< Farawa 46 >

1 Saboda haka Isra’ila ya kama hanya da dukan abin da yake nasa, sa’ad da ya kai Beyersheba, sai ya miƙa hadayu ga Allah na Ishaku, mahaifinsa.
So Jacob left [Canaan], taking with him all his family and possessions. When they arrived at Beersheba, he offered sacrifices to God, the one whom his father Isaac worshiped.
2 Allah kuwa ya yi magana ga Isra’ila a wahayi da dare ya ce, “Yaƙub! Yaƙub!” Yaƙub kuwa ya amsa ya ce, “Ga ni.”
That night, God called to Jacob in a vision, saying, “Jacob! Jacob!” He replied, “I am here!”
3 Sai Allah ya ce, “Ni ne Allah, Allah na mahaifinka. Kada ka ji tsoron zuwa Masar, gama zan mai da kai al’umma mai girma a can.
God said, “I am God, the one your father worshiped. Do not be afraid to go down to Egypt, because I will give you many descendants, and they will become a great nation there.
4 Zan gangara zuwa Masar tare da kai, tabbatacce zan sāke dawo da kai. Kuma hannun Yusuf zai rufe idanunka.”
I will go down to Egypt with you, and later I will bring [your descendants] back to Canaan again. And Joseph will be with you [MTY] when you die.” [IDM]
5 Sa’an nan Yaƙub ya bar Beyersheba,’ya’yan Isra’ila maza, suka ɗauki mahaifinsu Yaƙub da’ya’yansu da matansu a cikin wagonun da Fir’auna ya aika don a kawo shi.
Jacob left Beersheba, and his sons took their father, their wives, and their children, in the carts that the king had sent for them to travel in.
6 Suka kuma ɗauki dabbobinsu da mallakarsu, da suka samu a Kan’ana, Yaƙub kuwa da dukan zuriyarsa suka tafi Masar.
So Jacob and all his family went to Egypt. They took with them the livestock and all the other possessions that they had acquired in Canaan.
7 Ya ɗauki’ya’yansa maza da jikokinsa da’ya’yansa mata da jikokinsa mata, dukan zuriyarsa zuwa Masar.
Jacob went to Egypt with all his sons and his daughters and grandsons and granddaughters—his whole family.
8 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza (Yaƙub da zuriyarsa) waɗanda suka tafi Masar, Ruben ɗan farin Yaƙub.
(Here is/I will now give you) a list of the names of the members of Jacob’s family who went with him to Egypt: Reuben, Jacob’s oldest son; Reuben’s sons Hanoch, Pallu, Hezron, and Carmi; Simeon and his sons Jemuel, Jamin, Ohad, Jakin, Zohar, and Shaul, who was the son of a Canaan people-group woman; Levi and his sons Gershon, Kohath, and Merari; Judah and his sons, Shelah, Perez, and Zerah (his other sons, Er, and Onan, had died in Canaan); Perez and his two sons Hezron and Hamul; Issachar and his sons Tola, Puah, Jashub, and Shimron; Zebulon and his sons Sered, Elon, and Jahleel; (Those were the sons of Jacob and Leah, and their daughter Dinah, who were born in Paddan-Aram/Mesopotamia: There were 33 of them, altogether.) They had Gad and his sons Zephon, Haggi, Shuni, Ezbon, Eri, Arodi, and Areli; Asher and his sons Imnah, Ishvah, Ishvi, and Beriah; and their sister Serah; Beriah’s sons Heber and Malkiel; (Those were the children and grandchildren of Jacob and Zilpah, the slave girl whom Laban gave to his daughter Leah: There were 16 of them, altogether.) Joseph and Benjamin, the sons of Jacob’s wife Rachel; (Ephraim and Manasseh were Joseph’s two sons. [They did not go down to Egypt] because they were already in Egypt. They were sons of Asenath, the daughter of On, who was the priest in the temple in On [city].) Benjamin and his sons Bela, Beker, Ashbel, Gera, Naaman, Ehi, Rosh, Muppim, Huppim, and Ard; (Those were the sons and grandsons of Rachel and Jacob: There were 14 people altogether.) Dan and his son Hushim; Naphtali and his sons Jahziel, Guni, Jezer, and Shillem. (Those were the sons and grandsons of Jacob and Bilhah, the slave girl whom Laban gave to his daughter Rachel: There were seven people altogether.)
9 ’Ya’yan Ruben maza su ne, Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.
10 ’Ya’yan Simeyon maza su ne, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar da Sha’ul ɗan mutuniyar Kan’ana.
11 ’Ya’yan Lawi maza su ne, Gershon, Kohat da Merari.
12 ’Ya’yan Yahuda maza su ne, Er, Onan, Shela, Ferez da Zera (amma Er da Onan sun mutu a ƙasar Kan’ana).’Ya’yan Ferez maza su ne, Hezron da Hamul.
13 ’Ya’yan Issakar maza su ne, Tola, Fuwa, Yoshub da Shimron.
14 ’Ya’yan Zebulun maza su ne, Sered, Elon da Yaleyel.
15 Waɗannan su ne’ya’yan Liyatu maza da ta haifa wa Yaƙub a Faddan Aram, ban da’yarsa Dina.’Ya’yansa maza da mata duka, mutum talatin da uku ne.
16 ’Ya’yan Gad maza su ne, Zafon, Haggi, Shuni, Ezbon, Eri, Arodi da Areli.
17 ’Ya’yan Asher maza su ne, Imna, Ishba, Ishbi da Beriya.’Yar’uwarsu ita ce Sera.’Ya’yan Beriya maza su ne, Heber da Malkiyel.
18 Waɗannan su ne’ya’yan da Zilfa ta haifa wa Yaƙub, ita ce Laban ya ba wa’yarsa Liyatu.’Ya’yan duka, su sha shida ne.
19 ’Ya’yan Yaƙub maza waɗanda Rahila ta haifa su ne, Yusuf da Benyamin.
20 A Masar, Asenat’yar Fotifera, firist na On ta haifi Manasse da Efraim wa Yusuf.
21 ’Ya’yan Benyamin maza su ne, Bela, Beker, Ashbel, Gera, Na’aman, Ehi, Rosh, Muffim, Huffim da Ard.
22 Waɗannan su ne’ya’yan Rahila maza waɗanda ta haifa wa Yaƙub, dukansu mutum goma sha huɗu ne.
23 Yaron Dan shi ne, Hushim.
24 ’Ya’yan Naftali maza su ne, Yazeyel, Guni, Yezer da Shillem.
25 Waɗannan su ne’ya’ya mazan da Bilha ta haifa wa Yaƙub, ita ce Laban ya ba wa’yarsa Rahila.’Ya’yan suka su bakwai ne.
26 Dukan waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub, waɗanda suke zuriyarsa kai tsaye ban da matan’ya’yansa maza, su mutum sittin da shida ne.
Altogether there were 66 people who were Jacob’s descendants who went to Egypt with him. That number does not include his sons’ wives.
27 In aka haɗa da’ya’yan nan maza guda biyu waɗanda aka haifa wa Yusuf a Masar, membobin iyalin Yaƙub, waɗanda suka tafi Masar, duka su saba’in ne.
Including Jacob and Joseph and Joseph’s two sons who were born in Egypt, there were 70 members of Jacob’s family when they were all there in Egypt.
28 To, Yaƙub ya aiki Yahuda yă yi gaba yă sadu da Yusuf, don yă nuna musu hanyar da za su bi zuwa yankin Goshen. Da suka isa yankin Goshen,
Jacob sent Judah to go ahead of the rest of them to talk with Joseph and ask for directions on how to travel to Goshen. Then [Judah returned to the rest of his family and] they all traveled to the Goshen region. When they arrived there,
29 sai Yusuf ya kintsa keken yaƙinsa ya haura zuwa Goshen don yă taryi mahaifinsa, Isra’ila. Nan da nan da isowar Yusuf a wurin mahaifinsa, sai ya rungumi mahaifinsa, ya yi kuka na dogon lokaci.
Joseph got his chariot ready and went to Goshen to meet his father. When Joseph arrived, he threw his arms around his father’s neck and cried a long time.
30 Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Yanzu ina a shirye in mutu, da yake na gani da kaina cewa har yanzu kana da rai.”
Jacob said to Joseph, “I have seen you and I know that you are still alive! So now I am ready to die.”
31 Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa da gidan mahaifinsa, “Zan haura in yi magana da Fir’auna, zan kuwa ce masa, ‘’Yan’uwana da gidan mahaifina, waɗanda suke zaune a ƙasar Kan’ana, sun zo wurina.
Then Joseph said to his [older] brothers [and younger brother] and to the rest of his father’s family, “I will go to the king and say to him, ‘My [older] brothers [and younger brother] and my father and the rest of his family, who were living in Canaan land, have all come to me.
32 Mutanen fa, makiyaya ne; suna kiwon dabbobi, sun kuma zo tare da garkunansu da shanunsa da kuma kome da suka mallaka.’
The men are all shepherds. They take care of their livestock, and they have brought with them their sheep and goats and cattle, and everything else that they own.’
33 Sa’ad da Fir’auna ya kira ku ciki, ya yi tambaya, ‘Mece ce sana’arku?’
When the king summons you and asks, ‘What work do you do?’
34 Ku amsa, ‘Bayinka suna kiwon dabbobi ne, tun muna samari har zuwa yanzu, kamar yadda kakanninmu suka yi.’ Ta haka za a bar ku ku zauna a yankin Goshen, gama Masarawa suna ƙyamar makiyaya.”
answer him by saying, ‘From the time when we were young, we have taken care of livestock, just as our ancestors did.’ If you tell him that, he will let you live in the Goshen region.” Joseph told them to say that because the people of Egypt despised all shepherds.

< Farawa 46 >