< Farawa 44 >
1 Yusuf kuwa ya ba wa mai yin masa hidima a gida, waɗannan umarnai cewa, “Cika buhunan mutanen nan da abinci iyakar yadda za su iya ɗauka, ka kuma sa kuɗin kowanne a bakin buhunsa.
And he commaunded the rueler of his house saynge: fyll the mens sackes with food as moch as they can carie
2 Sa’an nan ka sa kwaf nawa, wannan na azurfa a bakin buhun autan, tare da kuɗinsa na hatsi.” Sai mai hidimar ya yi kamar yadda Yusuf ya umarta.
and put euery mans money in his bagge mouth and put my syluer cuppe in the sackes mouth of the yongest and his corne money also. And he dyd as Ioseph had sayde.
3 Da gari ya waye, sai aka sallami mutanen tare da jakunansu.
And in ye mornynge as soone as it was lighte the me were let goo with their asses.
4 Ba su yi nisa da birnin ba sa’ad da Yusuf ya ce wa mai yin masa hidima, “Tashi, ka bi waɗannan mutane nan da nan, in ka same su, ka ce musu, ‘Me ya sa kuka sāka alheri da mugunta?
And when they were out of the cytie and not yet ferre awaye Ioseph sayde vnto the ruelar of his house: vp and folowe after the men and ouertake them and saye vnto them: wherefore haue ye rewarded euell for good?
5 Ba da wannan kwaf ne maigidana yake sha daga ciki yana kuma yin amfani da shi don duba? Wannan mugun abu ne da kuka yi.’”
is that not the cuppe of which my lorde drynketh ad doth he not prophesie therin? ye haue euell done that ye haue done.
6 Sa’ad da ya same su, sai ya maimaita waɗannan kalmomi gare su.
And he ouertoke them and sayde the same wordes vnto them.
7 Amma suka ce masa, “Me ya sa ranka yă daɗe yake faɗin irin waɗannan abubuwa? Allah yă sawwaƙe bayinka su yi irin wannan abu!
And they answered him: wherfore sayth my lorde soch wordes? God forbydd that thy servauntes shulde doo so.
8 Mun ma dawo maka da kuɗin da muka samu a cikin bakunan buhunanmu daga ƙasar Kan’ana. Saboda haka me zai sa mu saci azurfa ko zinariya daga gidan maigidanka?
Beholde the money which we founde in oure sackes mouthes we brought agayne vnto the out of the lande of Canaa: how then shulde we steale out of my lordes house ether syluer or golde?
9 In aka sami wani daga cikin bayinka da shi, zai mutu; sai sauran su zama bayin mai girma.”
with whosoeuer of thy seruauntes it be founde let him dye and let vs also be my lordes bondmen.
10 Sai ya ce, “To, shi ke nan, bari yă zama yadda kuka faɗa. Duk wanda aka same shi da kwaf na azurfan zai zama bawana, sauran kuwa za su’yantu daga zargin.”
And he sayde: Now therfore acordynge vnto youre woordes he with whom it is found shalbe my seruaunte: but ye shalbe harmelesse.
11 Da sauri kowannensu ya sauko da buhunsa ƙasa, ya buɗe.
And attonce euery man toke downe his sacke to the grounde ad every man opened his sacke.
12 Sa’an nan mai hidimar ya fara bincike, farawa daga babba, ya ƙare a ƙaramin. Aka kuwa sami kwaf ɗin a buhun Benyamin.
And he serched and began at the eldest and left at the yongest. And the cuppe was founde in Ben Iamins sacke.
13 Ganin wannan sai suka kyakkece rigunansu. Sa’an nan suka jibga wa jakunansu kaya, suka koma birni.
Then they rent their clothes and laded euery man his asse and went agayne vnto the cytie.
14 Yusuf yana nan har yanzu a gida sa’ad da Yahuda da’yan’uwansa suka shiga, suka fāɗi rub da ciki a ƙasa a gabansa.
And Iuda and his brethre came to Iosephs house for he was yet there ad they fell before him on the grounde.
15 Yusuf ya ce musu, “Mene ne wannan da kuka yi? Ba ku san cewa mutum kamar ni yana iya gane abubuwa ta wurin duba ba?”
And Ioseph sayde vnto the: what dede is this which ye haue done? wist ye not that soch a man as I can prophesie?
16 Yahuda ya amsa ya ce, “Me za mu ce wa ranka yă daɗe? Yaya kuma za mu wanke kanmu daga wannan zargi? Allah ya tona laifin bayinka. Ga mu, za mu zama bayinka, da mu da wanda aka sami kwaf ɗin a hannunsa.”
Then sayde Iuda: what shall we saye vnto my lorde what shall we speake or what excuse can we make? God hath founde out ye wekednesse of thy seruauntes. Beholde both we and he with whom the cuppe is founde are thy seruauntes.
17 Amma Yusuf ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka! Mutumin da aka sami kwaf ɗin a hannunsa ne kaɗai zai zama bawana. Sauranku, ku koma ga mahaifinku da salama.”
And he answered: God forbyd ye I shulde do so the man with whom the cuppe is founde he shalbe my seruaunte: but goo ye in peace vn to youre father.
18 Sai Yahuda ya haura zuwa wurinsa ya ce, “Ranka yă daɗe, roƙo nake, bari bawanka yă yi magana da ranka yă daɗe. Kada ka yi fushi da bawanka, ko da yake daidai kake da Fir’auna kansa.
Then Iuda went vnto him and sayde: oh my lorde let thy servaunte speake a worde in my lordes audyence and be not wrooth with thi servaunte: for thou art euen as Pharao.
19 Ranka yă daɗe ya tambayi bayinka ya ce, ‘Kuna da mahaifi ko ɗan’uwa?’
My lorde axed his seruaunte sainge: haue ye a father or a brother?
20 Muka kuwa amsa, ‘Muna da mahaifi tsoho, akwai kuma ɗa matashi, wanda aka haifa masa cikin tsufarsa. Ɗan’uwansa ya rasu, shi ne kuwa ɗa kaɗai na mahaifiyarsa da ya rage, mahaifinsa kuwa yana ƙaunarsa.’
And we answered my lord we haue a father that is old and a yonge lad which he begat in his age: ad the brother of the sayde lad is dead and he is all that is left of that mother. And his father loueth him.
21 “Sai ka ce wa bayinka, ‘Ku kawo mini shi don in gan shi da kaina.’
Then sayde my lorde vnto his seruauntes brynge him vnto me that I maye sett myne eyes apon him.
22 Muka kuwa ce wa ranka yă daɗe, ‘Saurayin ba zai iya barin mahaifinsa ba, gama in ya bar shi, mahaifinsa zai mutu.’
And we answered my lorde that the lad coude not goo from his father for if he shulde leaue his father he were but a deed man.
23 Amma ka faɗa wa bayinka, ‘Sai kun kawo ƙaramin ɗan’uwanku tare da ku, in ba haka ba, ba za ku sāke ganin fuskata ba.’
Than saydest thou vnto thy servauntes: excepte youre yongest brother come with you loke that ye se my face no moare.
24 Sa’ad da muka koma wurin bawanka mahaifinmu, sai muka faɗa masa abin da ranka yă daɗe ya ce.
And when we came vnto thy servaunt oure father we shewed him what my lorde had sayde.
25 “Sai mahaifinmu ya ce, ‘Ku koma ku sayo ƙarin abinci.’
And when oure father sayde vnto vs goo agayne and bye vs a litle fode:
26 Amma muka ce, ‘Ba za mu iya gangarawa ba, sai in ƙaramin ɗan’uwanmu yana tare da mu. Ba za mu iya ganin fuskar mutumin ba, sai ƙaramin ɗan’uwanmu yana tare mu.’
we sayd yt we coude not goo. Neverthelesse if oure youngeste brother go with vs then will we goo for we maye not see the mannes face excepte oure yongest brother be with vs.
27 “Bawanka mahaifinmu ya ce mana, ‘Kun san cewa matata ta haifa mini’ya’ya biyu maza.
Then sayde thy servaunt oure father vnto vs. Ye knowe that my wyfe bare me. ij. sonnes.
28 Ɗayansu ya tafi daga gare ni, na kuwa ce, “Tabbatacce an yayyage shi kaca-kaca.” Ban kuwa gan shi ba tuntuni.
And the one went out from me and it is sayde of a suertie that he is torne in peaces of wyld beastes and I sawe him not sence.
29 In kun ɗauki wannan daga wurina shi ma wani abu ya same shi, za ku kawo furfura kaina zuwa kabari cikin baƙin ciki.’ (Sheol )
Yf ye shall take this also awaye fro me and some mysfortune happen apon him then shall ye brynge my gray heed with sorow vnto the grave. (Sheol )
30 “Saboda haka yanzu, in saurayin ba ya nan tare da mu sa’ad da na koma ga bawanka mahaifina, in kuma mahaifina, wanda ransa yana daure kurkusa da ran saurayin,
Now therfore whe I come to thy servaunt my father yf the lad be not with me: seinge that his lyfe hageth by the laddes lyfe
31 ya ga cewa saurayin ba ya nan, zai mutu. Bayinka za su sa bawanka, mahaifinmu, yă mutu cikin baƙin ciki, da tsufansa. (Sheol )
then as soone as he seeth that the lad is not come he will dye. So shall we thy servautes brynge the gray hedde of thy servaunt oure father with sorow vnto the grave. (Sheol )
32 Gama ni baranka na ɗauki lamunin saurayin a wurin mahaifinsa da cewa, ‘In ban komo maka da shi ba, sai alhakinsa yă zauna a kaina a gaban mahaifina, dukan raina!’
For I thy servaunt became suertie for the lad vnto my father and sayde: yf I bringe him not vnto the agayne. I will bere the blame all my life loge.
33 “To, yanzu, ina roƙonka bari bawanka yă zauna a nan a matsayin bawanka, ranka yă daɗe a maimakon saurayin, a kuma bar saurayin yă koma da’yan’uwansa.
Now therfore let me thy servaunt byde here for ye lad and be my lordes bondman: and let the lad goo home with his brethern.
34 Yaya zan koma ga mahaifina, in saurayin ba ya tare da ni? A’a! Kada ka bari in ga baƙin cikin da zai auko wa mahaifina.”
For how can I goo vnto my father and the lad not wyth me: lest I shulde see the wretchednes that shall come on my father.