< Farawa 46 >
1 Saboda haka Isra’ila ya kama hanya da dukan abin da yake nasa, sa’ad da ya kai Beyersheba, sai ya miƙa hadayu ga Allah na Ishaku, mahaifinsa.
And Israel went on his journey with all he had, and came to Beer-sheba, where he made offerings to the God of his father Isaac.
2 Allah kuwa ya yi magana ga Isra’ila a wahayi da dare ya ce, “Yaƙub! Yaƙub!” Yaƙub kuwa ya amsa ya ce, “Ga ni.”
And God said to Israel in a night-vision, Jacob, Jacob. And he said, Here am I.
3 Sai Allah ya ce, “Ni ne Allah, Allah na mahaifinka. Kada ka ji tsoron zuwa Masar, gama zan mai da kai al’umma mai girma a can.
And he said, I am God, the God of your father: go down to Egypt without fear, for I will make a great nation of you there:
4 Zan gangara zuwa Masar tare da kai, tabbatacce zan sāke dawo da kai. Kuma hannun Yusuf zai rufe idanunka.”
I will go down with you to Egypt, and I will see that you come back again, and at your death Joseph will put his hands on your eyes.
5 Sa’an nan Yaƙub ya bar Beyersheba,’ya’yan Isra’ila maza, suka ɗauki mahaifinsu Yaƙub da’ya’yansu da matansu a cikin wagonun da Fir’auna ya aika don a kawo shi.
Then Jacob went on from Beer-sheba; and the sons of Jacob took their father and their little ones and their wives in the carts which Pharaoh had sent for them.
6 Suka kuma ɗauki dabbobinsu da mallakarsu, da suka samu a Kan’ana, Yaƙub kuwa da dukan zuriyarsa suka tafi Masar.
And they took their cattle and all the goods which they had got in the land of Canaan, and came to Egypt, even Jacob and all his seed:
7 Ya ɗauki’ya’yansa maza da jikokinsa da’ya’yansa mata da jikokinsa mata, dukan zuriyarsa zuwa Masar.
His sons and his sons' sons, his daughters and his daughters' sons and all his family he took with him into Egypt.
8 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza (Yaƙub da zuriyarsa) waɗanda suka tafi Masar, Ruben ɗan farin Yaƙub.
And these are the names of the children of Israel who came into Egypt, even Jacob and all his sons: Reuben, Jacob's oldest son;
9 ’Ya’yan Ruben maza su ne, Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.
And the sons of Reuben: Hanoch and Pallu and Hezron and Carmi;
10 ’Ya’yan Simeyon maza su ne, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar da Sha’ul ɗan mutuniyar Kan’ana.
And the sons of Simeon: Jemuel and Jamin and Ohad and Jachin and Zohar and Shaul, the son of a woman of Canaan;
11 ’Ya’yan Lawi maza su ne, Gershon, Kohat da Merari.
And the sons of Levi: Gershon, Kohath, and Merari;
12 ’Ya’yan Yahuda maza su ne, Er, Onan, Shela, Ferez da Zera (amma Er da Onan sun mutu a ƙasar Kan’ana).’Ya’yan Ferez maza su ne, Hezron da Hamul.
And the sons of Judah: Er and Onan and Shelah and Perez and Zerah: but Er and Onan had come to their death in the land of Canaan; and the sons of Perez were Hezron and Hamul.
13 ’Ya’yan Issakar maza su ne, Tola, Fuwa, Yoshub da Shimron.
And the sons of Issachar: Tola and Puah and Job and Shimron;
14 ’Ya’yan Zebulun maza su ne, Sered, Elon da Yaleyel.
And the sons of Zebulun: Sered and Elon and Jahleel;
15 Waɗannan su ne’ya’yan Liyatu maza da ta haifa wa Yaƙub a Faddan Aram, ban da’yarsa Dina.’Ya’yansa maza da mata duka, mutum talatin da uku ne.
All these, together with his daughter Dinah, were the children of Leah, whom Jacob had by her in Paddan-aram; they were thirty-three in number.
16 ’Ya’yan Gad maza su ne, Zafon, Haggi, Shuni, Ezbon, Eri, Arodi da Areli.
And the sons of Gad: Ziphion and Haggi, Shuni and Ezbon, Eri and Arodi and Areli;
17 ’Ya’yan Asher maza su ne, Imna, Ishba, Ishbi da Beriya.’Yar’uwarsu ita ce Sera.’Ya’yan Beriya maza su ne, Heber da Malkiyel.
And the sons of Asher: Jimnah and Ishvah and Ishvi and Beriah, and Sarah, their sister; and the sons of Beriah: Heber and Malchiel.
18 Waɗannan su ne’ya’yan da Zilfa ta haifa wa Yaƙub, ita ce Laban ya ba wa’yarsa Liyatu.’Ya’yan duka, su sha shida ne.
These are the children of Zilpah, whom Laban gave to his daughter Leah, and Jacob had these sixteen children by her.
19 ’Ya’yan Yaƙub maza waɗanda Rahila ta haifa su ne, Yusuf da Benyamin.
The sons of Jacob's wife Rachel: Joseph and Benjamin.
20 A Masar, Asenat’yar Fotifera, firist na On ta haifi Manasse da Efraim wa Yusuf.
And Joseph had Manasseh and Ephraim in the land of Egypt, by Asenath, the daughter of Poti-phera, priest of On.
21 ’Ya’yan Benyamin maza su ne, Bela, Beker, Ashbel, Gera, Na’aman, Ehi, Rosh, Muffim, Huffim da Ard.
And the sons of Benjamin were Belah and Becher and Ashbel, Gera and Naaman, Ehi and Rosh, Muppim and Huppim and Ard.
22 Waɗannan su ne’ya’yan Rahila maza waɗanda ta haifa wa Yaƙub, dukansu mutum goma sha huɗu ne.
All these were the children of Rachel whom Jacob had by her, fourteen persons.
23 Yaron Dan shi ne, Hushim.
And the son of Dan was Hushim.
24 ’Ya’yan Naftali maza su ne, Yazeyel, Guni, Yezer da Shillem.
And the sons of Naphtali: Jahzeel and Guni and Jezer and Shillem.
25 Waɗannan su ne’ya’ya mazan da Bilha ta haifa wa Yaƙub, ita ce Laban ya ba wa’yarsa Rahila.’Ya’yan suka su bakwai ne.
These were the children of Bilhah, whom Laban gave to his daughter Rachel, seven persons.
26 Dukan waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub, waɗanda suke zuriyarsa kai tsaye ban da matan’ya’yansa maza, su mutum sittin da shida ne.
All the persons who came with Jacob into Egypt, the offspring of his body, were sixty-six, without taking into account the wives of Jacob's sons.
27 In aka haɗa da’ya’yan nan maza guda biyu waɗanda aka haifa wa Yusuf a Masar, membobin iyalin Yaƙub, waɗanda suka tafi Masar, duka su saba’in ne.
And the sons of Joseph whom he had in Egypt were two. Seventy persons of the family of Jacob came into Egypt.
28 To, Yaƙub ya aiki Yahuda yă yi gaba yă sadu da Yusuf, don yă nuna musu hanyar da za su bi zuwa yankin Goshen. Da suka isa yankin Goshen,
Now he had sent Judah before him to Goshen, to get word from Joseph; and so they came to the land of Goshen.
29 sai Yusuf ya kintsa keken yaƙinsa ya haura zuwa Goshen don yă taryi mahaifinsa, Isra’ila. Nan da nan da isowar Yusuf a wurin mahaifinsa, sai ya rungumi mahaifinsa, ya yi kuka na dogon lokaci.
And Joseph got his carriage ready and went to Goshen for the meeting with his father; and when he came before him, he put his arms round his neck, weeping.
30 Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Yanzu ina a shirye in mutu, da yake na gani da kaina cewa har yanzu kana da rai.”
And Israel said to Joseph, Now that I have seen you living again, I am ready for death.
31 Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa da gidan mahaifinsa, “Zan haura in yi magana da Fir’auna, zan kuwa ce masa, ‘’Yan’uwana da gidan mahaifina, waɗanda suke zaune a ƙasar Kan’ana, sun zo wurina.
And Joseph said to his brothers and to his father's people, I will go and give the news to Pharaoh, and say to him, My brothers and my father's people, from the land of Canaan, have come to me;
32 Mutanen fa, makiyaya ne; suna kiwon dabbobi, sun kuma zo tare da garkunansu da shanunsa da kuma kome da suka mallaka.’
And these men are keepers of sheep and owners of cattle, and have with them their flocks and their herds and all they have.
33 Sa’ad da Fir’auna ya kira ku ciki, ya yi tambaya, ‘Mece ce sana’arku?’
Now when Pharaoh sends for you and says, What is your business?
34 Ku amsa, ‘Bayinka suna kiwon dabbobi ne, tun muna samari har zuwa yanzu, kamar yadda kakanninmu suka yi.’ Ta haka za a bar ku ku zauna a yankin Goshen, gama Masarawa suna ƙyamar makiyaya.”
You are to say, Your servants have been keepers of cattle from our early days up to now, like our fathers; in this way you will be able to have the land of Goshen for yourselves; because keepers of sheep are unclean in the eyes of the Egyptians.