< Farawa 45 >
1 Yusuf bai ƙara iya daurewa a gaban dukan masu yi masa hidima ba, sai ya yi kuka da ƙarfi ya ce, “Kowa yă tashi daga gabana!” Saboda haka ba kowa a wurin sa’ad da Yusuf ya sanar da kansa ga’yan’uwansa.
Joseph myyte no lengere absteyne hym silf, while many men stoden bifore; wherfor he comaundide that alle men schulden go out, and that noon alien were present in the knowyng of Joseph and hise britheren.
2 Sai ya yi kuka da ƙarfi har Masarawa suka ji, har labarin ya kai gidan Fir’auna.
And Joseph reiside the vois with wepyng, which Egipcians herden, and al the hows of Farao.
3 Yusuf kuwa ya ce wa’yan’uwansa, “Ni ne Yusuf! Mahaifina yana nan da rai har yanzu?” Amma’yan’uwansa ba su iya amsa masa ba, gama sun firgita ƙwarai a gabansa.
And he seide to hise britheren, Y am Joseph; lyueth my fadir yit? The brithren myyten not answere, and weren agast bi ful myche drede.
4 Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ku zo kusa da ni.” Da suka yi haka, sai ya ce, “Ni ne ɗan’uwanku Yusuf, wannan da kuka sayar zuwa Masar!
To whiche he seide mekeli, Neiye ye to me. And whanne thei hadden neiyed nyy, he seide, Y am Joseph youre brother, whom ye selden in to Egipt;
5 Yanzu dai, kada ku damu, kada kuma ku yi fushi da kanku saboda kun sayar da ni a nan, gama Allah ya aiko ni gabanku ne don in ceci rayuka.
nyle ye drede, nether seme it to be hard to you, that ye seelden me in to these cuntreis; for God hath sent me bifore you in to Egipt for youre helthe.
6 Ga shi shekaru biyu ke nan ake yunwa a ƙasar, kuma da sauran shekara biyar masu zuwa da ba za a yi noma ko girbi ba.
For it is twei yeer that hungur bigan `to be in the lond, yit fyue yeer suen, in whiche me schal not mow ere, nether repe;
7 Amma Allah ya aiko ni gabanku ne don in adana muku raguwa a duniya, in kuma ceci rayukanku ta wurin ceto mai girma.
and God bifor sente me, that ye be reserued on erthe, and moun haue metis to lyue.
8 “Saboda haka fa, ba ku ba ne kuka aiko ni nan, Allah ne. Ya mai da ni mahaifi ga Fir’auna, shugaban dukan gidansa da kuma mai mulkin dukan Masar.
Y was sent hidur not bi youre counsel, but bi Goddis wille, which made me as the fadir of Farao, and the lord of al his hows, and prince in al the lond of Egipt.
9 Yanzu sai ku gaggauta zuwa wurin mahaifina ku faɗa masa, ‘Abin da ɗanka Yusuf ya ce; Allah ya mai da ni shugaban dukan Masar. Gangaro wurina; kada ka jinkirta.
Haste ye, and `stie ye to my fadir, and ye schulen seie to hym, Thi sone Joseph sendith these thingis; God hath maad me lord of al the lond of Egipt; come doun to me, and tarie not, and dwelle in the lond of Gessen;
10 Za ka yi zama a yankin Goshen, ka kasance kusa da ni. Kai,’ya’yanka da kuma jikokinka, garkunanka da shanunka, da kuma dukan abin da kake da shi.
and thou schalt be bisidis me, thou, and thi sones, and the sones of thi sones, thi scheep, and thi grete beestis, and alle thingis whiche thou weldist,
11 Zan tanada maka a nan, domin akwai saura shekaru biyar na yunwa masu zuwa. In ba haka ba, kai da gidanka da dukan mallakarka za ku zama gajiyayyu.’
and there Y schal fede thee; for yit fyue yeer of hungur ben residue, lest bothe thou perische, and thin hows, and alle thingis whiche thou weldist.
12 “Ku kanku kun gani, haka ma ɗan’uwana Benyamin, cewa tabbatacce ni ne nake magana da ku.
Lo! youre iyen, and the iyen of my brother Beniamyn seen, that my mouth spekith to you;
13 Faɗa wa mahaifina game da dukan girman da aka ba ni a Masar, da kuma game da kome da kuka gani. Ku kuma kawo mahaifina a nan da sauri.”
telle ye to my fadir al my glorie, and alle thingis whiche ye sien in Egipt; haste ye, and brynge ye hym to me.
14 Sa’an nan ya rungume ɗan’uwansa Benyamin ya yi kuka, sai Benyamin ya rungume shi yana kuka.
And whanne he hadde biclippid, and hadde feld in to the necke of Beniamyn, his brother, he wepte, the while also Benjamin wepte in lijk maner on the necke of Joseph.
15 Ya sumbaci dukan’yan’uwansa, ya kuma yi kuka a kansu. Bayan haka sai’yan’uwansa suka yi masa magana.
And Joseph kisside alle hise britheren, and wepte on alle; aftir whiche thingis thei weren hardi to speke to hym.
16 Sa’ad da labarin ya kai fadan Fir’auna cewa’yan’uwan Yusuf sun zo, sai Fir’auna da dukan hafsoshin suka ji daɗi.
And it was herd, and pupplischid bi famouse word in the halle of the kyng, The britheren of Joseph ben comun. And Farao ioiede, and al his meynee;
17 Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Faɗa wa’yan’uwanka, ‘Yi wannan; ku jibge dabbobinku ku koma zuwa ƙasar Kan’ana,
and Farao seide to Joseph, that he schulde comaunde hise britheren, and `seie, Charge youre beestis, and go ye in to the lond of Canaan,
18 Ku kawo mahaifinku da iyalanku zuwa wurina. Zan ba ku mafi kyau na ƙasar Masar, za ku kuwa ci moriyar ƙasar.’
and take ye fro thennus youre fadir, and kynrede, and come ye to me; and Y schal yyue to you alle the goodis of Egipt, that ye ete the merow of the lond.
19 “An kuma umarce ka, ka faɗa musu, ‘Ku yi wannan, ku ɗauki wagonu daga Masar domin’ya’yanku da matanku, ku ɗauki mahaifinku ku zo.
Comaunde thou also, that thei take waynes of the lond of Egipt to the cariage of her litle children, and wyues, and seie thou, `Take ye youre fadir, and haste ye comynge soone,
20 Kada ku damu da mallakarku, gama mafi kyau na Masar za su zama naku.’”
nether leeue ye ony thing of the purtenaunce of youre hows, for alle the richessis of Egipt schulen be youre.
21 Sai’ya’yan Isra’ila maza suka yi haka. Yusuf ya ba su wagonu kamar yadda Fir’auna ya umarta, ya kuma ba su guzuri don tafiyarsu.
The sones of Israel diden, as it was comaundid to hem; to whiche Joseph yaf waynes, bi the comaundement of Farao, and metis in the weie;
22 Ya ba da sababbin riguna ga kowannensu amma ga Benyamin ya ba shi shekel ɗari uku na azurfa da riguna kashi biyar.
and he comaundide twei stoolis to be brouyt forth to ech; forsothe he yaf to Beniamyn thre hundrid platis of siluer, with fyue the beste stoolis;
23 Ga kuma abin da ya aika wa mahaifinsa, jakuna goma da aka jibge da abubuwa mafi kyau na Masar, da jakuna mata guda goma ɗauke da hatsi da burodi da waɗansu tanade-tanade don tafiyarsa.
and sente to his fadir so myche of siluer, and of cloothis, and he addide to hem ten male assis, that schulden bere of alle richessis of Egipt, and so many femal assis, berynge wheete and looues in the weie.
24 Sa’an nan ya sallami’yan’uwansa, yayinda suke barin wurin ya ce musu, “Kada ku yi faɗa a hanya!”
Therfor he lefte hise britheren, and seide to hem goynge forth, Be ye not wrooth in the weie.
25 Saboda haka suka haura, suka fita daga Masar, suka zo wurin maihaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana.
Whiche stieden fro Egipt, and camen in to the lond of Canaan, to her fadir Jacob;
26 Suka faɗa masa, “Yusuf yana da rai! Gaskiya, shi ne mai mulkin dukan Masar.” Gaban Yaƙub ya fāɗi, domin bai gaskata su ba.
and telden to hym, and seiden, Joseph, thi sone, lyueth, and he is lord in al the lond of Egipt. And whanne this was herd, Jacob wakide as of a greuouse sleep; netheles he bileuyde not to hem.
27 Amma sa’ad da suka faɗa masa kome da Yusuf ya faɗa musu, da kuma sa’ad da ya ga wagonun da Yusuf ya aika don a ɗauke shi a kai da shi can, sai ya farfaɗo, ya dawo cikin hankalinsa.
Thei telden ayenward al the ordre of the thing; and whanne Jacob hadde seyn the waynes, and alle thingis whiche Joseph hadde sent, his spirit lyuede ayen,
28 Sai Yaƙub ya ce, “Na yarda! Ɗana Yusuf yana da rai har yanzu. Zan tafi in gan shi kafin in mutu.”
and he seide, It suffisith to me, if Joseph my sone lyueth yit, Y schal go and `Y schal se hym bifore that Y die.