< Farawa 45 >
1 Yusuf bai ƙara iya daurewa a gaban dukan masu yi masa hidima ba, sai ya yi kuka da ƙarfi ya ce, “Kowa yă tashi daga gabana!” Saboda haka ba kowa a wurin sa’ad da Yusuf ya sanar da kansa ga’yan’uwansa.
Yousefe da dimusa: dawa: beba: le, bu ea hawa: hamosu da amo hou ba: sa: besa: le, e da ili huluane amo sesei fisima: ne sia: i. E da ea yolalali ilima e da Yousefe adoloba, dunu eno da hame ba: i.
2 Sai ya yi kuka da ƙarfi har Masarawa suka ji, har labarin ya kai gidan Fir’auna.
E bagadewane dibiba: le, Idibidi dunu ilia da nabi. Amalalu, ilia da amo sia: ne iasu Felou ea diasuga adola asi.
3 Yusuf kuwa ya ce wa’yan’uwansa, “Ni ne Yusuf! Mahaifina yana nan da rai har yanzu?” Amma’yan’uwansa ba su iya amsa masa ba, gama sun firgita ƙwarai a gabansa.
Yousefe da ea yolalali ilima amane sia: i, “Na da Yousefe. Na ada da wali hahawane esalabala?” Be ea yolalali da amo sia: nababeba: le, ilia da bagadewane beda: iba: le, bu adole imunu da ilima hamedei.
4 Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ku zo kusa da ni.” Da suka yi haka, sai ya ce, “Ni ne ɗan’uwanku Yusuf, wannan da kuka sayar zuwa Masar!
Be Yousefe da ilima amane sia: i, “Nolalali! Dilia nama gadenena misa!” Ilia da misini, e eno adole i, “Na da dilia eya Yousefe amo dilia Idibidi sogega bidi lai.
5 Yanzu dai, kada ku damu, kada kuma ku yi fushi da kanku saboda kun sayar da ni a nan, gama Allah ya aiko ni gabanku ne don in ceci rayuka.
Dilia mae fofogadigima, amola mae da: i dioma! Amola dilia wadela: i houba: le, wadela: i fawane ninima doaga: i, mae dawa: ma! Gode Hi da dilia loboga, na guiguda: eno dunu ilia esalusu gaga: ma: ne, asunasi dagoi.
6 Ga shi shekaru biyu ke nan ake yunwa a ƙasar, kuma da sauran shekara biyar masu zuwa da ba za a yi noma ko girbi ba.
Wali da ha: i bagade ode ageyadu fawane. Ode biyale gala eno amoga osobo da hame gidinamu amo ha: i manu hame faimu, amo hou ba: mu.
7 Amma Allah ya aiko ni gabanku ne don in adana muku raguwa a duniya, in kuma ceci rayukanku ta wurin ceto mai girma.
Gode da na amo dili bisili masunusa: , asunasi dagoi. Bai E da dili amola diligaga fa: no lalelegemu mano, amo bogomu higa: i hodosa.
8 “Saboda haka fa, ba ku ba ne kuka aiko ni nan, Allah ne. Ya mai da ni mahaifi ga Fir’auna, shugaban dukan gidansa da kuma mai mulkin dukan Masar.
Amaiba: le houdafa da dilia na guiguda: hame asunasi. Gode Hifawane da na asunasi. Gode hamobeba: le, na da wali Felou ea bisili ouligisu hina dunu hamoi dagoi. Na da ea soge huluane ouligisa. Na da Idibidi fi huluane ilima hina esala.
9 Yanzu sai ku gaggauta zuwa wurin mahaifina ku faɗa masa, ‘Abin da ɗanka Yusuf ya ce; Allah ya mai da ni shugaban dukan Masar. Gangaro wurina; kada ka jinkirta.
Amaiba: le, hedolo na adama buhagili, ema ea mano Yousefe amane sia: sa amo adoma, ‘Gode da na Idibidi dunu huluanema hina bagade hamoi dagoi. Wahadafa nama misa.
10 Za ka yi zama a yankin Goshen, ka kasance kusa da ni. Kai,’ya’yanka da kuma jikokinka, garkunanka da shanunka, da kuma dukan abin da kake da shi.
Di da Gousiene sogega na gadenene fimu da defea. Di, dia mano, dia aowa, dia sibi, dia goudi, dia bulamagau amola dia liligi gagui huluane.
11 Zan tanada maka a nan, domin akwai saura shekaru biyar na yunwa masu zuwa. In ba haka ba, kai da gidanka da dukan mallakarka za ku zama gajiyayyu.’
Di da Gousiene sogega esalea, na da di ouligisa esalumu, amo dawa: ma. Wali ha: i bagade ode biyale gala eno ba: mu. Di, dia sosogo fi, amola dia lai gebo, amo huluane ha: ga bogomu na bagadewane higa: i hodosa.”
12 “Ku kanku kun gani, haka ma ɗan’uwana Benyamin, cewa tabbatacce ni ne nake magana da ku.
Yousefe da eno amane sia: i, “Defea! Wali dilia huluane amola di Bediamini, da noga: le dawa: Na da dafawane Yousefe e.
13 Faɗa wa mahaifina game da dukan girman da aka ba ni a Masar, da kuma game da kome da kuka gani. Ku kuma kawo mahaifina a nan da sauri.”
Na ada noga: le adoma amane, ‘Na da guiguda: Idibidi soge ganodini gasa bagade gala. Dilia ba: i liligi huluane ema adoma. Amasea, hedolowane e nama oule misa.’”
14 Sa’an nan ya rungume ɗan’uwansa Benyamin ya yi kuka, sai Benyamin ya rungume shi yana kuka.
E da Bediamini ha: giwane nonogone dinanu. Bediamini amola Yousefe nonogone dinanu.
15 Ya sumbaci dukan’yan’uwansa, ya kuma yi kuka a kansu. Bayan haka sai’yan’uwansa suka yi masa magana.
Amanoba, dinanuwane, e da yolalali huluane ouga: ne, nonogoi. Amalalu, yolalali da ema sia: dasu.
16 Sa’ad da labarin ya kai fadan Fir’auna cewa’yan’uwan Yusuf sun zo, sai Fir’auna da dukan hafsoshin suka ji daɗi.
Felou ea diasu fi da Yousefe yolalali da ema doaga: i, amo nababeba: le, hahawane ba: i.
17 Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Faɗa wa’yan’uwanka, ‘Yi wannan; ku jibge dabbobinku ku koma zuwa ƙasar Kan’ana,
Felou da Yousefema amane sia: i, “Diolalali ilima amane sia: ma, ilia da ilia ohe baligiga ha: i manu legele, hedolowane Ga: ina: ne sogega buhagima.
18 Ku kawo mahaifinku da iyalanku zuwa wurina. Zan ba ku mafi kyau na ƙasar Masar, za ku kuwa ci moriyar ƙasar.’
Amalalu, ilia ada amola fi huluane, guiguda: bu oule misa. Na da soge baligili ida: iwane Idibidi soge ganodini, amo ilima imunu. Ilia baligiliwane hahawane esalusu ba: mu.
19 “An kuma umarce ka, ka faɗa musu, ‘Ku yi wannan, ku ɗauki wagonu daga Masar domin’ya’yanku da matanku, ku ɗauki mahaifinku ku zo.
Ilia Idibidi gaguli fula ahoasu (bulamagau amoga hiougi) amoga ilia uda amola mano fonobahadi, amoga fila heda: ma: ne, amo oule masunu da defea. Ilia eda amola, bu oule misa: ne sia: ma.
20 Kada ku damu da mallakarku, gama mafi kyau na Masar za su zama naku.’”
Ilia liligi eno ilia sogega fisibiba: le, ilima mae da: i dioma: ne sia: ma. Liligi baligili ida: iwane Idibidi soge ganodini amo ninia da ilima imunu.”
21 Sai’ya’yan Isra’ila maza suka yi haka. Yusuf ya ba su wagonu kamar yadda Fir’auna ya umarta, ya kuma ba su guzuri don tafiyarsu.
Ya: igobe ea mano da amo sia: defele hamosu. Yousefe da ilima gaguli fula ahoasu i, amola ilia logoga moma: ne ha: i manu i.
22 Ya ba da sababbin riguna ga kowannensu amma ga Benyamin ya ba shi shekel ɗari uku na azurfa da riguna kashi biyar.
E da abula afadafa salima: ne, ilima afae afae i. Be Bediaminima e da abula biyale salima: ne i, amola silifa muni fage 300 agoane i.
23 Ga kuma abin da ya aika wa mahaifinsa, jakuna goma da aka jibge da abubuwa mafi kyau na Masar, da jakuna mata guda goma ɗauke da hatsi da burodi da waɗansu tanade-tanade don tafiyarsa.
E da ea adama dougi nabuane gala amo da: iya, Idibidi liligi ida: iwane gala ligisi, amo asunasi. Amola e da dougi nabuane eno amo da: iya gagoma, bali, agi amola logoga moma: ne ha: i manu eno i.
24 Sa’an nan ya sallami’yan’uwansa, yayinda suke barin wurin ya ce musu, “Kada ku yi faɗa a hanya!”
E da yolalali asunasi. E da ilima amane sia: i, “Dilia logoga ahoasea, mae sia: ga gegema!”
25 Saboda haka suka haura, suka fita daga Masar, suka zo wurin maihaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana.
Ilia Idibidi yolesili, ilia eda Ya: igobe amo Ga: ina: ne sogega esalu, ema buhagi.
26 Suka faɗa masa, “Yusuf yana da rai! Gaskiya, shi ne mai mulkin dukan Masar.” Gaban Yaƙub ya fāɗi, domin bai gaskata su ba.
Ilia ema amane sia: i, “Yousefe da esala. E da Idibidi fi huluane ilima hina esala.” Ya: igobe da bogomuwane fofogadigili, ilia sia: dafawaneyale dawa: mu hamedei ba: i.
27 Amma sa’ad da suka faɗa masa kome da Yusuf ya faɗa musu, da kuma sa’ad da ya ga wagonun da Yusuf ya aika don a ɗauke shi a kai da shi can, sai ya farfaɗo, ya dawo cikin hankalinsa.
Be ilia Yousefe ea sia: huluane ema olelebeba: le, amola gaguli fula ahoasu Yousefe da e Idibidi sogega oule masa: ne iasi amo ba: beba: le, e da uhi.
28 Sai Yaƙub ya ce, “Na yarda! Ɗana Yusuf yana da rai har yanzu. Zan tafi in gan shi kafin in mutu.”
E amane sia: i, “Na gofe Yousefe da esala! Na da Godema eno hame adole ba: mu! Na da mae bogole e ba: la masunu!”