< Farawa 44 >

1 Yusuf kuwa ya ba wa mai yin masa hidima a gida, waɗannan umarnai cewa, “Cika buhunan mutanen nan da abinci iyakar yadda za su iya ɗauka, ka kuma sa kuɗin kowanne a bakin buhunsa.
UJosefa waselaya inceku yendlu yakhe wathi: “Gcwalisa silikici amasaka amadoda la ngokudla konke abangakuthwala, ubusubuyisela isiliva salowo lalowo emlonyeni wesaka lakhe.
2 Sa’an nan ka sa kwaf nawa, wannan na azurfa a bakin buhun autan, tare da kuɗinsa na hatsi.” Sai mai hidimar ya yi kamar yadda Yusuf ya umarta.
Ubusufaka inkomitsho yami, leyana eyesiliva, emlonyeni wesaka lalowo omncinyane wabo ndawonye lesiliva sakhe samabele.” Yenza njengalokho uJosefa ayekutshilo.
3 Da gari ya waye, sai aka sallami mutanen tare da jakunansu.
Kwathi emadabukakusa bawavalelisa amadoda asuka kanye labobabhemi bawo.
4 Ba su yi nisa da birnin ba sa’ad da Yusuf ya ce wa mai yin masa hidima, “Tashi, ka bi waɗannan mutane nan da nan, in ka same su, ka ce musu, ‘Me ya sa kuka sāka alheri da mugunta?
Ayengakahambi okuya ngaphi ukusuka edolobheni lapho uJosefa athi encekwini yakhe, “Axhume ngokuphangisa amadoda lawana, ungawafica uthi kuwo, ‘Lenzeleni ukuphindisela okuhle ngokubi na?
5 Ba da wannan kwaf ne maigidana yake sha daga ciki yana kuma yin amfani da shi don duba? Wannan mugun abu ne da kuka yi.’”
Le kakusinkomitsho enatha ngenkosi yami njalo ehlahlula ngayo na? Le yinto embi kakhulu eseliyenzile!’”
6 Sa’ad da ya same su, sai ya maimaita waɗannan kalmomi gare su.
Wathi esebaficile wawatsho amazwi la kubo.
7 Amma suka ce masa, “Me ya sa ranka yă daɗe yake faɗin irin waɗannan abubuwa? Allah yă sawwaƙe bayinka su yi irin wannan abu!
Kodwa bathi kuye, “Kungani inkosi yethu isitsho izinto ezinjalo? Kakube kude lezinceku zakho ukwenza ulutho olunjalo!
8 Mun ma dawo maka da kuɗin da muka samu a cikin bakunan buhunanmu daga ƙasar Kan’ana. Saboda haka me zai sa mu saci azurfa ko zinariya daga gidan maigidanka?
Phela siyibuyisile kuwe isiliva sisuka laso elizweni laseKhenani, lesiyana esasifumana phakathi emilonyeni yamasaka ethu. Pho besingakwenza njani ukweba isiliva loba igolide endlini yenkosi yakho na?
9 In aka sami wani daga cikin bayinka da shi, zai mutu; sai sauran su zama bayin mai girma.”
Nxa omunye wezinceku zakho efunyanwa elayo, uzabulawa; kuthi thina abanye sibe yizigqili zenkosi yethu.”
10 Sai ya ce, “To, shi ke nan, bari yă zama yadda kuka faɗa. Duk wanda aka same shi da kwaf na azurfan zai zama bawana, sauran kuwa za su’yantu daga zargin.”
Wathi, “Kulungile, kakube njengokutsho kwenu. Lowo ozafunyanwa elayo uzakuba yisigqili sami, lina abanye lonke kalizukuba lecala.”
11 Da sauri kowannensu ya sauko da buhunsa ƙasa, ya buɗe.
Ngulowo lalowo wabo wethula isaka lakhe walivula.
12 Sa’an nan mai hidimar ya fara bincike, farawa daga babba, ya ƙare a ƙaramin. Aka kuwa sami kwaf ɗin a buhun Benyamin.
Inceku yasihamba ihlola, yaqala ngomdala yayacina ngomcinyane. Inkomitsho yayafunyanwa esakeni likaBhenjamini.
13 Ganin wannan sai suka kyakkece rigunansu. Sa’an nan suka jibga wa jakunansu kaya, suka koma birni.
Bekubona lokhu badabula izigqoko zabo. Emva kwalokho bonke betshatisa obabhemi babo amasaka baphindela edolobheni.
14 Yusuf yana nan har yanzu a gida sa’ad da Yahuda da’yan’uwansa suka shiga, suka fāɗi rub da ciki a ƙasa a gabansa.
UJosefa wayelokhu esendlini lapho uJuda labafowabo abafika khona bazilahla phansi phambi kwakhe.
15 Yusuf ya ce musu, “Mene ne wannan da kuka yi? Ba ku san cewa mutum kamar ni yana iya gane abubuwa ta wurin duba ba?”
UJosefa wathi kubo, “Kuyini lokhu elikwenzileyo? Kalazi na ukuthi umuntu onjengami ubona izinto ngokuhlahlula?”
16 Yahuda ya amsa ya ce, “Me za mu ce wa ranka yă daɗe? Yaya kuma za mu wanke kanmu daga wannan zargi? Allah ya tona laifin bayinka. Ga mu, za mu zama bayinka, da mu da wanda aka sami kwaf ɗin a hannunsa.”
UJuda waphendula wathi, “Kambe singabe sisathini? Singakuveza kanjani ukuba msulwa kwethu? UNkulunkulu usembule icala lezinceku zakho. Manje sesiyizichaka zenkosi yami, thina ngokwethu lalowo ofunyenwe elayo inkomitsho.”
17 Amma Yusuf ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka! Mutumin da aka sami kwaf ɗin a hannunsa ne kaɗai zai zama bawana. Sauranku, ku koma ga mahaifinku da salama.”
Kodwa uJosefa wathi. “Kakube kude lami ukwenza into enjalo! Yileyo indoda kuphela efunyanwe ilayo inkomitsho ezakuba yisichaka sami. Abanye lonke buyelani kuyihlo ngokuthula.”
18 Sai Yahuda ya haura zuwa wurinsa ya ce, “Ranka yă daɗe, roƙo nake, bari bawanka yă yi magana da ranka yă daɗe. Kada ka yi fushi da bawanka, ko da yake daidai kake da Fir’auna kansa.
UJuda wasesondela kuye wathi, “Oh, nkosi yami, akuvumele inceku yakho itsho ilizwi enkosini yami. Ungayizondeli inceku yakho, loba wena ulingana loFaro ngokwakhe.
19 Ranka yă daɗe ya tambayi bayinka ya ce, ‘Kuna da mahaifi ko ɗan’uwa?’
Inkosi yami yabuza izinceku zayo yathi, ‘Lilaye na uyihlo kumbe umfowenu?’
20 Muka kuwa amsa, ‘Muna da mahaifi tsoho, akwai kuma ɗa matashi, wanda aka haifa masa cikin tsufarsa. Ɗan’uwansa ya rasu, shi ne kuwa ɗa kaɗai na mahaifiyarsa da ya rage, mahaifinsa kuwa yana ƙaunarsa.’
Thina saphendula sathi, ‘Silaye ubaba oseluphele, njalo ikhona indodana ayizala eseluphele. Umnewabo wafa, njalo yiyo yodwa eseleyo emadodaneni kanina, ngakho uyise uyayithanda.’
21 “Sai ka ce wa bayinka, ‘Ku kawo mini shi don in gan shi da kaina.’
Wena wasusithi ezincekwini zakho, ‘Mletheni kimi ukuze ngimbone mina ngokwami.’
22 Muka kuwa ce wa ranka yă daɗe, ‘Saurayin ba zai iya barin mahaifinsa ba, gama in ya bar shi, mahaifinsa zai mutu.’
Thina sathi enkosini yami, ‘Umfana ngeke asuka kuyise; nxa esuka kuye, uyise uzakufa.’
23 Amma ka faɗa wa bayinka, ‘Sai kun kawo ƙaramin ɗan’uwanku tare da ku, in ba haka ba, ba za ku sāke ganin fuskata ba.’
Kodwa izinceku zakho wazitshela wathi, ‘Ngaphandle kokuba umnawenu omncane lize laye, ngeke liphinde libubone njalo ubuso bami.’
24 Sa’ad da muka koma wurin bawanka mahaifinmu, sai muka faɗa masa abin da ranka yă daɗe ya ce.
Sathi ukubuyela encekwini yakho ubaba, samtshela lokho okwakutshiwo yinkosi yami.
25 “Sai mahaifinmu ya ce, ‘Ku koma ku sayo ƙarin abinci.’
Ubaba wasesithi, ‘Buyelani liyethenga okunye njalo ukudla.’
26 Amma muka ce, ‘Ba za mu iya gangarawa ba, sai in ƙaramin ɗan’uwanmu yana tare da mu. Ba za mu iya ganin fuskar mutumin ba, sai ƙaramin ɗan’uwanmu yana tare mu.’
Kodwa thina sathi, ‘Ngeke siye khona. Kuphela nxa umnawethu omncane elathi, singahamba. Ngeke sibubone ubuso bendoda leyo ngaphandle kokuba umnawethu omncane silaye.’
27 “Bawanka mahaifinmu ya ce mana, ‘Kun san cewa matata ta haifa mini’ya’ya biyu maza.
Inceku yakho ubaba yathi kithi, ‘Liyakwazi ukuthi umkami wangizalela amadodana amabili.
28 Ɗayansu ya tafi daga gare ni, na kuwa ce, “Tabbatacce an yayyage shi kaca-kaca.” Ban kuwa gan shi ba tuntuni.
Omunye wabo wasuka kimi, ngathi, “Ngempela udlithiziwe waba yizicucu.” Ngakho kangisaphindanga ngambona kusukela khonapho.
29 In kun ɗauki wannan daga wurina shi ma wani abu ya same shi, za ku kawo furfura kaina zuwa kabari cikin baƙin ciki.’ (Sheol h7585)
Manje lingangithathela lalo futhi abesesehlelwa ngokubi, lizakwehlisela ikhanda lami eliyimpunga engcwabeni ngidabukile kakhulu.’ (Sheol h7585)
30 “Saboda haka yanzu, in saurayin ba ya nan tare da mu sa’ad da na koma ga bawanka mahaifina, in kuma mahaifina, wanda ransa yana daure kurkusa da ran saurayin,
Ngakho-ke, nxa umfana singelaye lapho sengibuyela encekwini yakho ubaba, yena ompilo yakhe isondelelene kakhulu leyomfana lo,
31 ya ga cewa saurayin ba ya nan, zai mutu. Bayinka za su sa bawanka, mahaifinmu, yă mutu cikin baƙin ciki, da tsufansa. (Sheol h7585)
uzakuthi angabona umfana engekho, ahle afe. Thina zinceku zakho sizakusa ikhanda likababa eliyimpunga engcwabeni lihlulukelwe. (Sheol h7585)
32 Gama ni baranka na ɗauki lamunin saurayin a wurin mahaifinsa da cewa, ‘In ban komo maka da shi ba, sai alhakinsa yă zauna a kaina a gaban mahaifina, dukan raina!’
Inceku yakho yanikela ukuphila kwayo ngokuphepha komfana kubaba. Ngathi, ‘Nxa ngingambuyisi kuwe, ngizawuthwala lowomlandu kuwe, baba, impilo yami yonke!’
33 “To, yanzu, ina roƙonka bari bawanka yă zauna a nan a matsayin bawanka, ranka yă daɗe a maimakon saurayin, a kuma bar saurayin yă koma da’yan’uwansa.
Ngakho-ke ngiyacela ukuthi uvumele inceku yakho isale lapha njengesichaka senkosi yami esikhundleni somfana, yena umfana akhululwe ahambe labanewabo.
34 Yaya zan koma ga mahaifina, in saurayin ba ya tare da ni? A’a! Kada ka bari in ga baƙin cikin da zai auko wa mahaifina.”
Ngingabuyela ngithini kubaba umfana ngingelaye? Hatshi! Ungangenzi ngibone usizi olungamehlela ubaba.”

< Farawa 44 >