< Farawa 44 >
1 Yusuf kuwa ya ba wa mai yin masa hidima a gida, waɗannan umarnai cewa, “Cika buhunan mutanen nan da abinci iyakar yadda za su iya ɗauka, ka kuma sa kuɗin kowanne a bakin buhunsa.
And he commanded [the one] who [was] over household his saying fill [the] sacks of the men food just as they are able! to carry and put [the] silver of each man in [the] mouth of sack his.
2 Sa’an nan ka sa kwaf nawa, wannan na azurfa a bakin buhun autan, tare da kuɗinsa na hatsi.” Sai mai hidimar ya yi kamar yadda Yusuf ya umarta.
And cup my [the] cup of silver you will put in [the] mouth of [the] sack of the young [brother] and [the] silver of grain his and he did according to [the] word of Joseph which he had spoken.
3 Da gari ya waye, sai aka sallami mutanen tare da jakunansu.
The morning it was light and the men they were sent off they and donkeys their.
4 Ba su yi nisa da birnin ba sa’ad da Yusuf ya ce wa mai yin masa hidima, “Tashi, ka bi waɗannan mutane nan da nan, in ka same su, ka ce musu, ‘Me ya sa kuka sāka alheri da mugunta?
They they came out the city not they had gone far and Joseph he said to [the one] who [was] over household his arise pursue after the men and you will overtake them and you will say to them why? have you repaid evil for good.
5 Ba da wannan kwaf ne maigidana yake sha daga ciki yana kuma yin amfani da shi don duba? Wannan mugun abu ne da kuka yi.’”
¿ Not [is] this [that] which he drinks master my in it and he indeed he practices divination by it you have done evil [that] which you have done.
6 Sa’ad da ya same su, sai ya maimaita waɗannan kalmomi gare su.
And he overtook them and he spoke to them the words these.
7 Amma suka ce masa, “Me ya sa ranka yă daɗe yake faɗin irin waɗannan abubuwa? Allah yă sawwaƙe bayinka su yi irin wannan abu!
And they said to him why? does he speak master my according to the words these far be it to servants your from doing according to the manner this.
8 Mun ma dawo maka da kuɗin da muka samu a cikin bakunan buhunanmu daga ƙasar Kan’ana. Saboda haka me zai sa mu saci azurfa ko zinariya daga gidan maigidanka?
Here! silver which we found in [the] mouth of sacks our we brought back to you from [the] land of Canaan and how? will we steal from [the] house of master your silver or gold.
9 In aka sami wani daga cikin bayinka da shi, zai mutu; sai sauran su zama bayin mai girma.”
[anyone] whom It is found with him of servants your and he will die and also we we will be[long] to lord my to slaves.
10 Sai ya ce, “To, shi ke nan, bari yă zama yadda kuka faɗa. Duk wanda aka same shi da kwaf na azurfan zai zama bawana, sauran kuwa za su’yantu daga zargin.”
And he said also now according to words your [will be] so it [anyone] whom it is found with him he will be of me slave and you you will be innocent.
11 Da sauri kowannensu ya sauko da buhunsa ƙasa, ya buɗe.
And they hurried and they brought down each man sack his [the] ground towards and they opened each man sack his.
12 Sa’an nan mai hidimar ya fara bincike, farawa daga babba, ya ƙare a ƙaramin. Aka kuwa sami kwaf ɗin a buhun Benyamin.
And he searched with the old [brother] he began and with the young [brother] he finished and it was found the cup in [the] sack of Benjamin.
13 Ganin wannan sai suka kyakkece rigunansu. Sa’an nan suka jibga wa jakunansu kaya, suka koma birni.
And they tore clothes their and he loaded each man on donkey his and they went back the city towards.
14 Yusuf yana nan har yanzu a gida sa’ad da Yahuda da’yan’uwansa suka shiga, suka fāɗi rub da ciki a ƙasa a gabansa.
And he came Judah and brothers his [the] house of towards Joseph and he still he [was] there and they fell before him [the] ground towards.
15 Yusuf ya ce musu, “Mene ne wannan da kuka yi? Ba ku san cewa mutum kamar ni yana iya gane abubuwa ta wurin duba ba?”
And he said to them Joseph what? [is] the deed this which you have done ¿ not do you know that indeed he practices divination a man who [is] like me.
16 Yahuda ya amsa ya ce, “Me za mu ce wa ranka yă daɗe? Yaya kuma za mu wanke kanmu daga wannan zargi? Allah ya tona laifin bayinka. Ga mu, za mu zama bayinka, da mu da wanda aka sami kwaf ɗin a hannunsa.”
And he said Judah what? will we say to lord my what? will we speak and what? will we justify ourselves God he has found [the] guilt of servants your here we [are] slaves of lord my both we as well as [the one] who it was found the cup in hand his.
17 Amma Yusuf ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka! Mutumin da aka sami kwaf ɗin a hannunsa ne kaɗai zai zama bawana. Sauranku, ku koma ga mahaifinku da salama.”
And he said far be it to me from doing this the man whom it was found the cup in hand his he he will be of me slave and you go up to peace to father your.
18 Sai Yahuda ya haura zuwa wurinsa ya ce, “Ranka yă daɗe, roƙo nake, bari bawanka yă yi magana da ranka yă daɗe. Kada ka yi fushi da bawanka, ko da yake daidai kake da Fir’auna kansa.
And he drew near to him Judah and he said pardon me O lord my may he speak please servant your a word in [the] ears of lord my and may not it burn anger your on servant your for as you as Pharaoh.
19 Ranka yă daɗe ya tambayi bayinka ya ce, ‘Kuna da mahaifi ko ɗan’uwa?’
Lord my he asked servants his saying ¿ [does] there [belong] to you a father or a brother.
20 Muka kuwa amsa, ‘Muna da mahaifi tsoho, akwai kuma ɗa matashi, wanda aka haifa masa cikin tsufarsa. Ɗan’uwansa ya rasu, shi ne kuwa ɗa kaɗai na mahaifiyarsa da ya rage, mahaifinsa kuwa yana ƙaunarsa.’
And we said to lord my there [belongs] to us a father old and a child of old age young and brother his he died and he was left he to only him to mother his and father his he loves him.
21 “Sai ka ce wa bayinka, ‘Ku kawo mini shi don in gan shi da kaina.’
And you said to servants your bring down him to me so let me set eye my on him.
22 Muka kuwa ce wa ranka yă daɗe, ‘Saurayin ba zai iya barin mahaifinsa ba, gama in ya bar shi, mahaifinsa zai mutu.’
And we said to lord my not he will be able the young man to leave father his and he will leave father his and he will die.
23 Amma ka faɗa wa bayinka, ‘Sai kun kawo ƙaramin ɗan’uwanku tare da ku, in ba haka ba, ba za ku sāke ganin fuskata ba.’
And you said to servants your if not he will come down brother your young with you not you will repeat! to see face my.
24 Sa’ad da muka koma wurin bawanka mahaifinmu, sai muka faɗa masa abin da ranka yă daɗe ya ce.
And it was that we went up to servant your father my and we told to him [the] words of lord my.
25 “Sai mahaifinmu ya ce, ‘Ku koma ku sayo ƙarin abinci.’
And he said father our go back buy for us a little of food.
26 Amma muka ce, ‘Ba za mu iya gangarawa ba, sai in ƙaramin ɗan’uwanmu yana tare da mu. Ba za mu iya ganin fuskar mutumin ba, sai ƙaramin ɗan’uwanmu yana tare mu.’
And we said not we are able to go down if there [is] brother our young with us and we will go down for not we will be able to see [the] face of the man and brother our young not he [is] with us.
27 “Bawanka mahaifinmu ya ce mana, ‘Kun san cewa matata ta haifa mini’ya’ya biyu maza.
And he said servant your father my to us you you know that two [sons] she bore to me wife my.
28 Ɗayansu ya tafi daga gare ni, na kuwa ce, “Tabbatacce an yayyage shi kaca-kaca.” Ban kuwa gan shi ba tuntuni.
And he went out the one from with me and I said surely certainly he has been torn to pieces and not I have seen him until now.
29 In kun ɗauki wannan daga wurina shi ma wani abu ya same shi, za ku kawo furfura kaina zuwa kabari cikin baƙin ciki.’ (Sheol )
And you will take also this [one] from with presence my and it will happen to him harm and you will cause to go down gray hair my in calamity Sheol towards. (Sheol )
30 “Saboda haka yanzu, in saurayin ba ya nan tare da mu sa’ad da na koma ga bawanka mahaifina, in kuma mahaifina, wanda ransa yana daure kurkusa da ran saurayin,
And therefore when come I to servant your father my and the lad not [is] he with us and life his [is] bound up with life his.
31 ya ga cewa saurayin ba ya nan, zai mutu. Bayinka za su sa bawanka, mahaifinmu, yă mutu cikin baƙin ciki, da tsufansa. (Sheol )
And it will be when sees he that there not [is] the young man and he will die and they will bring down servants your [the] gray hair of servant your father our in sorrow Sheol towards. (Sheol )
32 Gama ni baranka na ɗauki lamunin saurayin a wurin mahaifinsa da cewa, ‘In ban komo maka da shi ba, sai alhakinsa yă zauna a kaina a gaban mahaifina, dukan raina!’
For servant your he stood surety for the young man from with father my saying if not I will bring him to you and I will be culpable to father my all the days.
33 “To, yanzu, ina roƙonka bari bawanka yă zauna a nan a matsayin bawanka, ranka yă daɗe a maimakon saurayin, a kuma bar saurayin yă koma da’yan’uwansa.
And therefore let him remain please servant your in place of the young man a slave of lord my and the lad let him go up with brothers his.
34 Yaya zan koma ga mahaifina, in saurayin ba ya tare da ni? A’a! Kada ka bari in ga baƙin cikin da zai auko wa mahaifina.”
For how? will I go up to father my and the lad not [is] he with me lest I should look on the calamity which it will find father my.