< Farawa 45 >

1 Yusuf bai ƙara iya daurewa a gaban dukan masu yi masa hidima ba, sai ya yi kuka da ƙarfi ya ce, “Kowa yă tashi daga gabana!” Saboda haka ba kowa a wurin sa’ad da Yusuf ya sanar da kansa ga’yan’uwansa.
Da kunde Josef ikke længer beherske sig over for alle dem der stod hos ham, og han raabte »Lad alle gaa ud!« Saaledes var der ingen til Stede, da Josef gav sig til Kende for sine Brødre.
2 Sai ya yi kuka da ƙarfi har Masarawa suka ji, har labarin ya kai gidan Fir’auna.
Saa brast han i lydelig Graad, saa Ægypterne hørte det, og det spurgtes i Faraos Hus;
3 Yusuf kuwa ya ce wa’yan’uwansa, “Ni ne Yusuf! Mahaifina yana nan da rai har yanzu?” Amma’yan’uwansa ba su iya amsa masa ba, gama sun firgita ƙwarai a gabansa.
og Josef sagde til sine Brødre: »Jeg er Josef! Lever min Fader endnu?« Men hans Brødre kunde ikke svare ham, saa forfærdede var de for ham.
4 Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ku zo kusa da ni.” Da suka yi haka, sai ya ce, “Ni ne ɗan’uwanku Yusuf, wannan da kuka sayar zuwa Masar!
Saa sagde Josef til sine Brødre: »Kom hen til mig!« Og da de kom derhen, sagde Josef: »Jeg er eders Broder Josef, som I solgte til Ægypten;
5 Yanzu dai, kada ku damu, kada kuma ku yi fushi da kanku saboda kun sayar da ni a nan, gama Allah ya aiko ni gabanku ne don in ceci rayuka.
men I skal ikke græmme eder eller være forknytte, fordi I solgte mig herhen, thi Gud har sendt mig forud for eder for at opholde Liv;
6 Ga shi shekaru biyu ke nan ake yunwa a ƙasar, kuma da sauran shekara biyar masu zuwa da ba za a yi noma ko girbi ba.
i to Aar har der nu været Hungersnød i Landet, og fem Aar endnu skal der hverken pløjes eller høstes;
7 Amma Allah ya aiko ni gabanku ne don in adana muku raguwa a duniya, in kuma ceci rayukanku ta wurin ceto mai girma.
derfor sendte Gud mig forud for eder, for at I kan faa Efterkommere paa Jorden, og for at mange hos eder kan reddes og holdes i Live.
8 “Saboda haka fa, ba ku ba ne kuka aiko ni nan, Allah ne. Ya mai da ni mahaifi ga Fir’auna, shugaban dukan gidansa da kuma mai mulkin dukan Masar.
Og nu, ikke I, men Gud har sendt mig hid, og han har gjort mig til Fader hos Farao og til Herre over hele hans Hus og til Hersker over hele Ægypten.
9 Yanzu sai ku gaggauta zuwa wurin mahaifina ku faɗa masa, ‘Abin da ɗanka Yusuf ya ce; Allah ya mai da ni shugaban dukan Masar. Gangaro wurina; kada ka jinkirta.
Skynd jer nu hjem til min Fader og sig til ham: Din Søn Josef lader sige: Gud har sat mig til Hersker over hele Ægypten; kom uden Tøven ned til mig
10 Za ka yi zama a yankin Goshen, ka kasance kusa da ni. Kai,’ya’yanka da kuma jikokinka, garkunanka da shanunka, da kuma dukan abin da kake da shi.
og tag Bolig i Gosens Land og bo i min Nærhed med dine Sønner og Sønnesønner, dit Smaakvæg og Hornkvæg og alt, hvad du ejer og har;
11 Zan tanada maka a nan, domin akwai saura shekaru biyar na yunwa masu zuwa. In ba haka ba, kai da gidanka da dukan mallakarka za ku zama gajiyayyu.’
der vil jeg sørge for dit Underhold — thi Hungersnøden vil vare fem Aar endnu — for at ikke du, dit Hus eller nogen, der hører dig til, skal gaa til Grunde!
12 “Ku kanku kun gani, haka ma ɗan’uwana Benyamin, cewa tabbatacce ni ne nake magana da ku.
Nu ser I, ogsaa min Broder Benjamin, med egne Øjne, at det er mig, der taler til eder;
13 Faɗa wa mahaifina game da dukan girman da aka ba ni a Masar, da kuma game da kome da kuka gani. Ku kuma kawo mahaifina a nan da sauri.”
og I skal fortælle min Fader om al min Herlighed i Ægypten og om alt, hvad I har set, og saa skal I skynde eder at bringe min Fader herned.«
14 Sa’an nan ya rungume ɗan’uwansa Benyamin ya yi kuka, sai Benyamin ya rungume shi yana kuka.
Saa faldt han grædende sin Broder Benjamin om Halsen, og Benjamin græd i hans Arme.
15 Ya sumbaci dukan’yan’uwansa, ya kuma yi kuka a kansu. Bayan haka sai’yan’uwansa suka yi masa magana.
Og han kyssede alle sine Brødre og græd ved deres Bryst; og nu kunde hans Brødre tale med ham.
16 Sa’ad da labarin ya kai fadan Fir’auna cewa’yan’uwan Yusuf sun zo, sai Fir’auna da dukan hafsoshin suka ji daɗi.
Men det spurgtes i Faraos Hus, at Josefs Brødre var kommet, og Farao og hans Tjenere glædede sig derover:
17 Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Faɗa wa’yan’uwanka, ‘Yi wannan; ku jibge dabbobinku ku koma zuwa ƙasar Kan’ana,
og Farao sagde til Josef: »Sig til dine Brødre: Saaledes skal I gøre: Læs eders Dyr og drag til Kana'ans Land,
18 Ku kawo mahaifinku da iyalanku zuwa wurina. Zan ba ku mafi kyau na ƙasar Masar, za ku kuwa ci moriyar ƙasar.’
hent eders Fader og eders Familier og kom hid til mig, saa vil jeg give eder det bedste, der er i Ægypten, og I skal nyde Landets Fedme.
19 “An kuma umarce ka, ka faɗa musu, ‘Ku yi wannan, ku ɗauki wagonu daga Masar domin’ya’yanku da matanku, ku ɗauki mahaifinku ku zo.
Byd dem at gøre saaledes: Tag eder Vogne i Ægypten til eders Børn og Kvinder, sæt eders Fader op og kom hid;
20 Kada ku damu da mallakarku, gama mafi kyau na Masar za su zama naku.’”
bryd eder ikke om eders Ejendele, thi det bedste, der er i hele Ægypten, skal være eders!«
21 Sai’ya’yan Isra’ila maza suka yi haka. Yusuf ya ba su wagonu kamar yadda Fir’auna ya umarta, ya kuma ba su guzuri don tafiyarsu.
Det gjorde Israels Sønner saa. Og efter Faraos Bud gav Josef dem Vogne og Rejsekost med;
22 Ya ba da sababbin riguna ga kowannensu amma ga Benyamin ya ba shi shekel ɗari uku na azurfa da riguna kashi biyar.
hver især gav han dem et Sæt Festklæder, men Benjamin gav han 300 Sekel Sølv og fem Sæt Festklæder;
23 Ga kuma abin da ya aika wa mahaifinsa, jakuna goma da aka jibge da abubuwa mafi kyau na Masar, da jakuna mata guda goma ɗauke da hatsi da burodi da waɗansu tanade-tanade don tafiyarsa.
og sin Fader sendte han ti Æsler med det bedste, der var i Ægypten og ti Aseninder med Korn, Brød og Rejsetæring til Faderen.
24 Sa’an nan ya sallami’yan’uwansa, yayinda suke barin wurin ya ce musu, “Kada ku yi faɗa a hanya!”
Saa tog han Afsked med sine Brødre, og da de drog bort, sagde han til dem: »Kives ikke paa Vejen!«
25 Saboda haka suka haura, suka fita daga Masar, suka zo wurin maihaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana.
Saaledes drog de hjem fra Ægypten og kom til deres Fader Jakob i Kana'ans Land;
26 Suka faɗa masa, “Yusuf yana da rai! Gaskiya, shi ne mai mulkin dukan Masar.” Gaban Yaƙub ya fāɗi, domin bai gaskata su ba.
og de fortalte ham det og sagde: »Josef lever endnu, og han er Hersker over hele Ægypten.« Men hans Hjerte blev koldt, thi han troede dem ikke.
27 Amma sa’ad da suka faɗa masa kome da Yusuf ya faɗa musu, da kuma sa’ad da ya ga wagonun da Yusuf ya aika don a ɗauke shi a kai da shi can, sai ya farfaɗo, ya dawo cikin hankalinsa.
Saa fortalte de ham alt, hvad Josef havde sagt til dem; og da han saa Vognene, som Josef havde sendt for at hente ham, oplivedes deres Fader Jakobs Aand atter;
28 Sai Yaƙub ya ce, “Na yarda! Ɗana Yusuf yana da rai har yanzu. Zan tafi in gan shi kafin in mutu.”
og Israel sagde: »Det er stort, min Søn Josef lever endnu; jeg vil drage hen og se ham, inden jeg dør!«

< Farawa 45 >