< Farawa 43 >

1 A yanzu, yunwa ta yi tsanani a ƙasar.
Koro kech ne pod ger ahinya e piny.
2 Saboda haka sa’ad da suka cinye dukan hatsin da suka kawo daga Masar, mahaifinsu ya ce musu, “Ku koma, ku sayo mana ƙarin abinci.”
Bangʼ kane gisechamo cham duto mane gia godo Misri, wuon-gi nowachonegi niya, “Doguru mondo udhi ungʼiewnwae chiemo moko.”
3 Amma Yahuda ya ce masa, “Mutumin ya gargaɗe mu sosai cewa, ‘Ba za ku sāke ganin fuskata ba sai in ɗan’uwanku yana tare da ku.’
To Juda nowachone niya, “Ngʼat cha nosiemowa matek ni, ‘Ok nachak awuo kodu ka ok ubiro gi owadu.’
4 In za ka aika da ɗan’uwanmu tare da mu, za mu gangara mu sayo maka abinci.
Kinyalo yie mondo Benjamin odhi kodwa, to wabiro dhi mondo wadhi warund cham.
5 Amma in ba za ka aika da shi ba, ba za mu gangara ba, gama mutumin ya ce mana, ‘Ba za ku sāke ganin fuskata ba sai ko in ɗan’uwanku yana tare da ku.’”
To ka ok iore, to ok wabi dhi, nikech ngʼatno nowachonwa ni, ‘Ok abi chak awuo kodu ka ok ubiro gi owadu.’”
6 Isra’ila ya yi tambaya, “Me ya sa kuka kawo wannan damuwa a kaina ta wurin faɗa wa mutumin cewa kuna da wani ɗan’uwa?”
Israel nopenjogi niya, “Angʼo ma omiyo ukelona chandruogni ka unyiso ngʼatno ni un kod owadu moro?”
7 Suka amsa, “Mutumin ya yi mana tambaya sosai game da kanmu da iyalinmu. Ya tambaye mu, ‘Mahaifinku yana da rai har yanzu? Kuna da wani ɗan’uwa?’ Mu dai mun amsa tambayoyinsa ne. Ta yaya za mu sani zai ce, ‘Ku kawo ɗan’uwanku a nan’?”
To negidwoke niya, “Ngʼatno nopenjowa ahinya kuomwa wawegi kendo kuom joodwa. Nopenjowa ni, ‘Bende wuonu pod ngima? Bende un gi owadu machielo?’ Ne wadwoke mana gik mane openjowa. Ere kaka dine wangʼe ni obiro wachonwa ni, ‘Dhi ukel owaduno ka’?”
8 Sa’an nan Yahuda ya ce wa Isra’ila mahaifinsa, “Ka aika saurayin tare da ni za mu kuwa tafi nan da nan, saboda mu da’ya’yanmu mu rayu, kada mu mutu.
Eka Juda nowacho ne Israel wuon mare niya, “We wawuogi kendo adhi gi wuowini, mondo omi wan kod in kod nyithindwa kik kech negwa.
9 Ni kaina zan tabbatar da lafiyarsa; na ɗauki lamuninsa, a hannuna za ka neme shi. In ban dawo da shi gare ka, in sa shi nan a gabanka ba, zan ɗauki laifin a gabanka dukan kwanakina.
An awuon asingora ni abiro rite kendo en e lweta. Ka ok aduoge iri ka, to ikwana kaka jaketho e ndalo duto mag ngimana.
10 Ai, da ba mun jinkirta ba, da mun komo har sau biyu.”
Ka debed ni ok waseketho kinde, dine wasedhi ma waduogo diriyo.”
11 Sa’an nan mahaifinsu Isra’ila ya ce musu, “In dole ne a yi haka, to, sai ku yi. Ku sa waɗansu amfani mafi kyau na ƙasar a buhunanku, ku ɗauka zuwa wurin mutumin a matsayin kyauta, da ɗan man ƙanshi na shafawa, da kuma’yar zuma, da kayan yaji, da ƙaro, da tsabar citta da kuma almon.
Eka Israel wuon-gi nowachonegi niya, “Ka en ni nyaka obed kamano, to timuru kama. Keturu gik moko mabeyo mag pinyni e ogundeu kendo utergi ne ngʼatno kaka mich; ma gin yiende moko, gi mor kich gi gik mangʼwe ngʼar gi mane-mane kod oyungu.
12 Ku ɗauki ninki biyu na yawan azurfa tare da ku, gama dole ku mayar da azurfan da aka sa a cikin bakunan buhunanku. Mai yiwuwa an yi haka a kuskure ne.
Kawuru pesa moromo rundo nyadiriyo, nikech nyaka uduoki pesa mane oket ei ogundeu. Nyalo bedo ni mano nobothnigi.
13 Ku ɗauki ɗan’uwanku kuma ku koma wurin mutumin nan da nan.
Kawuru owadu kendo udhi ir ngʼatno piyo.
14 Bari Allah Maɗaukaki yă nuna muku alheri a gaban mutumin saboda yă bar ɗan’uwanku da Benyamin su dawo tare da ku. Ni kuwa, in na yi rashi, na yi rashi.”
Kendo mad Nyasaye Maratego timnu ngʼwono e nyim ngʼatno mondo mi owe owadu kod Benjamin mondo oduog kodu. To an to kochuno ni nyaka abed mokuyo to abiro kuyo.”
15 Saboda haka mutanen suka ɗauki kyautar, da kuma kuɗin da ya ninka na farko. Suka kuma ɗauki Benyamin, suka gaggauta suka gangara zuwa Masar suka kuma gabatar da kansu ga Yusuf.
Kuom mano jogo nokawo mich kod pesa moromo rundo nyadiriyo, kod Benjamin bende. Negireto mapiyo nono ka gidhi Misri kendo negidhi ir Josef.
16 Sa’ad da Yusuf ya ga Benyamin tare da su, sai ya ce wa mai hidimar gidansa, “Ka shigar da mutanen cikin gida, ka yanka dabba ka shirya, gama mutanen za su ci abincin rana tare da ni.”
Kane Josef oneno Benjamin kani kodgi, nowacho ne jarit ode niya, “Kaw jogi iter oda, yangʼnegi chiayo kendo ilosnegi chiemo mondo gichiem koda sa auchiel.”
17 Mutumin ya yi kamar yadda Yusuf ya faɗa masa, ya kuwa ɗauki mutanen zuwa gidan Yusuf.
Jarit notimo mana kaka Josef nokone kendo notero jogo nyaka e od Josef.
18 Mutanen dai suka firgita sa’ad da aka ɗauke su zuwa gidansa. Suka yi tunani, “An kawo mu nan ne saboda azurfan da aka sa a cikin buhunanmu da farko. Yana so yă fāɗa mana, yă kuma sha ƙarfinmu, yă ƙwace mu kamar bayi, yă kuma kwashe jakunanmu.”
To jogo ne luoro omako kane otergi e od Josef. Negiparo niya, “Osekelwa ka nikech pesa ma wayudo koduok e ogundewa, chiengʼ mane wabiro kae mokwongo. Odwaro ni mondo oichwa kendo olowa mondo mi oketwa wasumbini, bangʼe okaw pundewa.”
19 Saboda haka suka je wurin mai yin wa Yusuf hidima, suka yi masa magana a bakin ƙofar gida.
Kuom mano negidhi ir jarit od Josef kendo giwuoyo kode e dhoot.
20 Suka ce, “Ranka yă daɗe, mun zo nan ƙaro na farko don mu saya abinci,
Negiwachone niya, “Jaduongʼ ne wabiro ka mokwongo ngʼiewo cham.
21 amma a inda muka tsaya don mu kwana, da muka buɗe buhunanmu sai kowannenmu ya sami azurfansa daidai a bakin buhunsa. Saboda haka ga kuɗin a hannunmu, mun sāke komowa da su.
To kamane wabuoroe gotieno ne wagonyo gundewa kendo ngʼato ka ngʼato kuomwa noyudo pesane mana kaka ne wabiro kodgi e dho ogunde. Kuom mano waseduogogi.
22 Mun kuma kawo ƙarin azurfa tare da mu don mu saya abinci. Ba mu san wa ya sa azurfanmu a cikin buhunanmu ba.”
Bende wasebiro gi pesa moko mondo wangʼiew godo chiemo. Ok wangʼeyo ngʼama noketo pesa e gundewa.”
23 Sai mai hidimar ya ce, “Ba kome, kada ku ji tsoro. Allahnku, Allahn mahaifinku ne ya ba ku dukiyar a cikin buhunanku; ni dai, na karɓi azurfanku.” Sa’an nan ya fitar musu da Simeyon.
Nowacho niya, “Mano ber. Kik uluor. Nyasaye ma Nyasach wuonu, osedwokonu pesau e gundeu; to pesa mane ungʼiewgo cham ira, an godo.” Eka ne okelonegi Simeon.
24 Mai yin hidimar ya ɗauki mutane zuwa gidan Yusuf ya ba su ruwa su wanke ƙafafunsu, ya kuma tanada wa jakunansu abinci.
Jarit notero jogo e od Josef, nomiyogi pi mondo giluokgo tiendgi kendo pundegi bende nomiyo chiemo.
25 Suka shirya kyautansu domin isowar Yusuf da rana, gama sun ji cewa zai ci abinci a nan.
Negiiko mich mane gibiro godo mondo gi dhi gimi Josef sa auchiel, nikech negisewinjo ni gidhi chiemo kode.
26 Sa’ad da Yusuf ya zo gida, sai suka ba shi kyautai da suka kawo, suka rusuna a gabansa har ƙasa.
Kane Josef odwogo dala, negimiye mich mane gikelone, kendo negikulore e nyime nyaka e lowo.
27 Ya tambaye su, yaya suke, sa’an nan ya ce, “Yaya tsohon nan mahaifinku da kuka faɗa mini? Yana da rai har yanzu?”
Josef nopenjogi kaka gidhi eka nowachonegi niya, “Jaduongʼ ma wuonu mane uwachona wach kuome ni nade? Bende pod ongima?”
28 Suka amsa, “Bawanka mahaifinmu yana da rai har yanzu da kuma ƙoshin lafiya.” Suka kuma rusuna suka yi mubaya’a.
Negidwoke niya, “Jatichni ma wuonwa pod ngima kendo odhi maber.” Kendo negikulorene ka gimiyogo duongʼ.
29 Da ya ɗaga idanu, sai ya ga ɗan’uwansa Benyamin, ɗan mahaifiyarsa, sai ya yi tambaya, “Wannan ne ƙaramin ɗan’uwanku, wanda kuka faɗa mini a kai?” Ya kuma ce, “Allah yă yi maka albarka, ɗana.”
Kane orango ma oneno owadgi Benjamin, wuod min-gi hie, nopenjogi niya, “Ma e owadu ma chogo, mane uwachona wachne?” Kendo nomedo wacho niya, “Nyasaye mad gwedhi wuoda.”
30 Saboda motsi mai zurfi da zuciyarsa ta yi da ganin ɗan’uwansa, sai Yusuf ya gaggauta ya fita, ya nemi wuri yă yi kuka. Ya shiga ɗakinsa ya yi kuka a can.
Ne mirima omake ka oneno Benjamin owadgi. Josef noreto kadhi oko kendo orango kamane onyalo pondoe ka oywak. Nodonjo e kachiende kendo ne oywak kuno.
31 Bayan ya wanke fuskarsa, sai ya fito ya daure, ya umarta, “A kawo abinci.”
Bangʼ kane oseluoko wangʼe, noduogo kendo ka otemo oore nowacho niya, “Chiemuru.”
32 Sai aka raba musu abinci, nasa shi kaɗai su kuma su kaɗai, domin Masarawa ba sa cin abinci tare da Ibraniyawa, gama wannan abin ƙyama ne ga Masarawa.
Negitokone chiembe kende, owetene kendgi, kendo jo-Misri mane chiemo kode bende nomi chiembgi kendgi, nikech jo-Misri ne ok nyal chiemo gi jo-Hibrania, nimar mano en gima kwero ne jo-Misri.
33 Aka zaunar da’yan’uwan Yusuf a gabansa bisa ga shekarunsu, daga ɗan fari zuwa auta.’Yan’uwan kuwa suka duddubi juna suna mamaki.
Owete Josef nobet e mesa e nyime kaluwore kaka nywolgi nobet, chakre wuowi maduongʼ nyaka wuowi matin kendo e kinde mane gibet kamano chunygi noparore.
34 Daga teburin da yake a gaban Yusuf aka riƙa ɗibar rabonsu ana kai musu, amma rabon Benyamin ya yi biyar ɗin na kowannensu. Suka kuwa sha, suka yi murna tare da shi.
Kane omigi chiemo koa e mesa mar Josef, chiemb Benjamin ne ngʼeny moloyo mar ngʼato angʼata nyadibich. Kuom mano negichiemo kendo gimetho ka gin thuolo kode.

< Farawa 43 >