Lawe ae la lakou i ka lakou mau holoholona, a me ka waiwai a lakou i loaa ai ma ka aina ma Kanaana, a hele mai i Aigupita; o Iakoba, lakou pu me na keiki ana a pau:
7 Ya ɗauki’ya’yansa maza da jikokinsa da’ya’yansa mata da jikokinsa mata, dukan zuriyarsa zuwa Masar.
O kana mau keikikane, a me ka lakou mau keikikane me ia, o kana mau kaikamahine, a me na kaikamahine a kana mau keikikane, a me kana mau hua a pau kana i lawe pu mai ai me ia i Aigupita.
8 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza (Yaƙub da zuriyarsa) waɗanda suka tafi Masar, Ruben ɗan farin Yaƙub.
Eia na inoa o na keikikane a Iseraela i hele i Aigupita; o Iakoba a me kana mau keikikane: o Reubena, ka Iakoba makahiapo.
9 ’Ya’yan Ruben maza su ne, Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.
A o na keikikane a Reubena; o Hanoka, o Palu, o Hezerona, a o Karemi.
10 ’Ya’yan Simeyon maza su ne, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar da Sha’ul ɗan mutuniyar Kan’ana.
O na keikikane a Simeona; o Iemuela, o Iamina, o Ohada, o Iakina, o Zohara, a o Saula, ke keiki a kekahi wahine no Kanaana.
11 ’Ya’yan Lawi maza su ne, Gershon, Kohat da Merari.
O na keikikane a Levi; o Geresona, o Kohata, a o Merari.
12 ’Ya’yan Yahuda maza su ne, Er, Onan, Shela, Ferez da Zera (amma Er da Onan sun mutu a ƙasar Kan’ana).’Ya’yan Ferez maza su ne, Hezron da Hamul.
O na keikikane a Iuda; o Era, o Onana, o Sela, o Pareza, a o Zara: aka, make iho la o Era laua o Onana ma ka aina o Kanaana. A o na keikikane a Pareza; o Hezerona a o Hamula.
13 ’Ya’yan Issakar maza su ne, Tola, Fuwa, Yoshub da Shimron.
O na keikikane a Isakara; o Tola, o Puva, o Ioba a o Simerona.
14 ’Ya’yan Zebulun maza su ne, Sered, Elon da Yaleyel.
O na keikikane a Zebuluna; o Sereda, o Elona a o Iahelela.
15 Waɗannan su ne’ya’yan Liyatu maza da ta haifa wa Yaƙub a Faddan Aram, ban da’yarsa Dina.’Ya’yansa maza da mata duka, mutum talatin da uku ne.
O lakou na keikikane a Lea, ana i hanau ai na Iakoba ma Padanarama, a me kana kaikamahine o Dina: o kana poe keikikane a pau a me na kaikamahine, he kanakolukumamakolu o lakou.
16 ’Ya’yan Gad maza su ne, Zafon, Haggi, Shuni, Ezbon, Eri, Arodi da Areli.
O na keikikane a Gada; o Zipiona, o Hagi, o Suni, o Ezebona, o Eri, o Arodi, a o Areli.
17 ’Ya’yan Asher maza su ne, Imna, Ishba, Ishbi da Beriya.’Yar’uwarsu ita ce Sera.’Ya’yan Beriya maza su ne, Heber da Malkiyel.
O na keikikane a Asera; o Iimena, o Isua, o Isui, o Beria, a o Sera ko lakou kaikuwahine: a o na keikikane a Beria; o Hebera, a o Malekiela,
18 Waɗannan su ne’ya’yan da Zilfa ta haifa wa Yaƙub, ita ce Laban ya ba wa’yarsa Liyatu.’Ya’yan duka, su sha shida ne.
O lakou na keikikane a Zilepa, a Labana i haawi aku ai i kana kaikamahine ia Lea: a o lakou kana i hanau ai na Iakoba, he poe umikumamaono.
19 ’Ya’yan Yaƙub maza waɗanda Rahila ta haifa su ne, Yusuf da Benyamin.
O na keikikane a Rahela a ka wahine na Iakoba: o Iosepa, a o Beniamina.
20 A Masar, Asenat’yar Fotifera, firist na On ta haifi Manasse da Efraim wa Yusuf.
A ua hanau na Iosepa ma ka aina o Aigupita, o Manase a o Eperaima, a Asenata a ke kaikamahine na Potipera ke kahuna no Ona, i hanau ai nana.
21 ’Ya’yan Benyamin maza su ne, Bela, Beker, Ashbel, Gera, Na’aman, Ehi, Rosh, Muffim, Huffim da Ard.
A o na keikikane a Beniamina; o Bela, o Bekera, o Asebela, o Gera, o Naamana, o Ehi, o Rosa, o Mupima, o Hupima, a o Areda.
22 Waɗannan su ne’ya’yan Rahila maza waɗanda ta haifa wa Yaƙub, dukansu mutum goma sha huɗu ne.
O lakou na keiki a Rahela i hanau na Iakoba: a o lakou a pau, he umikumamaha.
23 Yaron Dan shi ne, Hushim.
O na keikikane a Dana; o na Husima.
24 ’Ya’yan Naftali maza su ne, Yazeyel, Guni, Yezer da Shillem.
O na keiki a Napetali; o Iahezela, o Guni, o Iezera, a o Silema.
25 Waɗannan su ne’ya’ya mazan da Bilha ta haifa wa Yaƙub, ita ce Laban ya ba wa’yarsa Rahila.’Ya’yan suka su bakwai ne.
O lakou na keikikane a Bileha, a Labana i haawi aku ai na Rahela na kana kaikamahine; a hanau mai la oia ia laua na Iakoba: a o lakou a pau, ehiku lakou.
26 Dukan waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub, waɗanda suke zuriyarsa kai tsaye ban da matan’ya’yansa maza, su mutum sittin da shida ne.
O na kanaka a pau i hele pu me Iakoba i Aigupita, o ka poe mai loko mai o kona puhaka; kanaono lakou, a me kumamaono, aole hoi i heluia na wahine a kana mau keiki.
27 In aka haɗa da’ya’yan nan maza guda biyu waɗanda aka haifa wa Yusuf a Masar, membobin iyalin Yaƙub, waɗanda suka tafi Masar, duka su saba’in ne.
A o na keiki a Iosepa, i hanauia nana ma Aigupita, elua laua. O na kanaka a pau ma ka hale o Iakoba i hele mai i Aigupita, kanahiku lakou.
28 To, Yaƙub ya aiki Yahuda yă yi gaba yă sadu da Yusuf, don yă nuna musu hanyar da za su bi zuwa yankin Goshen. Da suka isa yankin Goshen,
A hoouna aku la oia ia Iuda, mamua ona io Iosepa la, e kuhiknhi aku mamua ona i Gosena; a hiki mai la lakou i ka aina o Gosena.
29 sai Yusuf ya kintsa keken yaƙinsa ya haura zuwa Goshen don yă taryi mahaifinsa, Isra’ila. Nan da nan da isowar Yusuf a wurin mahaifinsa, sai ya rungumi mahaifinsa, ya yi kuka na dogon lokaci.
A hoomakaukau ae la o Iosepa i ke kaa ona, pii aku la ia e halawai me Iseraela, me kona makuakane i Gosena, a ike aku la oia ia ia, kau iho la ia ma kona a-i, a uwe iho la ma kona a-i, a liuliu wale.
30 Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Yanzu ina a shirye in mutu, da yake na gani da kaina cewa har yanzu kana da rai.”
Olelo aku la o Iseraela ia Iosepa, Ano, e pono ia'u ka make, no kuu ike ana i kou maka, no ka mea, e ola ana oe.
31 Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa da gidan mahaifinsa, “Zan haura in yi magana da Fir’auna, zan kuwa ce masa, ‘’Yan’uwana da gidan mahaifina, waɗanda suke zaune a ƙasar Kan’ana, sun zo wurina.
Olelo aku la o Iosepa i kona poe hoahanau a me ka poe o kona makuakane, E, e pii aku au, e hoakaka aku ia Parao, a e hai aku au ia ia; O ko'u poe hoahanau, a me ka poe o ko'u makuakane i noho ai i ka aina o Kanaana, ua hele mai io'u nei:
32 Mutanen fa, makiyaya ne; suna kiwon dabbobi, sun kuma zo tare da garkunansu da shanunsa da kuma kome da suka mallaka.’
He poe kanaka malama hipa lakou, he poe kanaka hanai holoholona, a ua hele mai lakou me ka lakou hipa, a me ka lakou holoholona, a me ka lakou mea a pau.
33 Sa’ad da Fir’auna ya kira ku ciki, ya yi tambaya, ‘Mece ce sana’arku?’
A hiki i ka wa e hea mai ai o Parao ia oukou, a e ninau mai, Heaha ka oukou oihana?
34 Ku amsa, ‘Bayinka suna kiwon dabbobi ne, tun muna samari har zuwa yanzu, kamar yadda kakanninmu suka yi.’ Ta haka za a bar ku ku zauna a yankin Goshen, gama Masarawa suna ƙyamar makiyaya.”
Alaila, e olelo aku, He poe kanaka hanai holoholona kau mau kauwa nei, mai ka wa kamalii mai, o makou, a me ko makou poe makua: i noho ai oukou ma ka aina, ma Gosena, no ka mea, he haumia i ko Aigupita, na kahuhipa a pau.

< Farawa 46 >