< Farawa 46 >

1 Saboda haka Isra’ila ya kama hanya da dukan abin da yake nasa, sa’ad da ya kai Beyersheba, sai ya miƙa hadayu ga Allah na Ishaku, mahaifinsa.
Israël donc partit avec tout ce qu’il avait, vint au Puits du Serment; et là, des victimes immolées au Dieu de son père Isaac,
2 Allah kuwa ya yi magana ga Isra’ila a wahayi da dare ya ce, “Yaƙub! Yaƙub!” Yaƙub kuwa ya amsa ya ce, “Ga ni.”
Il l’entendit dans une vision de la nuit, l’appelant et lui disant: Jacob, Jacob. Il lui répondit: Me voici.
3 Sai Allah ya ce, “Ni ne Allah, Allah na mahaifinka. Kada ka ji tsoron zuwa Masar, gama zan mai da kai al’umma mai girma a can.
Dieu lui dit: Je suis le Dieu très fort de ton père; ne crains point, descends en Égypte, parce que je te ferai père d’une grande nation en ce pays.
4 Zan gangara zuwa Masar tare da kai, tabbatacce zan sāke dawo da kai. Kuma hannun Yusuf zai rufe idanunka.”
Moi-même je descendrai là avec toi, et moi-même je t’en ramènerai, lorsque tu en reviendras: et Joseph posera ses mains sur tes yeux.
5 Sa’an nan Yaƙub ya bar Beyersheba,’ya’yan Isra’ila maza, suka ɗauki mahaifinsu Yaƙub da’ya’yansu da matansu a cikin wagonun da Fir’auna ya aika don a kawo shi.
Jacob donc se leva du Puits du Serment, et ses fils le portèrent avec leurs petits enfants et leurs femmes sur les chars que Pharaon avait envoyés pour transporter le vieillard.
6 Suka kuma ɗauki dabbobinsu da mallakarsu, da suka samu a Kan’ana, Yaƙub kuwa da dukan zuriyarsa suka tafi Masar.
Et tout ce qu’il possédait dans la terre de Chanaan: il arriva donc en Égypte avec toute sa lignée,
7 Ya ɗauki’ya’yansa maza da jikokinsa da’ya’yansa mata da jikokinsa mata, dukan zuriyarsa zuwa Masar.
Ses fils, ses petits-fils, ses filles et toute sa race ensemble.
8 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza (Yaƙub da zuriyarsa) waɗanda suka tafi Masar, Ruben ɗan farin Yaƙub.
Or voici les noms des fils d’Israël, qui entrèrent en Égypte, lorsqu’il vint avec ses enfants. Le premier-né était Ruben.
9 ’Ya’yan Ruben maza su ne, Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.
Les fils de Ruben: Hénoch, Phallu, Hesron et Charmi.
10 ’Ya’yan Simeyon maza su ne, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar da Sha’ul ɗan mutuniyar Kan’ana.
Les fils de Siméon: Jamuel, Jamin, Ahod, Jachin, Sohar et Saül fils d’une Chananéenne.
11 ’Ya’yan Lawi maza su ne, Gershon, Kohat da Merari.
Les fils de Lévi: Gerson, Caath et Mérari.
12 ’Ya’yan Yahuda maza su ne, Er, Onan, Shela, Ferez da Zera (amma Er da Onan sun mutu a ƙasar Kan’ana).’Ya’yan Ferez maza su ne, Hezron da Hamul.
Les fils de Juda: Her, Onan, Séla, Pharès et Zara; mais Her et Onan moururent dans le pays de Chanaan. Et naquirent à Pharès, les fils Hesron et Hamul.
13 ’Ya’yan Issakar maza su ne, Tola, Fuwa, Yoshub da Shimron.
Les fils d’Issachar: Thola, Phua, Job et Semron.
14 ’Ya’yan Zebulun maza su ne, Sered, Elon da Yaleyel.
Les fils de Zabulon: Sared, Elon et Jahélel.
15 Waɗannan su ne’ya’yan Liyatu maza da ta haifa wa Yaƙub a Faddan Aram, ban da’yarsa Dina.’Ya’yansa maza da mata duka, mutum talatin da uku ne.
Ce sont là les fils de Lia qu’elle enfanta en Mésopotamie de Syrie, avec Dina sa fille; toutes les âmes de ses fils et de ses filles furent trente-trois.
16 ’Ya’yan Gad maza su ne, Zafon, Haggi, Shuni, Ezbon, Eri, Arodi da Areli.
Les fils de Gad: Séphion, Haggi, Suni, Esébon, Héri, Arodi et Aréli.
17 ’Ya’yan Asher maza su ne, Imna, Ishba, Ishbi da Beriya.’Yar’uwarsu ita ce Sera.’Ya’yan Beriya maza su ne, Heber da Malkiyel.
Les fils d’Aser: Jamné, Jésua, Jessui et Béria, et aussi Sara leur sœur. Les fils de Béria: Héber et Melchiel.
18 Waɗannan su ne’ya’yan da Zilfa ta haifa wa Yaƙub, ita ce Laban ya ba wa’yarsa Liyatu.’Ya’yan duka, su sha shida ne.
Ce sont là les fils de Zelpha que donna Laban à Lia sa fille, et qui les enfanta à Jacob: seize âmes.
19 ’Ya’yan Yaƙub maza waɗanda Rahila ta haifa su ne, Yusuf da Benyamin.
Les fils de Rachel femme de Jacob: Joseph et Benjamin.
20 A Masar, Asenat’yar Fotifera, firist na On ta haifi Manasse da Efraim wa Yusuf.
Et il naquit à Joseph dans la terre d’Égypte des fils que lui enfanta Aseneth, fille de Putiphar, prêtre d’Héliopolis: Manassé et Ephraïm.
21 ’Ya’yan Benyamin maza su ne, Bela, Beker, Ashbel, Gera, Na’aman, Ehi, Rosh, Muffim, Huffim da Ard.
Les fils de Benjamin: Béla, Béchor, Asbel, Géra, Naaman, Echi, Ros, Mophim, Ophim, et Ared.
22 Waɗannan su ne’ya’yan Rahila maza waɗanda ta haifa wa Yaƙub, dukansu mutum goma sha huɗu ne.
Ce sont là les fils de Rachel qu’elle engendra à Jacob: en tout quatorze âmes.
23 Yaron Dan shi ne, Hushim.
Les fils de Dan: Husim.
24 ’Ya’yan Naftali maza su ne, Yazeyel, Guni, Yezer da Shillem.
Les fils de Nephtali: Jasiel, Guni, Jéser et Sallem.
25 Waɗannan su ne’ya’ya mazan da Bilha ta haifa wa Yaƙub, ita ce Laban ya ba wa’yarsa Rahila.’Ya’yan suka su bakwai ne.
Ce sont là les fils de Bala que donna Laban à Rachel sa fille, et qu’elle enfanta à Jacob en tout sept âmes.
26 Dukan waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub, waɗanda suke zuriyarsa kai tsaye ban da matan’ya’yansa maza, su mutum sittin da shida ne.
Toutes les âmes qui entrèrent avec Jacob en Égypte, et qui étaient issues de lui, sans les femmes de ses fils, furent soixante-six;
27 In aka haɗa da’ya’yan nan maza guda biyu waɗanda aka haifa wa Yusuf a Masar, membobin iyalin Yaƙub, waɗanda suka tafi Masar, duka su saba’in ne.
Mais les fils de Joseph qui lui naquirent dans la terre d’Égypte, deux âmes. Toutes les âmes de la maison de Jacob qui entrèrent en Égypte, furent soixante-dix.
28 To, Yaƙub ya aiki Yahuda yă yi gaba yă sadu da Yusuf, don yă nuna musu hanyar da za su bi zuwa yankin Goshen. Da suka isa yankin Goshen,
Or Jacob envoya Juda devant lui vers Joseph, afin qu’on l’avertît, et qu’il vînt à sa rencontre dans la terre de Gessen.
29 sai Yusuf ya kintsa keken yaƙinsa ya haura zuwa Goshen don yă taryi mahaifinsa, Isra’ila. Nan da nan da isowar Yusuf a wurin mahaifinsa, sai ya rungumi mahaifinsa, ya yi kuka na dogon lokaci.
Lorsqu’il y fut arrivé, Joseph, son char attelé, monta au même lieu à la rencontre de son père; et le voyant, il se jeta à son cou, et, au milieu des embrassements, il pleura.
30 Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Yanzu ina a shirye in mutu, da yake na gani da kaina cewa har yanzu kana da rai.”
Et le père dit à Joseph: Maintenant je mourrai joyeux, puisque j’ai vu ta face, et que je te laisse vivant après moi.
31 Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa da gidan mahaifinsa, “Zan haura in yi magana da Fir’auna, zan kuwa ce masa, ‘’Yan’uwana da gidan mahaifina, waɗanda suke zaune a ƙasar Kan’ana, sun zo wurina.
Mais Joseph dit à ses frères et à toute la maison de son père: Je monterai et je porterai la nouvelle à Pharaon, et je lui dirai: Mes frères et la maison de mon père qui étaient dans la terre de Chanaan, sont venus vers moi.
32 Mutanen fa, makiyaya ne; suna kiwon dabbobi, sun kuma zo tare da garkunansu da shanunsa da kuma kome da suka mallaka.’
Ce sont des hommes pasteurs de brebis, et ils ont soin d’élever des troupeaux; leur menu et leur gros bétail et tout ce qu’ils pouvaient avoir, ils l’ont amené avec eux.
33 Sa’ad da Fir’auna ya kira ku ciki, ya yi tambaya, ‘Mece ce sana’arku?’
Lors donc qu’il vous appellera et demandera: Quelle est votre occupation?
34 Ku amsa, ‘Bayinka suna kiwon dabbobi ne, tun muna samari har zuwa yanzu, kamar yadda kakanninmu suka yi.’ Ta haka za a bar ku ku zauna a yankin Goshen, gama Masarawa suna ƙyamar makiyaya.”
Vous répondrez: Nous vos serviteurs, nous sommes des hommes pasteurs depuis notre enfance jusqu’à présent, et nous et nos pères. Or vous direz cela, afin que vous puissiez demeurer dans la terre de Gessen; car les Égyptiens détestent tous les pasteurs de brebis.

< Farawa 46 >