< Farawa 42 >
1 Sa’ad da Yaƙub ya sami labari cewa akwai hatsi a Masar, sai ya ce wa’ya’yansa maza, “Don me kuke duban juna kawai?”
Der Jakob saa, at Korn var til fals i Ægypten, da sagde Jakob til sine Sønner: Hvi se I paa hverandre?
2 Ya ci gaba, “Na ji cewa akwai hatsi a Masar. Ku gangara can ku sayo mana, domin mu rayu kada mu mutu.”
Og han sagde: Se, jeg hører, at der er Korn til føls i Ægypten, farer did ned og køber til os derfra, at vi maa leve og ikke dø.
3 Sai goma daga cikin’yan’uwan Yusuf suka gangara don su saya hatsi daga Masar.
Saa droge Josefs ti Brødre ned at købe Korn i Ægypten.
4 Amma Yaƙub bai aiki Benyamin, ɗan’uwan Yusuf tare da sauran ba, gama yana tsoro kada wani abu yă faru da shi.
Men Jakob lod ikke Benjamin, Josefs Broder, fare med sine Brødre; thi han sagde: Der kunde vederfares ham nogen Ulykke.
5 Sai’ya’yan Yaƙub suka isa Masar tare da sauran mutanen don sayen abinci, gama yunwar ta kai yankin Kan’ana ma.
Saa kom Israels Sønner at købe iblandt dem, som kom; thi der var Hunger i Landet Kanaan.
6 To, Yusuf ne gwamnar ƙasar wanda yake sayar da hatsi ga dukan mutanenta. Saboda haka sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka isa, sai suka rusuna masa har ƙasa da fuskokinsu.
Og Josef var Regent over Landet, han var den, som solgte til alt Folket i Landet; og Josefs Brødre kom, og de faldt ned for ham paa deres Ansigt til Jorden.
7 Nan da nan da Yusuf ya ga’yan’uwansa, sai ya gane su, amma ya yi kamar baƙo, ya kuma yi musu magana da tsawa. Ya tambaya, “Daga ina kuka fito?” Suka amsa, “Daga ƙasar Kan’ana, don mu saya abinci.”
Og Josef saa sine Brødre og kendte dem og holdt sig fremmed mod dem og talede haarde Ting med dem og sagde til dem: Hvorfra komme I? og de sagde: Fra det Land Kanaan for at købe Spise.
8 Ko da yake Yusuf ya gane’yan’uwansa, su ba su gane shi ba.
Og Josef kendte sine Brødre; men de kendte ikke ham.
9 Sa’an nan ya tuna da mafarkansa game da su, ya kuma ce musu, “Ku’yan leƙen asiri ne! Kun zo don ku leƙi asirin ƙasar ku ga inda ba ta da tsaro.”
Og Josef kom de Drømme i Hu, som han havde drømt om dem, og sagde til dem: I ere Spejdere, I ere komne at bese, hvor Landet er blot.
10 Suka amsa suka ce, “A’a, ranka yă daɗe, bayinka sun zo don saya abinci ne.
Og de sagde til ham: Nej, min Herre! men dine Tjenere ere komne for at købe Spise.
11 Mu duka’ya’yan mutum ɗaya maza ne. Bayinka mutane ne masu gaskiya, ba’yan leƙen asiri ba ne.”
Vi ere alle een Mands Sønner, vi ere redelige, dine Tjenere ere ikke Spejdere.
12 Ya ce musu “Sam! Kun zo ne ku ga inda ƙasarmu babu tsaro.”
Og han sagde til dem: Nej, men I ere komne for at bese, hvor Landet er blot.
13 Amma suka amsa suka ce, “Bayinka dā su goma sha biyu ne,’yan’uwa,’ya’yan mutum guda maza, wanda yake zama a ƙasar Kan’ana. Ƙaraminmu yanzu yana tare da mahaifinmu, ɗayan kuma ya rasu.”
De svarede: Vi, dine Tjenere, vare tolv Brødre, een Mands Sønner i Kanaans Land; og se, den yngste er endnu hos vor Fader, men den ene er ikke til.
14 Yusuf ya ce musu, “Daidai ne yadda na faɗa muku. Ku’yan leƙen asiri ne!
Og Josef sagde til dem: Det er det, som jeg har talet til eder, der jeg sagde: I ere Spejdere.
15 Ga kuwa yadda za a gwada ku. Muddin Fir’auna yana a raye, ba za ku bar wannan wuri ba sai ƙaramin ɗan’uwanku ya zo nan.
Derpaa skulle I prøves: saa sandt Farao lever, skulle I ikke komme herfra, uden eders yngste Broder kommer hid.
16 Ku aiki ɗaya daga cikinku yă kawo ɗan’uwanku; za a sa sauranku a kurkuku, saboda a gwada maganarku a ga ko gaskiya ce kuke faɗi. In ba haka ba, to, da ran Fir’auna, ku’yan leƙen asiri ne!”
Sender een af eder bort, at han skal hente eders Broder; men I skulle være fangne, og eders Ord skulle prøves, om I fare med Sandhed; thi hvis ikke, da ere I, saa sandt Farao lever, Spejdere.
17 Ya kuwa sa su duka a kurkuku na kwana uku.
Og han satte dem tilsammen i Forvaring i tre Dage.
18 A rana ta uku, Yusuf ya ce musu, “Ku yi wannan za ku kuwa rayu, gama ina tsoron Allah.
Men den tredje Dag sagde Josef til dem: Gører dette, saa skulle I leve; jeg frygter Gud.
19 In ku mutane masu gaskiya ne, ku bar ɗaya daga cikin’yan’uwanku yă zauna a kurkuku, yayinda sauranku su tafi, su kai hatsi don gidajenku da suke yunwa.
Dersom I ere redelige, da lader een af eders Brødre blive som Fange i eders Forvaringshus; men farer I andre hen og fører det hjem, som I have købt mod Hungeren, for eders Huse,
20 Amma dole ku kawo ƙaramin ɗan’uwanku gare ni, saboda a tabbatar da maganarku har ba za ku mutu ba.” Suka kuwa yi haka.
og henter eders yngste Broder til mig, saa skulle eders Ord tros, og I skulle ikke dø; og de gjorde saaledes.
21 Sai suka ce wa juna, “Tabbatacce ana hukunta mu ne saboda ɗan’uwanmu. Mun ga yadda ya yi wahala sa’ad da ya roƙe mu saboda ransa, amma ba mu saurare shi ba, shi ya sa wannan wahala ta zo mana.”
Men de sagde den ene til den anden: Vi have sandelig forskyldt dette for vor Broder, da vi saa hans Sjæls Angest, idet han bad os, og vi vilde ikke høre, derfor kommer denne Angest over os.
22 Ruben ya amsa, “Ban faɗa muku cewa kada ku ɗauki alhakin yaron nan ba, sai kuka ƙi ji, to, yau ga alhakin jininsa muke biya.”
Og Ruben svarede dem og sagde: Talede jeg det ikke til eder, der jeg sagde: synder ikke mod Drengen, og I hørte ikke? og se, nu kræves ogsaa hans Blod.
23 Ba su san cewa Yusuf yana jin su ba, da yake yana amfani da mai fassara ne.
Men de vidste ikke, at Josef forstod det; thi der var en Tolk imellem dem.
24 Sai ya juya daga gare su ya yi kuka, sa’an nan ya dawo ya yi musu magana kuma. Ya sa aka ɗauke Simeyon daga gare su, aka daure shi a idanunsu.
Og han vendte sig fra dem og græd, og han vendte sig til dem igen og talede med dem og tog Simeon fra dem og lod ham binde for deres Øjne.
25 Yusuf ya yi umarni a cika buhunansu da hatsi, a kuma sa azurfan kowane mutum a cikin buhunsa, a kuma ba su kalaci don tafiyarsu. Bayan aka yi musu wannan,
Og Josef befalede, at man skulde fylde deres Poser med Korn og give dem deres Penge igen, hver i sin Sæk, og give dem Tæring paa Vejen; og han gjorde saa mod dem.
26 suka jibga hatsinsu a kan jakuna, sai suka kama hanya.
Og de lagde deres Korn paa deres Asener og fore derfra.
27 A wurin da suka tsaya don su kwana, ɗaya daga cikinsu ya buɗe buhunsa don yă ciyar da jakinsa, sai ya ga azurfansa a bakin buhunsa.
Men der den ene lod sin Sæk op for at give sit Asen Foder i Herberget, da saa han sine Penge, og se, de laa oven i hans Pose.
28 Sai ya ce wa’yan’uwansa, “An mayar mini da azurfata. Ga shi a cikin buhuna.” Zuciyarsu ta karai, suka dubi juna suna rawan jiki, suka ce, “Mene ne wannan da Allah ya yi mana?”
Og han sagde til sine Brødre: Mine Penge ere komne igen, og se, de ere her i min Pose; da faldt deres Mod, og de forskrækkedes den ene med den anden og sagde: Hvorfor har Gud gjort os dette?
29 Sa’ad da suka zo wurin mahaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana, suka faɗa masa dukan abin da ya faru da su. Suka ce,
Og de kom til Jakob, deres Fader, til Kanaans Land; og de gave ham til Kende alt det, som var dem vederfaret, og sagde:
30 “Mutumin da yake shugaba a ƙasar ya yi mana matsananciyar magana, ya kuma ɗauke mu tamƙar’yan leƙen asirin ƙasa.
Den Mand, som er Herre i Landet, talte os haardelig til og holdt os for Landets Spejdere.
31 Amma muka ce masa, ‘Mu masu gaskiya ne; mu ba’yan leƙen asiri ba ne.
Og vi svarede ham: vi ere redelige, vi ere ikke Spejdere.
32 Dā mu’yan’uwa ne goma sha biyu,’ya’yan mahaifi guda maza. Ɗayanmu ya rasu, kuma ƙaramin yanzu yana tare da mahaifinmu a Kan’ana.’
Vi vare tolv Brødre, vor Faders Sønner, den ene er ikke til, og den yngste er endnu hos vor Fader i Kanaans Land.
33 “Sai mutumin wanda yake shugaba a kan ƙasar ya ce mana, ‘Ga yadda zan san ko ku mutane masu gaskiya ne. Ku bar ɗaya daga cikin’yan’uwanku a nan tare da ni, ku ɗauki abinci domin gidajenku masu yunwa, ku tafi.
Da sagde Manden, Landets Herre, til os: derpaa vil jeg kende, om I ere redelige: lader den ene af eders Brødre blive hos mig, og tager, hvad I behøve mod Hungeren for eders Huse, og farer hen
34 Amma ku kawo mini ƙaramin ɗan’uwanku domin in san cewa ku ba’yan leƙen asiri ba ne, amma mutane ne masu gaskiya. Sa’an nan zan mayar muku da ɗan’uwanku, ku kuma iya yin sana’a a ƙasar.’”
og henter eders yngste Broder til mig, saa kan jeg kende, at I ikke ere Spejdere, men at I ere redelige; saa vil jeg give eder eders Broder igen, og I maa handle i Landet.
35 Yayinda suke juyewa hatsi daga buhunansu, sai ga ƙunshin azurfan kowane mutum a buhunsa! Sa’ad da su da mahaifinsu suka ga ƙunshe-ƙunshen kuɗi, suka firgita.
Og det skete, der de tømte deres Sække, se, da var hvers Pengeknude i hans Sæk; og de saa deres Pengeknuder, de og deres Fader, og frygtede.
36 Yaƙub mahaifinsu, ya ce musu, “Kun sa ni rashin’ya’yana. Yusuf ya rasu, Simeyon kuma ba ya nan, yanzu kuma kuna so ku ɗauki Benyamin. Kome yana gāba da ni!”
Da sagde Jakob, deres Fader, til dem: I berøve mig mine Børn; Josef er ikke til, og Simeon er ikke til, og Benjamin ville I tage hen; over mig kommer det altsammen.
37 Sai Ruben ya ce wa mahaifinsa, “Ka kashe dukan’ya’yana maza, in ban dawo da shi gare ka ba. Ka sa shi ga kulawata, zan kuwa dawo da shi.”
Og Ruben talede til sin Fader og sagde: Du maa slaa begge mine Sønner ihjel, om jeg ikke fører ham til dig igen; giv ham i min Haand, og jeg vil føre ham til dig igen.
38 Amma Yaƙub ya ce, “Ɗana ba zai gangara zuwa can tare da ku ba, ɗan’uwansa ya rasu, shi ne kaɗai ya rage. In wani abu ya faru da shi a tafiyar da za ku yi, za ku sa furfurata ta gangara zuwa kabari cikin baƙin ciki.” (Sheol )
Og han sagde: Min Søn skal ikke fare ned med eder; thi hans Broder er død, og han alene er bleven tilbage, og møder ham nogen Ulykke paa Vejen, som I drage hen paa, da skulle I føre mine graa Haar med Sorg til Graven. (Sheol )