< Farawa 45 >

1 Yusuf bai ƙara iya daurewa a gaban dukan masu yi masa hidima ba, sai ya yi kuka da ƙarfi ya ce, “Kowa yă tashi daga gabana!” Saboda haka ba kowa a wurin sa’ad da Yusuf ya sanar da kansa ga’yan’uwansa.
Then could Joseph not refrain himself before all those that stood by him; and he cried, Cause every man to go out from me. And there remained no man with him, while Joseph made himself known unto his brothers.
2 Sai ya yi kuka da ƙarfi har Masarawa suka ji, har labarin ya kai gidan Fir’auna.
And he raised his voice in weeping; and the Egyptians heard it, and the house of Pharaoh heard it.
3 Yusuf kuwa ya ce wa’yan’uwansa, “Ni ne Yusuf! Mahaifina yana nan da rai har yanzu?” Amma’yan’uwansa ba su iya amsa masa ba, gama sun firgita ƙwarai a gabansa.
And Joseph said unto his brothers, I am Joseph; doth my father yet live? And his brothers could not answer him; for they were terrified at his presence.
4 Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ku zo kusa da ni.” Da suka yi haka, sai ya ce, “Ni ne ɗan’uwanku Yusuf, wannan da kuka sayar zuwa Masar!
And Joseph said unto his brothers, Come near to me, I pray you; and they came near; and he said, I am Joseph your brother, whom ye sold into Egypt.
5 Yanzu dai, kada ku damu, kada kuma ku yi fushi da kanku saboda kun sayar da ni a nan, gama Allah ya aiko ni gabanku ne don in ceci rayuka.
But now be not grieved, nor be angry with yourselves, that ye sold me hither; for in order to preserve life did God send me before you.
6 Ga shi shekaru biyu ke nan ake yunwa a ƙasar, kuma da sauran shekara biyar masu zuwa da ba za a yi noma ko girbi ba.
For these two years hath the famine been already in the land; and there are yet five years, in which there will be neither ploughing nor harvesting.
7 Amma Allah ya aiko ni gabanku ne don in adana muku raguwa a duniya, in kuma ceci rayukanku ta wurin ceto mai girma.
And God hath thus sent me before you to prepare for you a permanence on the earth, and to save your lives by a great deliverance.
8 “Saboda haka fa, ba ku ba ne kuka aiko ni nan, Allah ne. Ya mai da ni mahaifi ga Fir’auna, shugaban dukan gidansa da kuma mai mulkin dukan Masar.
So now it was not you that sent me hither, but God; and he hath made me a father to Pharaoh, and a lord for all his house, and a ruler throughout all the land of Egypt.
9 Yanzu sai ku gaggauta zuwa wurin mahaifina ku faɗa masa, ‘Abin da ɗanka Yusuf ya ce; Allah ya mai da ni shugaban dukan Masar. Gangaro wurina; kada ka jinkirta.
Haste ye, and go up to my father, and say unto him, Thus hath said thy son Joseph, God hath made me lord of all Egypt; come down unto me, tarry not.
10 Za ka yi zama a yankin Goshen, ka kasance kusa da ni. Kai,’ya’yanka da kuma jikokinka, garkunanka da shanunka, da kuma dukan abin da kake da shi.
And thou shalt dwell in the land of Goshen, and thou shalt be near unto me, thou, and thy children, and thy children's children, and thy flocks, and thy herds, and all that is thine.
11 Zan tanada maka a nan, domin akwai saura shekaru biyar na yunwa masu zuwa. In ba haka ba, kai da gidanka da dukan mallakarka za ku zama gajiyayyu.’
And I will maintain thee there; for there are yet five years of famine; lest thou, and thy household, and all that thou hast, come to poverty.
12 “Ku kanku kun gani, haka ma ɗan’uwana Benyamin, cewa tabbatacce ni ne nake magana da ku.
And, behold, your own eyes see, and the eyes of my brother Benjamin, that it is my mouth that speaketh unto you.
13 Faɗa wa mahaifina game da dukan girman da aka ba ni a Masar, da kuma game da kome da kuka gani. Ku kuma kawo mahaifina a nan da sauri.”
And ye shall tell my father of all my honor in Egypt, and of all that ye have seen; and ye shall hasten and bring down my father hither.
14 Sa’an nan ya rungume ɗan’uwansa Benyamin ya yi kuka, sai Benyamin ya rungume shi yana kuka.
And he fell upon his brother Benjamin's neck, and wept; and Benjamin wept upon his neck.
15 Ya sumbaci dukan’yan’uwansa, ya kuma yi kuka a kansu. Bayan haka sai’yan’uwansa suka yi masa magana.
And he kissed all his brothers, and wept upon them; and after that his brothers spoke with him.
16 Sa’ad da labarin ya kai fadan Fir’auna cewa’yan’uwan Yusuf sun zo, sai Fir’auna da dukan hafsoshin suka ji daɗi.
And the report thereof was heard in Pharaoh's house, saying, Joseph's brothers are come; and it was pleasing in the eyes of Pharaoh, and in the eyes of his servants.
17 Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Faɗa wa’yan’uwanka, ‘Yi wannan; ku jibge dabbobinku ku koma zuwa ƙasar Kan’ana,
And Pharaoh said unto Joseph, Say unto thy brothers, This do ye; load your beasts, and go, get you unto the land of Canaan;
18 Ku kawo mahaifinku da iyalanku zuwa wurina. Zan ba ku mafi kyau na ƙasar Masar, za ku kuwa ci moriyar ƙasar.’
And take your father and your households, and come unto me; and I will give you the best of the land of Egypt, and ye shall eat the fat of the land.
19 “An kuma umarce ka, ka faɗa musu, ‘Ku yi wannan, ku ɗauki wagonu daga Masar domin’ya’yanku da matanku, ku ɗauki mahaifinku ku zo.
And thou art commanded, This do ye, take unto yourselves out of the land of Egypt wagons for your little ones, and for your wives, and take up your father, and come.
20 Kada ku damu da mallakarku, gama mafi kyau na Masar za su zama naku.’”
And do ye feel no concern on account of your household goods; for the best of all the land of Egypt is yours.
21 Sai’ya’yan Isra’ila maza suka yi haka. Yusuf ya ba su wagonu kamar yadda Fir’auna ya umarta, ya kuma ba su guzuri don tafiyarsu.
And the children of Israel did so; and Joseph gave them wagons, according to the command of Pharaoh; and he gave them provision for the way.
22 Ya ba da sababbin riguna ga kowannensu amma ga Benyamin ya ba shi shekel ɗari uku na azurfa da riguna kashi biyar.
To all of them he gave to each changes of raiment; but to Benjamin he gave three hundred pieces of silver, and five changes of raiment.
23 Ga kuma abin da ya aika wa mahaifinsa, jakuna goma da aka jibge da abubuwa mafi kyau na Masar, da jakuna mata guda goma ɗauke da hatsi da burodi da waɗansu tanade-tanade don tafiyarsa.
And to his father he sent after this manner: ten asses laden with the best things of Egypt, and ten she-asses laden with corn and bread and other food for his father, for the journey.
24 Sa’an nan ya sallami’yan’uwansa, yayinda suke barin wurin ya ce musu, “Kada ku yi faɗa a hanya!”
And he accompanied his brothers on the way, and they departed: and he said unto them, Do not fall out by the way.
25 Saboda haka suka haura, suka fita daga Masar, suka zo wurin maihaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana.
And they went out of Egypt, and came into the land of Canaan, unto Jacob their father.
26 Suka faɗa masa, “Yusuf yana da rai! Gaskiya, shi ne mai mulkin dukan Masar.” Gaban Yaƙub ya fāɗi, domin bai gaskata su ba.
And they told him, saying, Joseph is yet alive; and that he is governor over all the land of Egypt. But his heart remained cold, for he believed them not.
27 Amma sa’ad da suka faɗa masa kome da Yusuf ya faɗa musu, da kuma sa’ad da ya ga wagonun da Yusuf ya aika don a ɗauke shi a kai da shi can, sai ya farfaɗo, ya dawo cikin hankalinsa.
But when they told him all the words of Joseph, which he had said unto them; and when he saw the wagons which Joseph had sent to carry him: the spirit of Jacob their father revived.
28 Sai Yaƙub ya ce, “Na yarda! Ɗana Yusuf yana da rai har yanzu. Zan tafi in gan shi kafin in mutu.”
And Israel said, Enough; Joseph my son is yet alive: I will go and see him before I die.

< Farawa 45 >