< Farawa 42 >

1 Sa’ad da Yaƙub ya sami labari cewa akwai hatsi a Masar, sai ya ce wa’ya’yansa maza, “Don me kuke duban juna kawai?”
Da Jakob fikk vite at det var korn i Egypten, sa han til sine sønner: Hvorfor sitter I og ser på hverandre?
2 Ya ci gaba, “Na ji cewa akwai hatsi a Masar. Ku gangara can ku sayo mana, domin mu rayu kada mu mutu.”
Og han sa: Jeg har hørt at det er korn i Egypten; dra dit ned og kjøp korn til oss der, så vi kan leve og ikke dø!
3 Sai goma daga cikin’yan’uwan Yusuf suka gangara don su saya hatsi daga Masar.
Da drog Josefs ti brødre ned for å kjøpe korn i Egypten.
4 Amma Yaƙub bai aiki Benyamin, ɗan’uwan Yusuf tare da sauran ba, gama yana tsoro kada wani abu yă faru da shi.
Men Benjamin, Josefs bror, sendte Jakob ikke avsted med hans brødre; for han sa: Det kunde møte ham en ulykke.
5 Sai’ya’yan Yaƙub suka isa Masar tare da sauran mutanen don sayen abinci, gama yunwar ta kai yankin Kan’ana ma.
Så kom Israels sønner for å kjøpe korn blandt alle de andre som kom; for det var hungersnød i Kana'ans land.
6 To, Yusuf ne gwamnar ƙasar wanda yake sayar da hatsi ga dukan mutanenta. Saboda haka sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka isa, sai suka rusuna masa har ƙasa da fuskokinsu.
Og Josef var den som rådet i landet; det var han som solgte korn til alt folket i landet; og Josefs brødre kom og bøide sig med sitt ansikt til jorden for ham.
7 Nan da nan da Yusuf ya ga’yan’uwansa, sai ya gane su, amma ya yi kamar baƙo, ya kuma yi musu magana da tsawa. Ya tambaya, “Daga ina kuka fito?” Suka amsa, “Daga ƙasar Kan’ana, don mu saya abinci.”
Da Josef så sine brødre, kjente han dem igjen; men han lot som om de var fremmede for ham, og talte hårdt til dem og sa til dem: Hvor kommer I fra? De sa: Fra Kana'ans land for å kjøpe korn.
8 Ko da yake Yusuf ya gane’yan’uwansa, su ba su gane shi ba.
Josef kjente sine brødre, men de kjente ikke ham.
9 Sa’an nan ya tuna da mafarkansa game da su, ya kuma ce musu, “Ku’yan leƙen asiri ne! Kun zo don ku leƙi asirin ƙasar ku ga inda ba ta da tsaro.”
Og Josef kom i hu det han hadde drømt om dem, og sa til dem: I er speidere, I er kommet for å se hvor landet ligger åpent.
10 Suka amsa suka ce, “A’a, ranka yă daɗe, bayinka sun zo don saya abinci ne.
De svarte ham: Nei, herre, dine tjenere er kommet for å kjøpe korn.
11 Mu duka’ya’yan mutum ɗaya maza ne. Bayinka mutane ne masu gaskiya, ba’yan leƙen asiri ba ne.”
Vi er alle sønner av én mann; vi er ærlige folk, dine tjenere er ikke speidere.
12 Ya ce musu “Sam! Kun zo ne ku ga inda ƙasarmu babu tsaro.”
Men han sa til dem: Jo, I er kommet for å se hvor landet ligger åpent.
13 Amma suka amsa suka ce, “Bayinka dā su goma sha biyu ne,’yan’uwa,’ya’yan mutum guda maza, wanda yake zama a ƙasar Kan’ana. Ƙaraminmu yanzu yana tare da mahaifinmu, ɗayan kuma ya rasu.”
Men de sa: Vi, dine tjenere, er tolv brødre, sønner av én mann i Kana'ans land, den yngste er nu hjemme hos vår far, og én er ikke mere til.
14 Yusuf ya ce musu, “Daidai ne yadda na faɗa muku. Ku’yan leƙen asiri ne!
Josef sa til dem: Det er som jeg har sagt til eder: I er speidere.
15 Ga kuwa yadda za a gwada ku. Muddin Fir’auna yana a raye, ba za ku bar wannan wuri ba sai ƙaramin ɗan’uwanku ya zo nan.
Men nu skal I prøves: Så sant Farao lever, skal I ikke komme herfra før eders yngste bror kommer hit.
16 Ku aiki ɗaya daga cikinku yă kawo ɗan’uwanku; za a sa sauranku a kurkuku, saboda a gwada maganarku a ga ko gaskiya ce kuke faɗi. In ba haka ba, to, da ran Fir’auna, ku’yan leƙen asiri ne!”
Send en av eder avsted for å hente eders bror, men I andre skal holdes fanget, og eders ord skal prøves, om det er sant det I sier; hvis ikke, så er I, så sant Farao lever, speidere.
17 Ya kuwa sa su duka a kurkuku na kwana uku.
Og han holdt dem alle sammen i fengsel i tre dager.
18 A rana ta uku, Yusuf ya ce musu, “Ku yi wannan za ku kuwa rayu, gama ina tsoron Allah.
Men den tredje dag sa Josef til dem: Gjør som jeg nu sier, så skal I leve! Jeg frykter Gud.
19 In ku mutane masu gaskiya ne, ku bar ɗaya daga cikin’yan’uwanku yă zauna a kurkuku, yayinda sauranku su tafi, su kai hatsi don gidajenku da suke yunwa.
Dersom I er ærlige folk, så skal en av eder brødre bli tilbake i fengslet, men I andre kan dra avsted og ha med eder korn til hjelp mot hungersnøden i eders hjem,
20 Amma dole ku kawo ƙaramin ɗan’uwanku gare ni, saboda a tabbatar da maganarku har ba za ku mutu ba.” Suka kuwa yi haka.
og før eders yngste bror til mig, så eders ord kan sannes, og I ikke skal dø. Og de så gjorde.
21 Sai suka ce wa juna, “Tabbatacce ana hukunta mu ne saboda ɗan’uwanmu. Mun ga yadda ya yi wahala sa’ad da ya roƙe mu saboda ransa, amma ba mu saurare shi ba, shi ya sa wannan wahala ta zo mana.”
Og de sa sig imellem: Sannelig, vi har skyld på oss for vår bror. Vi så hans sjeleangst da han bønnfalt oss, og vi vilde ikke høre; derfor er denne nød kommet over oss.
22 Ruben ya amsa, “Ban faɗa muku cewa kada ku ɗauki alhakin yaron nan ba, sai kuka ƙi ji, to, yau ga alhakin jininsa muke biya.”
Da tok Ruben til orde og sa til dem: Sa jeg ikke til eder: Gjør ikke synd mot gutten? Men I vilde ikke høre; se, derfor kreves nu hans blod.
23 Ba su san cewa Yusuf yana jin su ba, da yake yana amfani da mai fassara ne.
Men de visste ikke at Josef forstod det; for han brukte tolk når han talte med dem.
24 Sai ya juya daga gare su ya yi kuka, sa’an nan ya dawo ya yi musu magana kuma. Ya sa aka ɗauke Simeyon daga gare su, aka daure shi a idanunsu.
Og han vendte sig fra dem og gråt. Så vendte han sig til dem igjen og talte til dem, og han tok Simeon fra dem og lot ham binde så de så på.
25 Yusuf ya yi umarni a cika buhunansu da hatsi, a kuma sa azurfan kowane mutum a cikin buhunsa, a kuma ba su kalaci don tafiyarsu. Bayan aka yi musu wannan,
Og Josef bød sine folk at de skulde fylle deres sekker med korn og legge enhvers penger igjen i hans sekk og gi dem niste med på veien. Og de gjorde således med dem.
26 suka jibga hatsinsu a kan jakuna, sai suka kama hanya.
Så la de kornet på sine asener og drog derfra.
27 A wurin da suka tsaya don su kwana, ɗaya daga cikinsu ya buɗe buhunsa don yă ciyar da jakinsa, sai ya ga azurfansa a bakin buhunsa.
Men da en av dem åpnet sin sekk for å gi sitt asen fôr i herberget, da fikk han se sine penger, de lå øverst i hans sekk.
28 Sai ya ce wa’yan’uwansa, “An mayar mini da azurfata. Ga shi a cikin buhuna.” Zuciyarsu ta karai, suka dubi juna suna rawan jiki, suka ce, “Mene ne wannan da Allah ya yi mana?”
Og han sa til sine brødre: Mine penger er kommet igjen, og se, de ligger her i min sekk. Da blev de motfalne og vendte sig forferdet til hverandre og sa: Hvad er det Gud har gjort mot oss?
29 Sa’ad da suka zo wurin mahaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana, suka faɗa masa dukan abin da ya faru da su. Suka ce,
Så kom de hjem til Jakob, sin far, i Kana'ans land, og de fortalte ham alt det som hadde hendt dem, og sa:
30 “Mutumin da yake shugaba a ƙasar ya yi mana matsananciyar magana, ya kuma ɗauke mu tamƙar’yan leƙen asirin ƙasa.
Mannen som råder der i landet, talte hårdt til oss og tok oss for folk som vilde speide ut landet.
31 Amma muka ce masa, ‘Mu masu gaskiya ne; mu ba’yan leƙen asiri ba ne.
Og vi sa til ham: Vi er ærlige folk, vi er ikke speidere;
32 Dā mu’yan’uwa ne goma sha biyu,’ya’yan mahaifi guda maza. Ɗayanmu ya rasu, kuma ƙaramin yanzu yana tare da mahaifinmu a Kan’ana.’
vi er tolv brødre, alle sønner av samme far, én er ikke mere til, og den yngste er nu hjemme hos vår far i Kana'ans land.
33 “Sai mutumin wanda yake shugaba a kan ƙasar ya ce mana, ‘Ga yadda zan san ko ku mutane masu gaskiya ne. Ku bar ɗaya daga cikin’yan’uwanku a nan tare da ni, ku ɗauki abinci domin gidajenku masu yunwa, ku tafi.
Da sa mannen som råder der i landet, til oss: Av dette vil jeg forstå om I er ærlige folk: La en av eder brødre bli her hos mig og ta hvad I trenger mot hungersnøden i eders hjem, og far eders vei;
34 Amma ku kawo mini ƙaramin ɗan’uwanku domin in san cewa ku ba’yan leƙen asiri ba ne, amma mutane ne masu gaskiya. Sa’an nan zan mayar muku da ɗan’uwanku, ku kuma iya yin sana’a a ƙasar.’”
og kom så hit til mig med eders yngste bror, så jeg kan forstå at I ikke er speidere, men ærlige folk! Da vil jeg gi eder eders bror igjen, og I kan fritt dra omkring i landet.
35 Yayinda suke juyewa hatsi daga buhunansu, sai ga ƙunshin azurfan kowane mutum a buhunsa! Sa’ad da su da mahaifinsu suka ga ƙunshe-ƙunshen kuɗi, suka firgita.
Da de så tømte sine sekker, se, da lå enhvers pengepung i hans sekk; og da de og deres far så pengepungene, blev de redde.
36 Yaƙub mahaifinsu, ya ce musu, “Kun sa ni rashin’ya’yana. Yusuf ya rasu, Simeyon kuma ba ya nan, yanzu kuma kuna so ku ɗauki Benyamin. Kome yana gāba da ni!”
Og Jakob, deres far, sa til dem: I gjør mig barnløs; Josef er ikke mere til, og Simeon er ikke mere til, og Benjamin vil I ta fra mig; det kommer over mig alt sammen.
37 Sai Ruben ya ce wa mahaifinsa, “Ka kashe dukan’ya’yana maza, in ban dawo da shi gare ka ba. Ka sa shi ga kulawata, zan kuwa dawo da shi.”
Da sa Ruben til sin far: Begge mine sønner kan du drepe hvis jeg ikke kommer tilbake til dig med ham; gi ham i min hånd, så vil jeg føre ham tilbake til dig.
38 Amma Yaƙub ya ce, “Ɗana ba zai gangara zuwa can tare da ku ba, ɗan’uwansa ya rasu, shi ne kaɗai ya rage. In wani abu ya faru da shi a tafiyar da za ku yi, za ku sa furfurata ta gangara zuwa kabari cikin baƙin ciki.” (Sheol h7585)
Men han sa: Min sønn skal ikke dra ned med eder; for hans bror er død, og han er alene tilbake, og dersom det møter ham nogen ulykke på den vei som I drar, så kommer I til å sende mine grå hår med sorg ned i dødsriket. (Sheol h7585)

< Farawa 42 >