< Farawa 45 >

1 Yusuf bai ƙara iya daurewa a gaban dukan masu yi masa hidima ba, sai ya yi kuka da ƙarfi ya ce, “Kowa yă tashi daga gabana!” Saboda haka ba kowa a wurin sa’ad da Yusuf ya sanar da kansa ga’yan’uwansa.
Da kunde ikke Josef lenger legge bånd på sig for alle dem som stod hos ham; han ropte: La hver mann gå ut fra mig! Og det var ingen tilstede da Josef gav sig til kjenne for sine brødre.
2 Sai ya yi kuka da ƙarfi har Masarawa suka ji, har labarin ya kai gidan Fir’auna.
Og han brast i gråt og gråt så høit at egypterne hørte det, og de hørte det i Faraos hus.
3 Yusuf kuwa ya ce wa’yan’uwansa, “Ni ne Yusuf! Mahaifina yana nan da rai har yanzu?” Amma’yan’uwansa ba su iya amsa masa ba, gama sun firgita ƙwarai a gabansa.
Og Josef sa til sine brødre: Jeg er Josef, lever min far ennu? Men hans brødre kunde ikke svare ham, så forferdet stod de der foran ham.
4 Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ku zo kusa da ni.” Da suka yi haka, sai ya ce, “Ni ne ɗan’uwanku Yusuf, wannan da kuka sayar zuwa Masar!
Da sa Josef til sine brødre: Kjære, kom hit til mig! Så gikk de bort til ham; og han sa: Jeg er Josef, eders bror, som I solgte til Egypten.
5 Yanzu dai, kada ku damu, kada kuma ku yi fushi da kanku saboda kun sayar da ni a nan, gama Allah ya aiko ni gabanku ne don in ceci rayuka.
Men vær nu ikke bekymret og sørg ikke over at I solgte mig hit! For å holde eder i live har Gud sendt mig hit i forveien for eder;
6 Ga shi shekaru biyu ke nan ake yunwa a ƙasar, kuma da sauran shekara biyar masu zuwa da ba za a yi noma ko girbi ba.
for nu har det vært hungersnød i landet i to år, og ennu kommer det fem år da der hverken skal pløies eller høstes.
7 Amma Allah ya aiko ni gabanku ne don in adana muku raguwa a duniya, in kuma ceci rayukanku ta wurin ceto mai girma.
Men Gud har sendt mig i forveien for eder fordi han vilde levne eder en rest på jorden, og fordi han vilde holde eder i live, så det blev en stor frelse.
8 “Saboda haka fa, ba ku ba ne kuka aiko ni nan, Allah ne. Ya mai da ni mahaifi ga Fir’auna, shugaban dukan gidansa da kuma mai mulkin dukan Masar.
Så er det da ikke I som har sendt mig hit, men Gud; og han har satt mig til far for Farao og til herre over hele hans hus og til hersker i hele Egyptens land.
9 Yanzu sai ku gaggauta zuwa wurin mahaifina ku faɗa masa, ‘Abin da ɗanka Yusuf ya ce; Allah ya mai da ni shugaban dukan Masar. Gangaro wurina; kada ka jinkirta.
Skynd eder og dra op til min far og si til ham: Så sier din sønn Josef: Gud har satt mig til herre over hele Egypten; kom ned til mig, dryg ikke!
10 Za ka yi zama a yankin Goshen, ka kasance kusa da ni. Kai,’ya’yanka da kuma jikokinka, garkunanka da shanunka, da kuma dukan abin da kake da shi.
Du skal få bo i landet Gosen og være mig nær, både du og dine barn og dine barnebarn med ditt småfe og storfe og alt det du har.
11 Zan tanada maka a nan, domin akwai saura shekaru biyar na yunwa masu zuwa. In ba haka ba, kai da gidanka da dukan mallakarka za ku zama gajiyayyu.’
Og jeg vil sørge for dig der - for ennu kommer det fem hungersår - forat du ikke skal utarmes, du og ditt hus og alle de som hører dig til.
12 “Ku kanku kun gani, haka ma ɗan’uwana Benyamin, cewa tabbatacce ni ne nake magana da ku.
Og nu ser både I og min bror Benjamin med egne øine at det er jeg som taler med eder.
13 Faɗa wa mahaifina game da dukan girman da aka ba ni a Masar, da kuma game da kome da kuka gani. Ku kuma kawo mahaifina a nan da sauri.”
Fortell da min far om all min herlighet i Egypten og om alt det I har sett; og skynd eder å føre min far her ned!
14 Sa’an nan ya rungume ɗan’uwansa Benyamin ya yi kuka, sai Benyamin ya rungume shi yana kuka.
Så falt han sin bror Benjamin om halsen og gråt, og Benjamin gråt i hans armer.
15 Ya sumbaci dukan’yan’uwansa, ya kuma yi kuka a kansu. Bayan haka sai’yan’uwansa suka yi masa magana.
Og han kysset alle sine brødre og gråt ved deres bryst; og siden talte hans brødre med ham.
16 Sa’ad da labarin ya kai fadan Fir’auna cewa’yan’uwan Yusuf sun zo, sai Fir’auna da dukan hafsoshin suka ji daɗi.
Og da det spurtes i Faraos hus at Josefs brødre var kommet, blev Farao og hans tjenere glade.
17 Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Faɗa wa’yan’uwanka, ‘Yi wannan; ku jibge dabbobinku ku koma zuwa ƙasar Kan’ana,
Og Farao sa til Josef: Si til dine brødre: Så skal I gjøre: I skal lesse på eders dyr og fare hjem til Kana'ans land,
18 Ku kawo mahaifinku da iyalanku zuwa wurina. Zan ba ku mafi kyau na ƙasar Masar, za ku kuwa ci moriyar ƙasar.’
og ta så eders far og eders husfolk og kom til mig, og jeg vil gi eder det beste i Egyptens land, og I skal ete av landets fedme.
19 “An kuma umarce ka, ka faɗa musu, ‘Ku yi wannan, ku ɗauki wagonu daga Masar domin’ya’yanku da matanku, ku ɗauki mahaifinku ku zo.
Dette byder jeg dig nu å si til dem: Så skal I gjøre: I skal ta med eder vogner fra Egypten til eders barn og hustruer og hente eders far og komme hit,
20 Kada ku damu da mallakarku, gama mafi kyau na Masar za su zama naku.’”
og I skal ikke kvie eder for å reise fra eders eiendeler; for det beste i hele Egyptens land skal være eders.
21 Sai’ya’yan Isra’ila maza suka yi haka. Yusuf ya ba su wagonu kamar yadda Fir’auna ya umarta, ya kuma ba su guzuri don tafiyarsu.
Og Israels sønner gjorde så; og Josef gav dem vogner efter Faraos befaling og gav dem niste med på veien.
22 Ya ba da sababbin riguna ga kowannensu amma ga Benyamin ya ba shi shekel ɗari uku na azurfa da riguna kashi biyar.
Og han gav dem alle hver sin høitidsklædning, men Benjamin gav han tre hundre sekel sølv og fem høitidsklædninger.
23 Ga kuma abin da ya aika wa mahaifinsa, jakuna goma da aka jibge da abubuwa mafi kyau na Masar, da jakuna mata guda goma ɗauke da hatsi da burodi da waɗansu tanade-tanade don tafiyarsa.
Likeledes sendte han til sin far ti asener som bar av det beste Egypten hadde, og ti aseninner som bar korn og brød og fødevarer for hans far. på reisen.
24 Sa’an nan ya sallami’yan’uwansa, yayinda suke barin wurin ya ce musu, “Kada ku yi faɗa a hanya!”
Så lot han sine brødre fare, og de reiste; og han sa til dem: Trett ikke med hverandre på veien!
25 Saboda haka suka haura, suka fita daga Masar, suka zo wurin maihaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana.
Så drog de op fra Egypten og kom til Kana'ans land, til Jakob, sin far.
26 Suka faɗa masa, “Yusuf yana da rai! Gaskiya, shi ne mai mulkin dukan Masar.” Gaban Yaƙub ya fāɗi, domin bai gaskata su ba.
Og de fortalte ham at Josef ennu var i live, og at han var hersker over hele Egyptens land. Men hans hjerte var og blev koldt, for han trodde dem ikke.
27 Amma sa’ad da suka faɗa masa kome da Yusuf ya faɗa musu, da kuma sa’ad da ya ga wagonun da Yusuf ya aika don a ɗauke shi a kai da shi can, sai ya farfaɗo, ya dawo cikin hankalinsa.
Så fortalte de ham alt det Josef hadde sagt til dem, og han så vognene som Josef hadde sendt til å hente ham i; da oplivedes Jakobs deres fars ånd.
28 Sai Yaƙub ya ce, “Na yarda! Ɗana Yusuf yana da rai har yanzu. Zan tafi in gan shi kafin in mutu.”
Og Israel sa: Det er nok; Josef, min sønn, lever ennu; jeg vil dra avsted og se ham før jeg dør.

< Farawa 45 >