< Farawa 41 >
1 Bayan shekaru biyu cif, Fir’auna ya yi mafarki. A mafarkin, ya ga yana tsaye kusa da Nilu,
Två år därefter hände sig att Farao hade en dröm. Han tyckte sig stå vid Nilfloden.
2 sai ga shanu bakwai masu ƙiba mulmul, suka fito daga kogin, suna kiwo a cikin kyauro.
Och han såg sju kor, vackra och feta, stiga upp ur floden, och de betade i vassen.
3 Bayansu, sai ga waɗansu shanu bakwai, munana, ramammu, suka fito daga Nilu, suka tsaya kusa da waɗancan masu ƙiban, a bakin kogin.
Sedan såg han sju andra kor, fula och magra, stiga upp ur floden; och de ställde sig bredvid de förra korna på stranden av floden.
4 Shanun nan da suke munana ramammu, suka cinye shanu bakwai nan masu ƙiba mulmul. Sai Fir’auna ya farka.
Och de fula och magra korna åto upp de sju vackra och feta korna. Därefter vaknade Farao.
5 Ya sāke yin barci, sai ya yi mafarki na biyu; ya ga kawuna bakwai na dawa, ƙosassu masu kyau, suka yi girma a kara guda.
Men han somnade åter in och såg då i drömmen sju ax, frodiga och vackra, växa på samma strå.
6 Bayansu, sai ga waɗansu kawuna bakwai na dawa, suka fito sirara waɗanda iskar gabas ta sa suka yanƙwane.
Sedan såg han sju andra ax skjuta upp, tunna och svedda av östanvinden;
7 Siraran dawan suka haɗiye kawuna bakwai nan ƙosassu masu kyau. Sai Fir’auna ya farka, ashe, mafarki ne.
och de tunna axen uppslukade de sju frodiga och fulla axen. Därefter vaknade Farao och fann att det var en dröm.
8 Da safe sai hankalinsa ya tashi, saboda haka sai ya aika a kawo dukan masu duba da masu hikima na Masar. Fir’auna ya faɗa musu mafarkansa, amma babu wanda ya iya ba shi fassararsu.
Då han nu om morgonen var orolig till sinnes, sände han ut och lät kalla till sig alla spåmän och alla vise i Egypten. Och Farao förtäljde sina drömmar för dem; men ingen fanns, som kunde uttyda dem för Farao.
9 Sai shugaban masu shayarwa ya ce wa Fir’auna, “Yau an tuna mini da kāsawata.
Då talade överste munskänken till Farao och sade: "Jag måste i dag påminna om mina synder.
10 Sai ya ci gaba ya ce, Fir’auna ya taɓa husata da bayinsa, ya kuma jefa ni da shugaban masu tuya a cikin kurkuku a gidan shugaban masu tsaro.
När Farao en gång var förtörnad på sina tjänare, satte han mig jämte överste bagaren i fängelse i drabanthövitsmannens hus.
11 Kowannenmu ya yi mafarki a wani dare, kowane mafarki kuma ya kasance da ma’anarsa.
Då hade vi båda, jag och han, under samma natt en dröm, och våra drömmar hade var sin särskilda betydelse.
12 To, wani saurayi, mutumin Ibraniyawa ya kasance a can tare da mu, bawan shugaban masu tsaro. Sai muka faɗa masa mafarkanmu, ya kuwa fassara mana su, yana ba wa kowane mutum fassarar mafarkinsa.
Och jämte oss var där en ung hebré, som var tjänare hos hövitsmannen för drabanterna. För honom förtäljde vi våra drömmar, och han uttydde dem för oss; efter som var och en hade drömt gav han en uttydning.
13 Abubuwan kuwa suka kasance daidai yadda ya fassara su gare mu; aka mai da ni a matsayina, ɗaya mutumin kuwa aka rataye shi.”
Och såsom han uttydde för oss, så gick det. Jag blev åter insatt på min plats, och den andre blev upphängd."
14 Sai Fir’auna ya aika a kawo Yusuf, aka kuwa kawo shi da sauri daga kurkuku. Sa’ad da ya yi aski, ya kuma canja tufafinsa, sai ya zo gaban Fir’auna.
Då sände Farao och lät kalla Josef till sig; och man skyndade att föra honom ut ur fängelset. Och han lät raka sig och bytte om kläder och kom inför Farao.
15 Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Na yi mafarki, kuma babu wanda ya iya fassara shi. Amma na ji an ce sa’ad da ka ji mafarki, kana iya fassara shi.”
Och Farao sade till Josef: "Jag har haft en dröm, och ingen finnes, som kan uttyda den. Men jag har hört sägas om dig, att allenast du får höra en dröm, kan du uttyda den."
16 Yusuf ya amsa wa Fir’auna ya ce, “Ba ni ne da iyawar ba, Allah zai iya ba wa Fir’auna amsar da yake nema.”
Josef svarade Farao och sade: "I min makt står det icke; men Gud skall giva Farao ett lyckosamt svar."
17 Sa’an nan Fir’auna ya ce wa Yusuf, “A cikin mafarkina, na ga ina tsaye a bakin Nilu,
Då sade Farao till Josef: "Jag drömde att jag stod på stranden av Nilfloden.
18 sai ga shanu bakwai masu ƙiba mulmul, suka fito daga kogin, suna kiwo a cikin kyauro.
Och jag såg sju kor stiga upp ur floden, feta och vackra, och de betade i vassen.
19 Bayansu kuma, sai ga waɗansu shanu bakwai suka fito ƙanjamammu, munana, ramammu. Ban taɓa ganin irin munanan shanu haka a cikin dukan ƙasar Masar ba.
Sedan såg jag sju andra kor stiga upp, avfallna och mycket fula och magra; i hela Egyptens land har jag icke sett några så fula som dessa.
20 Ramammun shanun nan munana, suka cinye shanun nan bakwai masu ƙiba da suka fito da fari.
Och de magra och fula korna åto upp de sju första, feta korna.
21 Amma ko bayan da suka cinye su, babu wanda zai iya faɗa cewa sun yi haka; suna nan dai munana kamar yadda suke a dā. Sai na farka.
Men när de hade sväljt ned dem, kunde man icke märka att de hade sväljt ned dem, utan de förblevo fula såsom förut. Därefter vaknade jag.
22 “Har yanzu kuma, a cikin mafarkina na ga kawuna bakwai na dawa ƙosassu masu kyau, suna girma a kara guda.
Åter drömde jag och såg då sju ax, fulla och vackra, växa på samma strå.
23 Bayansu, sai ga waɗansu kawuna bakwai suka fito, yanƙwananne sirara waɗanda iskar gabas ta yanƙwane.
Sedan såg jag sju andra ax skjuta upp, förtorkade, tunna och svedda av östanvinden;
24 Siraran kawunan dawan nan suka haɗiye kawuna bakwai nan masu kyau. Na faɗa wannan wa masu duba, amma ba wanda ya iya fassara mini shi.”
och de tunna axen uppslukade de sju vackra axen. Detta omtalade jag för spåmännen; men ingen fanns, som kunde förklara det för mig."
25 Sai Yusuf ya ce wa Fir’auna, “Mafarkan Fir’auna, ɗaya ne. Allah ya bayyana wa Fir’auna abin da yake shirin yi.
Då sade Josef till Farao: "Faraos drömmar hava en och samma betydelse; vad Gud ämnar göra, det har han förkunnat för Farao.
26 Shanu masu kyau nan, shekaru bakwai ne, kawunan dawa bakwai ƙosassun nan kuwa shekaru bakwai ne; mafarkan iri ɗaya ne.
De sju vackra korna betyda sju år, de sju vackra axen betyda ock sju år; drömmarna hava en och samma betydelse.
27 Shanun nan ramammu, munana, da suka zo daga baya, shekaru bakwai ne, haka ma kawuna dawan nan shanyayyu da iskar gabas ta yanƙwane. Shekaru ne bakwai na yunwa.
Och de sju magra och fula korna som stego upp efter dessa betyda sju år, så ock de sju tomma axen, de som voro svedda av östanvinden; sju hungerår skola nämligen komma.
28 “Haka yake kamar yadda na faɗa wa Fir’auna cewa Allah ya nuna wa Fir’auna abin da yake shirin yi.
Detta menade jag, när jag sade till Farao: Vad Gud ämnar göra, det har han låtit Farao veta.
29 Shekaru bakwai na yalwar abinci suna zuwa a dukan ƙasar Masar,
Se, sju år skola komma med stor ymnighet över hela Egyptens land.
30 amma shekaru bakwai na yunwa za su biyo bayansu. Tsananin yunwar za tă sa a manta da dukan isashen abincin da aka samu a ƙasar Masar, yunwa kuwa za tă rufe dukan ƙasar.
Men efter dem skola sju hungerår inträffa, sådana, att man skall förgäta all den förra ymnigheten i Egyptens land, och hungersnöden skall förtära landet.
31 Ba za a tuna da isashen abincin da aka samu a ƙasar ba, domin yunwar da za tă biyo baya za tă zama da tsanani ƙwarai.
Och man skall icke hava något minne av den förra ymnigheten i landet, för den hungersnöds skull som sedan kommer, ty den skall bliva mycket svår.
32 Dalilin da aka ba wa Fir’auna mafarkan nan kashi biyu kuwa shi ne cewa Allah ya riga ya ƙaddara al’amarin. Allah zai aikata shi, ba da daɗewa ba.
Men att Farao har haft drömmen två gånger, det betyder att detta är av Gud bestämt, och att Gud skall låta det ske snart.
33 “Yanzu fa, bari Fir’auna yă nemi mutum mai basira da kuma hikima, yă sa shi yă shugabanci ƙasar Masar.
Må nu alltså Farao utse en förståndig och vis man, som han kan sätta över Egyptens land.
34 Bari Fir’auna yă naɗa komishinoni a kan ƙasar don su karɓi kashi ɗaya bisa biyar na girbin Masar a lokacin shekaru bakwai na yalwar abinci.
Må Farao göra så; må han ock förordna tillsyningsmän över landet och taga upp femtedelen av avkastningen i Egyptens land under de sju ymniga åren.
35 Ya kamata su tara dukan abincin waɗannan shekaru masu kyau da suke zuwa, su yi ajiyar hatsin a ƙarƙashin ikon Fir’auna, don a ajiye a birane don abinci.
Må man under dessa kommande goda år samla in allt som kan tjäna till föda och hopföra säd under Faraos vård i städerna, för att tjäna till föda, och må man sedan förvara den,
36 Ya kamata a adana abincin nan don ƙasar, kāriya shekaru bakwai na yunwa, domin a yi amfani da shi a lokacin shekarun yunwan da za su zo wa Masar, saboda kada ƙasar ta lalace da yunwa.”
så att dessa födoämnen finnas att tillgå för landet under de sju hungerår som skola komma över Egyptens land. Så skall landet icke behöva förgås genom hungersnöden."
37 Shirin ya yi wa Fir’auna da kuma dukan hafsoshinsa kyau.
Det talet behagade Farao och alla hans tjänare.
38 Saboda haka Fir’auna ya tambaye su, “Za mu iya samun wani kamar wannan mutum, wannan wanda Ruhun Allah yake cikinsa?”
Och Farao sade till sina tjänare: "Kunna vi finna någon i vilken Guds Ande så är som i denne?"
39 Sai Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Da yake Allah ya ba ka sanin dukan waɗannan, babu wani mai basira da kuma hikima kamar ka.
Och Farao sade till Josef: "Eftersom Gud har kungjort för dig allt detta, finnes ingen som är så förståndig och vis som du.
40 Za ka shugabanci fadata, kuma dukan mutanena za su zama a ƙarƙashinka. Da sarauta kaɗai zan fi ka girma.”
Du skall förestå mitt hus, och efter dina befallningar skall allt mitt folk rätta sig; allenast däri att tronen förbliver min vill jag vara förmer än du."
41 Saboda haka Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Ga shi na sa ka zama shugaban dukan ƙasar Masar.”
Ytterligare sade Farao till Josef: "Jag sätter dig nu över hela Egyptens land."
42 Sa’an nan Fir’auna ya zare zoben sarauta daga yatsarsa, ya sa shi a yatsan Yusuf. Ya sanya masa rigar lallausan lilin, ya kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa.
Och Farao tog ringen av sin hand och satte den på Josefs hand och lät kläda honom i kläder av fint linne och hängde den gyllene kedjan om hans hals.
43 Ya sa shi ya hau keken yaƙi a matsayi mai binsa na biyu, mutane kuwa suka yi shela a gabansa suna cewa, “A ba da hanya!” Ta haka ya sa shi shugaba a kan dukan ƙasar Masar.
Och han lät honom åka i vagnen närmast efter sin egen, och man utropade framför honom "abrek". Och han satte honom över hela Egyptens land.
44 Sa’an nan Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Ni ne Fir’auna, amma in ba tare da umarninka ba, ba wanda zai ɗaga hannu ko ƙafa a cikin dukan Masar.”
Och Farao sade till Josef: "Jag är Farao; utan din vilja skall ingen i hela Egyptens land lyfta hand eller fot."
45 Fir’auna ya ba wa Yusuf suna Zafenat-Faneya, ya kuma ba shi Asenat’yar Fotifera firist na On, ta zama matarsa. Yusuf kuwa ya zaga dukan ƙasar Masar.
Och Farao gav Josef namnet Safenat-Panea och gav honom till hustru Asenat, dotter till Poti-Fera, prästen i On. Och Josef begav sig ut och besåg Egyptens land.
46 Yusuf yana zuwa shekara talatin sa’ad da ya shiga hidimar Fir’auna sarkin Masar. Yusuf kuwa ya fita daga gaban Fir’auna, ya zaga ko’ina a Masar.
Josef var trettio år gammal, när han stod inför Farao, konungen i Egypten. Och Josef gick ut ifrån Farao och färdades omkring i hela Egyptens land.
47 A shekaru bakwai na yalwa, ƙasar ta ba da amfani mai yawa.
Och landet gav under de sju ymniga åren avkastning i överflöd
48 Yusuf ya tattara dukan abincin da aka samu a waɗannan shekaru bakwai na yalwa a Masar, ya kuma yi ajiyarsu a cikin birane. A kowane birni, ya sa abincin da aka nome a kewayensa.
och under dessa sju år som kommo i Egyptens land samlade han in allt som kunde tjäna till föda och lade upp det i städerna. I var särskild stad lade han upp de födoämnen som man hämtade ifrån fälten däromkring.
49 Sai Yusuf ya tara hatsi da yawan gaske, kamar yashi a bakin teku, har sai da ya kāsa iya auna shi, gama ba a iya aunawa.
Så hopförde Josef säd i stor myckenhet, såsom sanden i havet, till dess man måste upphöra att hålla räkning på den, eftersom det var omöjligt att hålla räkning på den.
50 Kafin shekarun yunwa su zo, Asenat’yar Fotifera, firist na On, ta haifa wa Yusuf’ya’ya maza biyu.
Och åt Josef föddes två söner, innan något hungerår kom; de föddes åt honom av Asenat, dotter till Poti-Fera, prästen i On.
51 Yusuf ya ba wa ɗansa na fari suna Manasse ya ce, “Gama Allah ya sa na mance dukan wahalata da dukan gidan mahaifina.”
Och Josef gav åt den förstfödde namnet Manasse, "ty", sade han, "Gud har låtit mig förgäta all min olycka och hela min faders hus."
52 Ya ba wa ɗansa na biyu suna Efraim ya ce, “Gama Allah ya wadata ni cikin wahalata.”
Och åt den andre gav han namnet Efraim, "ty", sade han, "Gud har gjort mig fruktsam i mitt lidandes land".
53 Shekaru bakwai na yalwa a Masar suka zo ga ƙarshe,
Men de sju ymniga åren som först hade kommit i Egyptens land gingo till ända;
54 sai shekaru bakwai na yunwa suka soma shigowa, kamar yadda Yusuf ya faɗa. Aka yi yunwa ko’ina amma ban da ƙasar Masar. Don akwai abinci.
sedan begynte de sju hungeråren, såsom Josef hade förutsagt. Och hungersnöd uppstod i alla andra länder; men i Egyptens land fanns bröd överallt.
55 Sa’ad da dukan Masar ta fara jin yunwa, sai mutane suka yi wa Fir’auna kuka don abinci. Sai Fir’auna ya ce wa dukan Masarawa, “Ku tafi wurin Yusuf, ku kuma yi abin da ya faɗa muku.”
Och när hela Egyptens land begynte hungra och folket ropade till Farao efter bröd, sade Farao till alla egyptier: "Gån till Josef, och gören vad han säger eder."
56 Sa’ad da yunwa ta bazu a dukan ƙasar, sai Yusuf ya buɗe gidajen ajiya, ya kuma sayar da hatsi ga Masarawa, gama yunwa ta yi tsanani a dukan Masar.
När nu alltså hungersnöd var över hela landet, öppnade Josef alla förrådshus och sålde säd åt egyptierna. Men hungersnöden blev allt större i Egyptens land;
57 Dukan ƙasashe kuwa suka zo Masar don saya hatsi daga Yusuf, gama yunwa ta yi tsanani a dukan duniya.
och från alla länder kom man till Josef i Egypten för att köpa säd, ty hungersnöden blev allt större i alla länder.