< Farawa 42 >

1 Sa’ad da Yaƙub ya sami labari cewa akwai hatsi a Masar, sai ya ce wa’ya’yansa maza, “Don me kuke duban juna kawai?”
Or Jacob apprenant que l’on vendait des vivres en Égypte, dit à ses fils: Pourquoi êtes-vous si négligents?
2 Ya ci gaba, “Na ji cewa akwai hatsi a Masar. Ku gangara can ku sayo mana, domin mu rayu kada mu mutu.”
J’ai appris qu’on vend du blé en Égypte; descendez-y, et achetez ce qui nous est nécessaire, afin que nous puissions vivre, et que nous ne soyons pas consumés par la disette.
3 Sai goma daga cikin’yan’uwan Yusuf suka gangara don su saya hatsi daga Masar.
Ainsi, descendant pour acheter du blé en Égypte, les dix frères de Joseph
4 Amma Yaƙub bai aiki Benyamin, ɗan’uwan Yusuf tare da sauran ba, gama yana tsoro kada wani abu yă faru da shi.
(Benjamin ayant été retenu dans la maison par Jacob qui avait dit à ses frères: C’est de peur qu’en chemin il n’éprouve quelque accident)
5 Sai’ya’yan Yaƙub suka isa Masar tare da sauran mutanen don sayen abinci, gama yunwar ta kai yankin Kan’ana ma.
Entrèrent dans la terre d’Égypte avec d’autres qui allaient pour en acheter; car la famine était dans la terre de Chanaan.
6 To, Yusuf ne gwamnar ƙasar wanda yake sayar da hatsi ga dukan mutanenta. Saboda haka sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka isa, sai suka rusuna masa har ƙasa da fuskokinsu.
Or Joseph était gouverneur dans la terre d’Égypte, et c’est selon sa volonté que le blé se vendait aux peuples. Lors donc que ses frères se furent prosternés devant lui
7 Nan da nan da Yusuf ya ga’yan’uwansa, sai ya gane su, amma ya yi kamar baƙo, ya kuma yi musu magana da tsawa. Ya tambaya, “Daga ina kuka fito?” Suka amsa, “Daga ƙasar Kan’ana, don mu saya abinci.”
Et qu’il les eut reconnus, il leur parlait durement, comme à des étrangers, leur demandant: D’où êtes-vous venus? Ils répondirent: De la terre de Chanaan, afin d’acheter ce qui est nécessaire à la vie.
8 Ko da yake Yusuf ya gane’yan’uwansa, su ba su gane shi ba.
Mais cependant reconnaissant ses frères, il ne fut pas reconnu d’eux.
9 Sa’an nan ya tuna da mafarkansa game da su, ya kuma ce musu, “Ku’yan leƙen asiri ne! Kun zo don ku leƙi asirin ƙasar ku ga inda ba ta da tsaro.”
Et se souvenant des songes qu’autrefois il avait vus, il leur dit: Vous êtes des espions; c’est pour voir les endroits les plus faibles du pays, que vous êtes venus.
10 Suka amsa suka ce, “A’a, ranka yă daɗe, bayinka sun zo don saya abinci ne.
Ils répondirent: Il n’en est pas ainsi, seigneur; mais vos serviteurs sont venus pour acheter des vivres,
11 Mu duka’ya’yan mutum ɗaya maza ne. Bayinka mutane ne masu gaskiya, ba’yan leƙen asiri ba ne.”
Nous sommes tous fils d’un seul homme; c’est en gens paisibles que nous sommes venus; et vos serviteurs ne méditent rien de mal.
12 Ya ce musu “Sam! Kun zo ne ku ga inda ƙasarmu babu tsaro.”
Joseph leur repartit: Il en est autrement; vous êtes venus pour observer les places de l’Égypte qui ne sont pas fortifiées.
13 Amma suka amsa suka ce, “Bayinka dā su goma sha biyu ne,’yan’uwa,’ya’yan mutum guda maza, wanda yake zama a ƙasar Kan’ana. Ƙaraminmu yanzu yana tare da mahaifinmu, ɗayan kuma ya rasu.”
Mais eux: Nous, vos serviteurs, disent-ils, nous sommes douze frères, fils d’un seul homme dans la terre de Chanaan; le plus jeune est avec notre père, et l’autre n’est plus.
14 Yusuf ya ce musu, “Daidai ne yadda na faɗa muku. Ku’yan leƙen asiri ne!
C’est, reprit-il, ce que j’ai dit: Vous êtes des espions.
15 Ga kuwa yadda za a gwada ku. Muddin Fir’auna yana a raye, ba za ku bar wannan wuri ba sai ƙaramin ɗan’uwanku ya zo nan.
Dès maintenant, je vous éprouverai: par la vie de Pharaon, vous ne sortirez pas d’ici, jusqu’à ce que vienne votre frère le plus jeune.
16 Ku aiki ɗaya daga cikinku yă kawo ɗan’uwanku; za a sa sauranku a kurkuku, saboda a gwada maganarku a ga ko gaskiya ce kuke faɗi. In ba haka ba, to, da ran Fir’auna, ku’yan leƙen asiri ne!”
Envoyez l’un d’entre vous, et qu’il l’amène, mais vous, vous serez dans les liens jusqu’à ce qu’il soit prouvé que ce que vous avez dit est vrai ou faux: autrement, par la vie de Pharaon, vous êtes des espions.
17 Ya kuwa sa su duka a kurkuku na kwana uku.
Il les mit donc en prison pendant trois jours.
18 A rana ta uku, Yusuf ya ce musu, “Ku yi wannan za ku kuwa rayu, gama ina tsoron Allah.
Mais, au troisième jour les ayant tirés de prison, il leur dit: Faites ce que j’ai dit et vous vivrez; car je crains Dieu.
19 In ku mutane masu gaskiya ne, ku bar ɗaya daga cikin’yan’uwanku yă zauna a kurkuku, yayinda sauranku su tafi, su kai hatsi don gidajenku da suke yunwa.
Si vous êtes des gens paisibles, que l’un de vos frères soit enchaîné dans la prison, et vous, allez et portez le blé que vous avez acheté dans vos maisons;
20 Amma dole ku kawo ƙaramin ɗan’uwanku gare ni, saboda a tabbatar da maganarku har ba za ku mutu ba.” Suka kuwa yi haka.
Mais amenez-moi votre frère le plus jeune, afin que je puisse vérifier vos paroles, et que vous ne mouriez pas. Ils firent comme il avait dit.
21 Sai suka ce wa juna, “Tabbatacce ana hukunta mu ne saboda ɗan’uwanmu. Mun ga yadda ya yi wahala sa’ad da ya roƙe mu saboda ransa, amma ba mu saurare shi ba, shi ya sa wannan wahala ta zo mana.”
Et ils se dirent les uns aux autres: C’est justement que nous souffrons tout ceci, parce que nous avons péché contre notre frère, voyant l’angoisse de son âme, quand il nous priait, et nous ne l’avons pas écouté: c’est pour cela qu’est venue sur nous cette tribulation.
22 Ruben ya amsa, “Ban faɗa muku cewa kada ku ɗauki alhakin yaron nan ba, sai kuka ƙi ji, to, yau ga alhakin jininsa muke biya.”
Un seul d’entre eux, Ruben dit: Ne vous ai-je pas dit: Ne péchez pas contre cet enfant? et vous ne m’avez pas écouté: voilà que son sang est redemandé.
23 Ba su san cewa Yusuf yana jin su ba, da yake yana amfani da mai fassara ne.
Or, ils ne savaient pas que Joseph les entendît, parce que c’est par interprète qu’il leur parlait.
24 Sai ya juya daga gare su ya yi kuka, sa’an nan ya dawo ya yi musu magana kuma. Ya sa aka ɗauke Simeyon daga gare su, aka daure shi a idanunsu.
Mais il se retira un moment et pleura: puis revenu, il leur parla.
25 Yusuf ya yi umarni a cika buhunansu da hatsi, a kuma sa azurfan kowane mutum a cikin buhunsa, a kuma ba su kalaci don tafiyarsu. Bayan aka yi musu wannan,
Et prenant Siméon et le liant, eux présents, il commanda à ses ministres qu’ils emplissent leurs sacs de blé, et qu’ils remissent l’argent de chacun d’eux dans son sac, en leur donnant de plus des vivres pour la route: ceux-ci firent ainsi.
26 suka jibga hatsinsu a kan jakuna, sai suka kama hanya.
Ainsi les frères de Joseph, emportant leur blé sur leurs ânes, partirent.
27 A wurin da suka tsaya don su kwana, ɗaya daga cikinsu ya buɗe buhunsa don yă ciyar da jakinsa, sai ya ga azurfansa a bakin buhunsa.
Or l’un d’eux ayant ouvert son sac pour donner à manger à sa bête dans l’hôtellerie, et ayant vu son argent à l’entrée du sac,
28 Sai ya ce wa’yan’uwansa, “An mayar mini da azurfata. Ga shi a cikin buhuna.” Zuciyarsu ta karai, suka dubi juna suna rawan jiki, suka ce, “Mene ne wannan da Allah ya yi mana?”
Dit à ses frères: Mon argent m’a été rendu, le voici dans le sac. Etonnés et troublés, ils se disaient mutuellement: Qu’est-ce que Dieu nous a fait?
29 Sa’ad da suka zo wurin mahaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana, suka faɗa masa dukan abin da ya faru da su. Suka ce,
Cependant ils vinrent vers Jacob leur père dans la terre de Chanaan, et ils lui racontèrent tout ce qui leur était arrivé, disant:
30 “Mutumin da yake shugaba a ƙasar ya yi mana matsananciyar magana, ya kuma ɗauke mu tamƙar’yan leƙen asirin ƙasa.
Le maître de ce pays nous a parlé durement, et il a cru que nous étions des explorateurs de la contrée.
31 Amma muka ce masa, ‘Mu masu gaskiya ne; mu ba’yan leƙen asiri ba ne.
Nous lui avons répondu: Nous sommes des gens paisibles, et nous ne dressons aucune embûche.
32 Dā mu’yan’uwa ne goma sha biyu,’ya’yan mahaifi guda maza. Ɗayanmu ya rasu, kuma ƙaramin yanzu yana tare da mahaifinmu a Kan’ana.’
Nous sommes douze frères, engendrés d’un seul père: l’un n’est plus, et le plus jeune est avec notre père dans la terre de Chanaan.
33 “Sai mutumin wanda yake shugaba a kan ƙasar ya ce mana, ‘Ga yadda zan san ko ku mutane masu gaskiya ne. Ku bar ɗaya daga cikin’yan’uwanku a nan tare da ni, ku ɗauki abinci domin gidajenku masu yunwa, ku tafi.
Il nous a reparti: Voici comment j’éprouverai si vous êtes des gens paisibles; laissez un de vos frères auprès de moi, et prenez les provisions nécessaires à vos maisons, et vous en allez.
34 Amma ku kawo mini ƙaramin ɗan’uwanku domin in san cewa ku ba’yan leƙen asiri ba ne, amma mutane ne masu gaskiya. Sa’an nan zan mayar muku da ɗan’uwanku, ku kuma iya yin sana’a a ƙasar.’”
Mais votre frère le plus jeune, amenez-le-moi, afin que je sache que vous n’êtes pas des espions, et que vous puissiez recouvrer celui qui est retenu dans les liens, et qu’ensuite vous ayez la liberté d’acheter ce que vous voudrez.
35 Yayinda suke juyewa hatsi daga buhunansu, sai ga ƙunshin azurfan kowane mutum a buhunsa! Sa’ad da su da mahaifinsu suka ga ƙunshe-ƙunshen kuɗi, suka firgita.
Ces choses dites, comme ils versaient leur blé, ils trouvèrent à l’entrée des sacs chacun leur argent lié; et étant tous ensemble saisis d’effroi,
36 Yaƙub mahaifinsu, ya ce musu, “Kun sa ni rashin’ya’yana. Yusuf ya rasu, Simeyon kuma ba ya nan, yanzu kuma kuna so ku ɗauki Benyamin. Kome yana gāba da ni!”
Jacob leur père dit: Vous avez fait que je suis sans enfants: Joseph n’est plus, Siméon est retenu dans les liens, et vous enlèverez Benjamin: c’est sur moi que tous ces malheurs sont retombés.
37 Sai Ruben ya ce wa mahaifinsa, “Ka kashe dukan’ya’yana maza, in ban dawo da shi gare ka ba. Ka sa shi ga kulawata, zan kuwa dawo da shi.”
Ruben lui répondit: Tuez mes deux fils, si je ne vous le ramène; remettez-le en ma main, et moi, je vous le rendrai.
38 Amma Yaƙub ya ce, “Ɗana ba zai gangara zuwa can tare da ku ba, ɗan’uwansa ya rasu, shi ne kaɗai ya rage. In wani abu ya faru da shi a tafiyar da za ku yi, za ku sa furfurata ta gangara zuwa kabari cikin baƙin ciki.” (Sheol h7585)
Mais Jacob: Non, dit-il, il ne descendra pas avec vous, mon fils: son frère est mort, et lui seul est resté; si quelque chose de fâcheux lui arrivait dans le pays où vous allez, vous feriez descendre mes cheveux blancs avec douleur dans les enfers. (Sheol h7585)

< Farawa 42 >