< Farawa 43 >

1 A yanzu, yunwa ta yi tsanani a ƙasar.
Cependant la famine pesai! violemment sur toute la terre.
2 Saboda haka sa’ad da suka cinye dukan hatsin da suka kawo daga Masar, mahaifinsu ya ce musu, “Ku koma, ku sayo mana ƙarin abinci.”
Et les vivres qu’ils avaient apportés de l’Égypte, étant consommés, Jacob dit à ses fils: Retournez, et achetez-nous quelques provisions.
3 Amma Yahuda ya ce masa, “Mutumin ya gargaɗe mu sosai cewa, ‘Ba za ku sāke ganin fuskata ba sai in ɗan’uwanku yana tare da ku.’
Juda répondit: Cet homme nous a fait une déclaration sous le sceau du serment, disant: Vous ne verrez point ma face si vous n’amenez votre frère le plus jeune avec vous.
4 In za ka aika da ɗan’uwanmu tare da mu, za mu gangara mu sayo maka abinci.
Si donc vous voulez l’envoyer avec nous, nous irons ensemble, et nous achèterons ce qui vous est nécessaire.
5 Amma in ba za ka aika da shi ba, ba za mu gangara ba, gama mutumin ya ce mana, ‘Ba za ku sāke ganin fuskata ba sai ko in ɗan’uwanku yana tare da ku.’”
Mais si vous ne voulez pas, nous n’irons pas; car cet homme, comme souvent nous l’avons dit, nous a fait une déclaration, disant: Vous ne verrez point ma face, sans votre frère le plus jeune.
6 Isra’ila ya yi tambaya, “Me ya sa kuka kawo wannan damuwa a kaina ta wurin faɗa wa mutumin cewa kuna da wani ɗan’uwa?”
Israël leur dit: Pour mon malheur vous avez fait de manière que vous lui avez indiqué que vous aviez encore un frère.
7 Suka amsa, “Mutumin ya yi mana tambaya sosai game da kanmu da iyalinmu. Ya tambaye mu, ‘Mahaifinku yana da rai har yanzu? Kuna da wani ɗan’uwa?’ Mu dai mun amsa tambayoyinsa ne. Ta yaya za mu sani zai ce, ‘Ku kawo ɗan’uwanku a nan’?”
Mais eux répondirent: Cet homme nous a interrogés par ordre sur notre famille: si notre père vivait, si nous avions un autre frère; et nous lui avons répondu conséquemment, selon ce qu’il avait demandé; est-ce que nous pouvions savoir qu’il dirait: Amenez votre frère avec vous?
8 Sa’an nan Yahuda ya ce wa Isra’ila mahaifinsa, “Ka aika saurayin tare da ni za mu kuwa tafi nan da nan, saboda mu da’ya’yanmu mu rayu, kada mu mutu.
Juda aussi dit à son père: Envoyez l’enfant avec moi, afin que nous partions et que nous puissions vivre, et que nous ne mourions pas, nous et nos petits enfants.
9 Ni kaina zan tabbatar da lafiyarsa; na ɗauki lamuninsa, a hannuna za ka neme shi. In ban dawo da shi gare ka, in sa shi nan a gabanka ba, zan ɗauki laifin a gabanka dukan kwanakina.
C’est moi qui me charge de l’enfant; c’est à ma main que vous le redemanderez; si je ne le ramène, et si je ne vous le rends, je serai coupable envers vous à jamais.
10 Ai, da ba mun jinkirta ba, da mun komo har sau biyu.”
S’il n’était pas intervenu de délai, nous serions déjà revenus une seconde fois.
11 Sa’an nan mahaifinsu Isra’ila ya ce musu, “In dole ne a yi haka, to, sai ku yi. Ku sa waɗansu amfani mafi kyau na ƙasar a buhunanku, ku ɗauka zuwa wurin mutumin a matsayin kyauta, da ɗan man ƙanshi na shafawa, da kuma’yar zuma, da kayan yaji, da ƙaro, da tsabar citta da kuma almon.
Ainsi Israël leur père leur dit: S’il le faut ainsi, faites ce que vous voudrez; prenez des meilleurs fruits de ce pays-ci dans vos vases, et portez à cet homme en présent un peu de résine, de miel, de storax, de stacté, de térébinthe et d’amandes.
12 Ku ɗauki ninki biyu na yawan azurfa tare da ku, gama dole ku mayar da azurfan da aka sa a cikin bakunan buhunanku. Mai yiwuwa an yi haka a kuskure ne.
Portez aussi avec vous le double d’argent; et celui que vous avez trouvé dans vos sacs, reportez-le, de peur que cela n’ait été fait par méprise.
13 Ku ɗauki ɗan’uwanku kuma ku koma wurin mutumin nan da nan.
Mais prenez aussi votre frère et allez vers cet homme.
14 Bari Allah Maɗaukaki yă nuna muku alheri a gaban mutumin saboda yă bar ɗan’uwanku da Benyamin su dawo tare da ku. Ni kuwa, in na yi rashi, na yi rashi.”
Que mon Dieu tout-puissant vous le rende favorable, afin qu’il renvoie avec vous votre frère qu’il retient, et ce Benjamin; et moi, je serai comme privé d’enfants.
15 Saboda haka mutanen suka ɗauki kyautar, da kuma kuɗin da ya ninka na farko. Suka kuma ɗauki Benyamin, suka gaggauta suka gangara zuwa Masar suka kuma gabatar da kansu ga Yusuf.
Ceux-ci prirent donc avec eux les présents, le double d’argent et Benjamin, et ils descendirent en Égypte et se présentèrent devant Joseph.
16 Sa’ad da Yusuf ya ga Benyamin tare da su, sai ya ce wa mai hidimar gidansa, “Ka shigar da mutanen cikin gida, ka yanka dabba ka shirya, gama mutanen za su ci abincin rana tare da ni.”
Lorsque Joseph les vit et Benjamin avec eux, il commanda à l’intendant de sa maison, disant: Fais entrer ces hommes dans la maison; tue des victimes, et apprête un festin; parce que c’est avec moi qu’ils doivent manger à midi.
17 Mutumin ya yi kamar yadda Yusuf ya faɗa masa, ya kuwa ɗauki mutanen zuwa gidan Yusuf.
Celui-ci fit ce qui lui avait été commandé, et il introduisit ces hommes dans la maison.
18 Mutanen dai suka firgita sa’ad da aka ɗauke su zuwa gidansa. Suka yi tunani, “An kawo mu nan ne saboda azurfan da aka sa a cikin buhunanmu da farko. Yana so yă fāɗa mana, yă kuma sha ƙarfinmu, yă ƙwace mu kamar bayi, yă kuma kwashe jakunanmu.”
Et là, épouvantés, ils se dirent mutuellement: C’est à cause de l’argent que nous avons rapporté précédemment dans nos sacs qu’il nous a fait entrer ici, pour déverser sur nous une fausse accusation, et nous réduire violemment en servitude, nous et nos ânes.
19 Saboda haka suka je wurin mai yin wa Yusuf hidima, suka yi masa magana a bakin ƙofar gida.
C’est pourquoi, à la porte même, s’approchant de l’intendant de la maison,
20 Suka ce, “Ranka yă daɗe, mun zo nan ƙaro na farko don mu saya abinci,
Ils dirent: Nous vous prions, seigneur, de nous écouter. Nous sommes déjà venus ici pour acheter des vivres;
21 amma a inda muka tsaya don mu kwana, da muka buɗe buhunanmu sai kowannenmu ya sami azurfansa daidai a bakin buhunsa. Saboda haka ga kuɗin a hannunmu, mun sāke komowa da su.
Lesquels achetés, quand nous fûmes arrivés à l’hôtellerie, nous ouvrîmes nos sacs, et nous trouvâmes l’argent à l’entrée des sacs: nous l’avons rapporté maintenant dans tout son poids.
22 Mun kuma kawo ƙarin azurfa tare da mu don mu saya abinci. Ba mu san wa ya sa azurfanmu a cikin buhunanmu ba.”
Mais nous avons rapporté aussi d’autre argent pour acheter ce qui nous est nécessaire. Nous ne savons pas qui a mis cet argent dans nos bourses.
23 Sai mai hidimar ya ce, “Ba kome, kada ku ji tsoro. Allahnku, Allahn mahaifinku ne ya ba ku dukiyar a cikin buhunanku; ni dai, na karɓi azurfanku.” Sa’an nan ya fitar musu da Simeyon.
Mais lui répondit: Paix avec vous! ne craignez point: votre Dieu et le Dieu de votre père vous a mis des trésors dans vos sacs, car l’argent que vous m’avez donné, c’est moi qui l’ai en bonne monnaie. Et il leur amena Siméon.
24 Mai yin hidimar ya ɗauki mutane zuwa gidan Yusuf ya ba su ruwa su wanke ƙafafunsu, ya kuma tanada wa jakunansu abinci.
Et les ayant introduits dans la maison, il leur apporta de l’eau, et ils lavèrent leurs pieds, et il donna à manger à leurs ânes.
25 Suka shirya kyautansu domin isowar Yusuf da rana, gama sun ji cewa zai ci abinci a nan.
Or eux préparaient leurs présents, attendant que Joseph entrât sur le midi; car ils avaient appris que c’était là qu’ils devaient manger du pain.
26 Sa’ad da Yusuf ya zo gida, sai suka ba shi kyautai da suka kawo, suka rusuna a gabansa har ƙasa.
Joseph donc entra dans sa maison, et ils lui offrirent les présents qu’ils tenaient en leurs mains, et ils se prosternèrent, inclinés vers la terre.
27 Ya tambaye su, yaya suke, sa’an nan ya ce, “Yaya tsohon nan mahaifinku da kuka faɗa mini? Yana da rai har yanzu?”
Mais Joseph, leur ayant rendu leur salut avec bonté, les interrogea, disant: Se porte-t-il bien, votre vieux père dont vous m’aviez parlé? vit-il encore?
28 Suka amsa, “Bawanka mahaifinmu yana da rai har yanzu da kuma ƙoshin lafiya.” Suka kuma rusuna suka yi mubaya’a.
Ceux-ci répondirent: Il se porte bien, votre serviteur notre père, il vit encore. Et s’étant profondément inclinés, ils se prosternèrent devant lui.
29 Da ya ɗaga idanu, sai ya ga ɗan’uwansa Benyamin, ɗan mahaifiyarsa, sai ya yi tambaya, “Wannan ne ƙaramin ɗan’uwanku, wanda kuka faɗa mini a kai?” Ya kuma ce, “Allah yă yi maka albarka, ɗana.”
Or Joseph, levant les yeux, vit Benjamin son frère utérin, et dit: Celui-ci est votre jeune frère dont vous m’aviez parlé? Et de nouveau: Dieu, dit-il, te soit miséricordieux, mon fils!
30 Saboda motsi mai zurfi da zuciyarsa ta yi da ganin ɗan’uwansa, sai Yusuf ya gaggauta ya fita, ya nemi wuri yă yi kuka. Ya shiga ɗakinsa ya yi kuka a can.
Et il se retira précipitamment, car ses entrailles s’étaient émues sur son frère, et des larmes s’échappaient de ses yeux: entrant donc dans sa chambre il pleura.
31 Bayan ya wanke fuskarsa, sai ya fito ya daure, ya umarta, “A kawo abinci.”
Puis, sortant de nouveau, le visage lavé, il se contint et dit: Servez des pains.
32 Sai aka raba musu abinci, nasa shi kaɗai su kuma su kaɗai, domin Masarawa ba sa cin abinci tare da Ibraniyawa, gama wannan abin ƙyama ne ga Masarawa.
Les pains servis à part pour Joseph, à part pour ses frères, et à part pour les Égyptiens qui mangeaient ensemble (car il n’est pas permis aux Égyptiens démanger avec les Hébreux, et ils regardent comme profane un semblable repas),
33 Aka zaunar da’yan’uwan Yusuf a gabansa bisa ga shekarunsu, daga ɗan fari zuwa auta.’Yan’uwan kuwa suka duddubi juna suna mamaki.
Ils s’assirent devant lui, le premier-né, selon son droit d’aînesse, et le plus jeune, selon son âge. Or ils étaient extrêmement surpris,
34 Daga teburin da yake a gaban Yusuf aka riƙa ɗibar rabonsu ana kai musu, amma rabon Benyamin ya yi biyar ɗin na kowannensu. Suka kuwa sha, suka yi murna tare da shi.
En prenant les parts qu’ils avaient reçues de lui; car une part d’autant plus grande vint à Benjamin, qu’elle surpassait cinq autres parts. Ils burent donc et firent grande chère avec lui.

< Farawa 43 >