< Farawa 46 >

1 Saboda haka Isra’ila ya kama hanya da dukan abin da yake nasa, sa’ad da ya kai Beyersheba, sai ya miƙa hadayu ga Allah na Ishaku, mahaifinsa.
And Israel, setting out with all that he had, arrived at the Well of the Oath. And sacrificing victims there to the God of his father Isaac,
2 Allah kuwa ya yi magana ga Isra’ila a wahayi da dare ya ce, “Yaƙub! Yaƙub!” Yaƙub kuwa ya amsa ya ce, “Ga ni.”
he heard him, by a vision in the night, calling him, and saying to him: “Jacob, Jacob.” And he answered him, “Behold, here I am.”
3 Sai Allah ya ce, “Ni ne Allah, Allah na mahaifinka. Kada ka ji tsoron zuwa Masar, gama zan mai da kai al’umma mai girma a can.
God said to him: “I am the most strong God of your father. Do not be afraid. Descend into Egypt, for there I will make of you a great nation.
4 Zan gangara zuwa Masar tare da kai, tabbatacce zan sāke dawo da kai. Kuma hannun Yusuf zai rufe idanunka.”
I will descend with you to that place, and I will lead you back from there, returning. Also, Joseph will place his hands over your eyes.
5 Sa’an nan Yaƙub ya bar Beyersheba,’ya’yan Isra’ila maza, suka ɗauki mahaifinsu Yaƙub da’ya’yansu da matansu a cikin wagonun da Fir’auna ya aika don a kawo shi.
Then Jacob rose up from the Well of the Oath. And his sons took him, with their little ones and wives, in the wagons that Pharaoh had sent to carry the old man,
6 Suka kuma ɗauki dabbobinsu da mallakarsu, da suka samu a Kan’ana, Yaƙub kuwa da dukan zuriyarsa suka tafi Masar.
along with all that he possessed in the land of Canaan. And he arrived in Egypt with all his offspring:
7 Ya ɗauki’ya’yansa maza da jikokinsa da’ya’yansa mata da jikokinsa mata, dukan zuriyarsa zuwa Masar.
his sons and his grandsons, his daughters and all his progeny together.
8 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza (Yaƙub da zuriyarsa) waɗanda suka tafi Masar, Ruben ɗan farin Yaƙub.
Now these are the names of the sons of Israel, who entered into Egypt, he with his children. The firstborn is Reuben.
9 ’Ya’yan Ruben maza su ne, Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.
The sons of Reuben: Hanoch and Pallu, and Hezron and Carmi.
10 ’Ya’yan Simeyon maza su ne, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar da Sha’ul ɗan mutuniyar Kan’ana.
The sons of Simeon: Jemuel and Jamin and Ohad, and Jachin and Zohar, and Shaul, the son of a Canaanite woman.
11 ’Ya’yan Lawi maza su ne, Gershon, Kohat da Merari.
The sons of Levi: Gershon and Kohath, and Merari.
12 ’Ya’yan Yahuda maza su ne, Er, Onan, Shela, Ferez da Zera (amma Er da Onan sun mutu a ƙasar Kan’ana).’Ya’yan Ferez maza su ne, Hezron da Hamul.
The sons of Judah: Er and Onan, and Shelah, and Perez and Zerah. Now Er and Onan died in the land of Canaan. And sons were born to Perez: Hezron and Hamul.
13 ’Ya’yan Issakar maza su ne, Tola, Fuwa, Yoshub da Shimron.
The sons of Issachar: Tola and Puvah, and Job and Shimron.
14 ’Ya’yan Zebulun maza su ne, Sered, Elon da Yaleyel.
The sons of Zebulun: Sered and Elon and Jahleel.
15 Waɗannan su ne’ya’yan Liyatu maza da ta haifa wa Yaƙub a Faddan Aram, ban da’yarsa Dina.’Ya’yansa maza da mata duka, mutum talatin da uku ne.
These are the sons of Leah, whom she bore, along with his daughter Dinah, in Mesopotamia of Syria. All the souls of her sons and daughters are thirty-three.
16 ’Ya’yan Gad maza su ne, Zafon, Haggi, Shuni, Ezbon, Eri, Arodi da Areli.
The sons of Gad: Ziphion and Haggi, and Shuni and Ezbon, and Eri and Arodi, and Areli.
17 ’Ya’yan Asher maza su ne, Imna, Ishba, Ishbi da Beriya.’Yar’uwarsu ita ce Sera.’Ya’yan Beriya maza su ne, Heber da Malkiyel.
The sons of Asher: Imnah and Jesua, and Jessui and Beriah, and also their sister Sarah. The sons of Beria: Heber and Malchiel.
18 Waɗannan su ne’ya’yan da Zilfa ta haifa wa Yaƙub, ita ce Laban ya ba wa’yarsa Liyatu.’Ya’yan duka, su sha shida ne.
These are the sons of Zilpah, whom Laban gave to his daughter Leah. And these she bore to Jacob: sixteen souls.
19 ’Ya’yan Yaƙub maza waɗanda Rahila ta haifa su ne, Yusuf da Benyamin.
The sons of Rachel, the wife of Jacob: Joseph and Benjamin.
20 A Masar, Asenat’yar Fotifera, firist na On ta haifi Manasse da Efraim wa Yusuf.
And sons were born to Joseph in the land of Egypt, whom Asenath, the daughter of Potiphera, priest of Heliopolis, bore for him: Manasseh and Ephraim.
21 ’Ya’yan Benyamin maza su ne, Bela, Beker, Ashbel, Gera, Na’aman, Ehi, Rosh, Muffim, Huffim da Ard.
The sons of Benjamin: Bela and Becher, and Ashbel and Gera, and Naaman and Ehi, and Rosh and Moppim, and Huppim and Ard.
22 Waɗannan su ne’ya’yan Rahila maza waɗanda ta haifa wa Yaƙub, dukansu mutum goma sha huɗu ne.
These are the sons of Rachel, whom she bore to Jacob: all these souls are fourteen.
23 Yaron Dan shi ne, Hushim.
The sons of Dan: Hushim.
24 ’Ya’yan Naftali maza su ne, Yazeyel, Guni, Yezer da Shillem.
The sons of Naphtali: Jahzeel and Guni, and Jezer and Shillem.
25 Waɗannan su ne’ya’ya mazan da Bilha ta haifa wa Yaƙub, ita ce Laban ya ba wa’yarsa Rahila.’Ya’yan suka su bakwai ne.
These are the sons of Bilhah, whom Laban gave to his daughter Rachel, and these she bore to Jacob: all these souls are seven.
26 Dukan waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub, waɗanda suke zuriyarsa kai tsaye ban da matan’ya’yansa maza, su mutum sittin da shida ne.
All the souls who went into Egypt with Jacob and who went out from his thigh, besides the wives of his sons, were sixty-six.
27 In aka haɗa da’ya’yan nan maza guda biyu waɗanda aka haifa wa Yusuf a Masar, membobin iyalin Yaƙub, waɗanda suka tafi Masar, duka su saba’in ne.
Now the sons of Joseph, who were born to him in the land of Egypt, were two souls. All the souls of the house of Jacob, who went into Egypt, were seventy.
28 To, Yaƙub ya aiki Yahuda yă yi gaba yă sadu da Yusuf, don yă nuna musu hanyar da za su bi zuwa yankin Goshen. Da suka isa yankin Goshen,
Then he sent Judah ahead of himself, to Joseph, in order to report to him, and so that he would meet him in Goshen.
29 sai Yusuf ya kintsa keken yaƙinsa ya haura zuwa Goshen don yă taryi mahaifinsa, Isra’ila. Nan da nan da isowar Yusuf a wurin mahaifinsa, sai ya rungumi mahaifinsa, ya yi kuka na dogon lokaci.
And when he had arrived there, Joseph harnessed his chariot, and he went up to meet his father at the same place. And seeing him, he fell upon his neck, and, amid embraces, he wept.
30 Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Yanzu ina a shirye in mutu, da yake na gani da kaina cewa har yanzu kana da rai.”
And the father said to Joseph, “Now I will die happy, because I have seen your face, and I am leaving you behind alive.”
31 Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa da gidan mahaifinsa, “Zan haura in yi magana da Fir’auna, zan kuwa ce masa, ‘’Yan’uwana da gidan mahaifina, waɗanda suke zaune a ƙasar Kan’ana, sun zo wurina.
And he said to his brothers and to all his father’s house: “I will go up and report to Pharaoh, and I will say to him: ‘My brothers, and my father’s house, who were in the land of Canaan, have come to me.
32 Mutanen fa, makiyaya ne; suna kiwon dabbobi, sun kuma zo tare da garkunansu da shanunsa da kuma kome da suka mallaka.’
And these honorable men are pastors of sheep, and they have the task of feeding the flock. Their cattle, and herds, and all that they were able to hold, they have brought with them.’
33 Sa’ad da Fir’auna ya kira ku ciki, ya yi tambaya, ‘Mece ce sana’arku?’
And when he will call you and will say, ‘What is your work?’
34 Ku amsa, ‘Bayinka suna kiwon dabbobi ne, tun muna samari har zuwa yanzu, kamar yadda kakanninmu suka yi.’ Ta haka za a bar ku ku zauna a yankin Goshen, gama Masarawa suna ƙyamar makiyaya.”
You will respond, ‘Your servants are pastors of honor, from our infancy even to the present time, both we and our fathers.’ Now you will say this so that you may be able to live in the land of Goshen, because the Egyptians detest all pastors of sheep.”

< Farawa 46 >