< Farawa 43 >

1 A yanzu, yunwa ta yi tsanani a ƙasar.
Men Hungersnøden var hård i Landet;
2 Saboda haka sa’ad da suka cinye dukan hatsin da suka kawo daga Masar, mahaifinsu ya ce musu, “Ku koma, ku sayo mana ƙarin abinci.”
og da de havde fortæret det Korn, de havde hentet i Ægypten, sagde deres Fader til dem: "Køb os igen lidt Føde!"
3 Amma Yahuda ya ce masa, “Mutumin ya gargaɗe mu sosai cewa, ‘Ba za ku sāke ganin fuskata ba sai in ɗan’uwanku yana tare da ku.’
Men Juda svarede ham: "Manden sagde os ganske afgjort: I bliver ikke stedt for mit Åsyn, medmindre eders Broder er med!
4 In za ka aika da ɗan’uwanmu tare da mu, za mu gangara mu sayo maka abinci.
Hvis du derfor vil sende vor Broder med os, vil vi rejse ned og købe dig Føde;
5 Amma in ba za ka aika da shi ba, ba za mu gangara ba, gama mutumin ya ce mana, ‘Ba za ku sāke ganin fuskata ba sai ko in ɗan’uwanku yana tare da ku.’”
men sender du ham ikke med, så rejser vi ikke derned, thi Manden sagde til os: I bliver ikke stedt for mit Åsyn, medmindre eders Broder er med!"
6 Isra’ila ya yi tambaya, “Me ya sa kuka kawo wannan damuwa a kaina ta wurin faɗa wa mutumin cewa kuna da wani ɗan’uwa?”
Så sagde Israel: "Hvorfor handlede I ilde imod mig og fortalte Manden, at I havde en Broder til?"
7 Suka amsa, “Mutumin ya yi mana tambaya sosai game da kanmu da iyalinmu. Ya tambaye mu, ‘Mahaifinku yana da rai har yanzu? Kuna da wani ɗan’uwa?’ Mu dai mun amsa tambayoyinsa ne. Ta yaya za mu sani zai ce, ‘Ku kawo ɗan’uwanku a nan’?”
De svarede: "Manden spurgte os nøje ud om os og vor Slægt og sagde: Lever eders Fader endnu? Har I en Broder til? Og vi svarede ham på hans Spørgsmål; kunde vi vide, at han vilde sige: Bring eders Broder herned!"
8 Sa’an nan Yahuda ya ce wa Isra’ila mahaifinsa, “Ka aika saurayin tare da ni za mu kuwa tafi nan da nan, saboda mu da’ya’yanmu mu rayu, kada mu mutu.
Men Juda sagde til sin Fader Israel: "Send dog Drengen med mig, så vi kan komme af Sted og blive i Live og undgå Døden, både vi og du og vore Børn!
9 Ni kaina zan tabbatar da lafiyarsa; na ɗauki lamuninsa, a hannuna za ka neme shi. In ban dawo da shi gare ka, in sa shi nan a gabanka ba, zan ɗauki laifin a gabanka dukan kwanakina.
Jeg svarer for ham, af min Hånd må du kræve ham: bringer jeg ham ikke til dig og stiller ham for dit Åsyn, vil jeg være din Skyldner for bestandig;
10 Ai, da ba mun jinkirta ba, da mun komo har sau biyu.”
havde vi nu ikke spildt Tiden, kunde vi have været tilbage to Gange!"
11 Sa’an nan mahaifinsu Isra’ila ya ce musu, “In dole ne a yi haka, to, sai ku yi. Ku sa waɗansu amfani mafi kyau na ƙasar a buhunanku, ku ɗauka zuwa wurin mutumin a matsayin kyauta, da ɗan man ƙanshi na shafawa, da kuma’yar zuma, da kayan yaji, da ƙaro, da tsabar citta da kuma almon.
Så sagde deres Fader Israel til dem: "Kan det ikke være anderledes, gør da i alt Fald således: Tag noget af det bedste, Landet frembringer, med i eders Sække og bring Manden en Gave, lidt Mastiksbalsam, lidt Honning, Tragakantgummi, Cistusharpiks, Pistacienødder og Mandler;
12 Ku ɗauki ninki biyu na yawan azurfa tare da ku, gama dole ku mayar da azurfan da aka sa a cikin bakunan buhunanku. Mai yiwuwa an yi haka a kuskure ne.
og tag dobbelt så mange Penge med, så I bringer de Penge tilbage, som var lagt oven i eders Sække; måske var det en Fejltagelse;
13 Ku ɗauki ɗan’uwanku kuma ku koma wurin mutumin nan da nan.
og tag så eders Broder og drag atter til Manden!
14 Bari Allah Maɗaukaki yă nuna muku alheri a gaban mutumin saboda yă bar ɗan’uwanku da Benyamin su dawo tare da ku. Ni kuwa, in na yi rashi, na yi rashi.”
Gud den Almægtige lade eder finde Barmhjertighed hos Manden, så han lader eders anden Broder og Benjamin fare - men skal jeg være barnløs, så lad mig da blive det!"
15 Saboda haka mutanen suka ɗauki kyautar, da kuma kuɗin da ya ninka na farko. Suka kuma ɗauki Benyamin, suka gaggauta suka gangara zuwa Masar suka kuma gabatar da kansu ga Yusuf.
Så tog Mændene deres Gave og dobbelt så mange Penge med; også Benjamin tog de med, brød op og drog ned til Ægypten, hvor de fremstillede sig for Josef.
16 Sa’ad da Yusuf ya ga Benyamin tare da su, sai ya ce wa mai hidimar gidansa, “Ka shigar da mutanen cikin gida, ka yanka dabba ka shirya, gama mutanen za su ci abincin rana tare da ni.”
Da Josef så Benjamin iblandt dem, sagde han til sin Hushovmester: "Bring de Mænd ind i mit Hus, lad slagte og lave til, thi de skal spise til Middag hos mig."
17 Mutumin ya yi kamar yadda Yusuf ya faɗa masa, ya kuwa ɗauki mutanen zuwa gidan Yusuf.
Manden gjorde, som Josef bød, og førte Mændene ind i Josefs Hus.
18 Mutanen dai suka firgita sa’ad da aka ɗauke su zuwa gidansa. Suka yi tunani, “An kawo mu nan ne saboda azurfan da aka sa a cikin buhunanmu da farko. Yana so yă fāɗa mana, yă kuma sha ƙarfinmu, yă ƙwace mu kamar bayi, yă kuma kwashe jakunanmu.”
Men Mændene blev bange, da de førtes ind i Josefs Hus, og sagde: "Det er for de Penges Skyld, der forrige Gang kom tilbage i vore Sække, at vi føres herind, for at de kan vælte sig ind på os og kaste sig over os, gøre os til Trælle og tage vore Æsler."
19 Saboda haka suka je wurin mai yin wa Yusuf hidima, suka yi masa magana a bakin ƙofar gida.
Derfor trådte de hen til Josefs Hushovmester ved Døren til Huset
20 Suka ce, “Ranka yă daɗe, mun zo nan ƙaro na farko don mu saya abinci,
og sagde: "Hør os, Herre! Vi drog en Gang før herned for at købe Føde,
21 amma a inda muka tsaya don mu kwana, da muka buɗe buhunanmu sai kowannenmu ya sami azurfansa daidai a bakin buhunsa. Saboda haka ga kuɗin a hannunmu, mun sāke komowa da su.
og da vi kom til vort Natteherberge og åbnede vore Sække, se. da lå vore Penge oven i hver enkelts Sæk, vore Penge til sidste Hvid. Men nu har vi bragt dem med tilbage
22 Mun kuma kawo ƙarin azurfa tare da mu don mu saya abinci. Ba mu san wa ya sa azurfanmu a cikin buhunanmu ba.”
og desuden andre Penge for at købe Føde. Vi ved ikke, hvem der har lagt Pengene i vore Sække!"
23 Sai mai hidimar ya ce, “Ba kome, kada ku ji tsoro. Allahnku, Allahn mahaifinku ne ya ba ku dukiyar a cikin buhunanku; ni dai, na karɓi azurfanku.” Sa’an nan ya fitar musu da Simeyon.
Men han svarede: "Vær ved godt Mod, frygt ikke! Eders Gud og eders Faders Gud har lagt en Skat i eders Sække - eders Penge har jeg modtaget!" Og han førte Simeon ud til dem.
24 Mai yin hidimar ya ɗauki mutane zuwa gidan Yusuf ya ba su ruwa su wanke ƙafafunsu, ya kuma tanada wa jakunansu abinci.
Så førte Manden dem ind i Josefs Hus og gav dem Vand til at tvætte deres Fødder og Foder til Æslerne.
25 Suka shirya kyautansu domin isowar Yusuf da rana, gama sun ji cewa zai ci abinci a nan.
Og de fremtog deres Gave, før Josef kom hjem ved Middagstid, thi de hørte, at de skulde spise der.
26 Sa’ad da Yusuf ya zo gida, sai suka ba shi kyautai da suka kawo, suka rusuna a gabansa har ƙasa.
Da Josef trådte ind i Huset, bragte de ham den Gave, de havde med, og kastede sig til Jorden for ham.
27 Ya tambaye su, yaya suke, sa’an nan ya ce, “Yaya tsohon nan mahaifinku da kuka faɗa mini? Yana da rai har yanzu?”
Han hilste på dem og spurgte: "Går det eders gamle Fader vel, ham, I talte om? Lever han endnu?"
28 Suka amsa, “Bawanka mahaifinmu yana da rai har yanzu da kuma ƙoshin lafiya.” Suka kuma rusuna suka yi mubaya’a.
De svarede: "Det går din Træl, vor Fader, vel; han lever endnu!" Og de bøjede sig og kastede sig til Jorden.
29 Da ya ɗaga idanu, sai ya ga ɗan’uwansa Benyamin, ɗan mahaifiyarsa, sai ya yi tambaya, “Wannan ne ƙaramin ɗan’uwanku, wanda kuka faɗa mini a kai?” Ya kuma ce, “Allah yă yi maka albarka, ɗana.”
Da han så fik Øje på sin kødelige Broder Benjamin, sagde han: "Er det så eders yngste Broder, som I talte til mig om?" Og han sagde: "Gud være dig nådig, min Søn!"
30 Saboda motsi mai zurfi da zuciyarsa ta yi da ganin ɗan’uwansa, sai Yusuf ya gaggauta ya fita, ya nemi wuri yă yi kuka. Ya shiga ɗakinsa ya yi kuka a can.
Men Josef brød hurtigt af, thi Kærligheden til Broderen blussede op i ham, og han kæmpede med Gråden; derfor gik han ind i sit Kammer og græd der.
31 Bayan ya wanke fuskarsa, sai ya fito ya daure, ya umarta, “A kawo abinci.”
Men da han havde badet sit Ansigt, kom han ud, og han beherskede sig og sagde: "Sæt Maden frem!"
32 Sai aka raba musu abinci, nasa shi kaɗai su kuma su kaɗai, domin Masarawa ba sa cin abinci tare da Ibraniyawa, gama wannan abin ƙyama ne ga Masarawa.
Så blev Maden sat frem særskilt for ham og for dem og for de Ægyptere, der spiste hos ham; thi Ægypterne kan ikke spise sammen med Hebræere, det er dem en Vederstyggelighed.
33 Aka zaunar da’yan’uwan Yusuf a gabansa bisa ga shekarunsu, daga ɗan fari zuwa auta.’Yan’uwan kuwa suka duddubi juna suna mamaki.
De blev bænket foran ham efter Alder, den førstefødte øverst og den yngste nederst, og Mændene undrede sig og så på hverandre;
34 Daga teburin da yake a gaban Yusuf aka riƙa ɗibar rabonsu ana kai musu, amma rabon Benyamin ya yi biyar ɗin na kowannensu. Suka kuwa sha, suka yi murna tare da shi.
og han lod dem bringe Mad fra sit eget Bord, og Benjamin fik fem Gange så meget som hver af de andre. Og de drak og blev lystige sammen med ham.

< Farawa 43 >