< Farawa 45 >

1 Yusuf bai ƙara iya daurewa a gaban dukan masu yi masa hidima ba, sai ya yi kuka da ƙarfi ya ce, “Kowa yă tashi daga gabana!” Saboda haka ba kowa a wurin sa’ad da Yusuf ya sanar da kansa ga’yan’uwansa.
And Ioseph coude no longer refrayne before all them that stode aboute him but commaunded that they shuld goo all out from him and that there shuld be no man with him whyle he vttred him selfe vnto his brethern.
2 Sai ya yi kuka da ƙarfi har Masarawa suka ji, har labarin ya kai gidan Fir’auna.
And he wepte alowde so that the Egiptians and the house of Pharao herde it.
3 Yusuf kuwa ya ce wa’yan’uwansa, “Ni ne Yusuf! Mahaifina yana nan da rai har yanzu?” Amma’yan’uwansa ba su iya amsa masa ba, gama sun firgita ƙwarai a gabansa.
And he sayde vnto his brethern: I am Ioseph: doth my father yet lyue? But his brethern coude not answere him for they were abasshed at his presence.
4 Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ku zo kusa da ni.” Da suka yi haka, sai ya ce, “Ni ne ɗan’uwanku Yusuf, wannan da kuka sayar zuwa Masar!
And Ioseph sayde vnto his brethern: come nere to me and they came nere. And he sayde: I am Ioseph youre brother whom ye sold in to Egipte.
5 Yanzu dai, kada ku damu, kada kuma ku yi fushi da kanku saboda kun sayar da ni a nan, gama Allah ya aiko ni gabanku ne don in ceci rayuka.
And now be not greued therwith nether let it seme a cruel thinge in youre eyes that ye solde me hither. For God dyd send me before you to saue lyfe.
6 Ga shi shekaru biyu ke nan ake yunwa a ƙasar, kuma da sauran shekara biyar masu zuwa da ba za a yi noma ko girbi ba.
For this is the seconde yere of derth in the lande and fyue moo are behynde in which there shall nether be earynge nor hervest.
7 Amma Allah ya aiko ni gabanku ne don in adana muku raguwa a duniya, in kuma ceci rayukanku ta wurin ceto mai girma.
Wherfore God sent me before you to make prouision that ye myghte continue in the erth and to save youre lyues by a greate delyuerance.
8 “Saboda haka fa, ba ku ba ne kuka aiko ni nan, Allah ne. Ya mai da ni mahaifi ga Fir’auna, shugaban dukan gidansa da kuma mai mulkin dukan Masar.
So now it was not ye that sent me hither but God: and he hath made me father vnto Pharao and lorde ouer all his house and rueler in all the land of Egipte.
9 Yanzu sai ku gaggauta zuwa wurin mahaifina ku faɗa masa, ‘Abin da ɗanka Yusuf ya ce; Allah ya mai da ni shugaban dukan Masar. Gangaro wurina; kada ka jinkirta.
Hast you ad goo to my father and tell him this sayeth thy sonne Ioseph: God hath made me lorde ouer all Egipte. Come downe vnto me and tarye not
10 Za ka yi zama a yankin Goshen, ka kasance kusa da ni. Kai,’ya’yanka da kuma jikokinka, garkunanka da shanunka, da kuma dukan abin da kake da shi.
And thou shalt dwell in the londe of Gosan and be by me: both thou and thi childern and thi childerns childern: and thy shepe and beestes and all that thou hast.
11 Zan tanada maka a nan, domin akwai saura shekaru biyar na yunwa masu zuwa. In ba haka ba, kai da gidanka da dukan mallakarka za ku zama gajiyayyu.’
There will I make provision for the: for there remayne yet v yeres of derth lest thou and thi houshold and all that thou hast perish.
12 “Ku kanku kun gani, haka ma ɗan’uwana Benyamin, cewa tabbatacce ni ne nake magana da ku.
Beholde youre eyes do se and the eyes also of my brother Ben Iamin that I speake to you by mouth.
13 Faɗa wa mahaifina game da dukan girman da aka ba ni a Masar, da kuma game da kome da kuka gani. Ku kuma kawo mahaifina a nan da sauri.”
Therfore tell my father of all my honoure which I haue in Egipte and of all that ye haue sene ad make hast and brynge in father hither.
14 Sa’an nan ya rungume ɗan’uwansa Benyamin ya yi kuka, sai Benyamin ya rungume shi yana kuka.
And he fell on his brother Ben Iamis necke and wepte and Ben Iamin wepte on his necke.
15 Ya sumbaci dukan’yan’uwansa, ya kuma yi kuka a kansu. Bayan haka sai’yan’uwansa suka yi masa magana.
Moreouer he fylled all his brethern and wepte apon them. And after that his brethern talked with him.
16 Sa’ad da labarin ya kai fadan Fir’auna cewa’yan’uwan Yusuf sun zo, sai Fir’auna da dukan hafsoshin suka ji daɗi.
And when the tidynges was come vnto Pharaos housse that Iosephes brethern were come it pleased Pharao well and all his seruauntes.
17 Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Faɗa wa’yan’uwanka, ‘Yi wannan; ku jibge dabbobinku ku koma zuwa ƙasar Kan’ana,
And Pharao spake vnto Ioseph: saye vnto thy brethern this do ye: lade youre beestes ad get you hence And when ye be come vnto the londe of Canaan
18 Ku kawo mahaifinku da iyalanku zuwa wurina. Zan ba ku mafi kyau na ƙasar Masar, za ku kuwa ci moriyar ƙasar.’
take youre father and youre housholdes and come vnto me and I will geue you the beste of the lande of Egipte and ye shall eate the fatt of the londe.
19 “An kuma umarce ka, ka faɗa musu, ‘Ku yi wannan, ku ɗauki wagonu daga Masar domin’ya’yanku da matanku, ku ɗauki mahaifinku ku zo.
And commaunded also. This do ye: take charettes with you out of the lande of Egipte for youre childern and for youre wyues: and brynge youre father and come.
20 Kada ku damu da mallakarku, gama mafi kyau na Masar za su zama naku.’”
Also regarde not youre stuff for the goodes of all the londe of Egipte shalbe youres.
21 Sai’ya’yan Isra’ila maza suka yi haka. Yusuf ya ba su wagonu kamar yadda Fir’auna ya umarta, ya kuma ba su guzuri don tafiyarsu.
And the childern of Israell dyd euen so And Ioseph gaue them charettes at the commaundment of Pharao and gaue them vitayle also to spende by the waye.
22 Ya ba da sababbin riguna ga kowannensu amma ga Benyamin ya ba shi shekel ɗari uku na azurfa da riguna kashi biyar.
And he gaue vnto eche of them chaunge of rayment: but vnto Ben Iamin he gaue. iij. hundred peces of syluer and. v. chaunge of rayment.
23 Ga kuma abin da ya aika wa mahaifinsa, jakuna goma da aka jibge da abubuwa mafi kyau na Masar, da jakuna mata guda goma ɗauke da hatsi da burodi da waɗansu tanade-tanade don tafiyarsa.
And vnto his father he sent after the same maner: x. he asses laden with good out of Egipte and. x. she asses laden with corne bred and meate: to serue his father by the waye.
24 Sa’an nan ya sallami’yan’uwansa, yayinda suke barin wurin ya ce musu, “Kada ku yi faɗa a hanya!”
So sent he his brethern awaye and they departed. And he sayde vnto them: se that ye fall nor out by the waye.
25 Saboda haka suka haura, suka fita daga Masar, suka zo wurin maihaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana.
And they departed from Egipte and came in to the land of Canaan vnto Iacob their father and told him saynge.
26 Suka faɗa masa, “Yusuf yana da rai! Gaskiya, shi ne mai mulkin dukan Masar.” Gaban Yaƙub ya fāɗi, domin bai gaskata su ba.
Ioseph is yet a lyue and is gouerner ouer all the land of Egipte. And Iacobs hert wauered for he beleued tho not.
27 Amma sa’ad da suka faɗa masa kome da Yusuf ya faɗa musu, da kuma sa’ad da ya ga wagonun da Yusuf ya aika don a ɗauke shi a kai da shi can, sai ya farfaɗo, ya dawo cikin hankalinsa.
And they tolde him all the wordes of Ioseph which he had sayde vnto them. But when he sawe the charettes which Ioseph had sent to carie him then his sprites reviued.
28 Sai Yaƙub ya ce, “Na yarda! Ɗana Yusuf yana da rai har yanzu. Zan tafi in gan shi kafin in mutu.”
And Israel sayde. I haue ynough yf Ioseph my sonne be yet alyue: I will goo and se him yer that I dye.

< Farawa 45 >