< Farawa 41 >

1 Bayan shekaru biyu cif, Fir’auna ya yi mafarki. A mafarkin, ya ga yana tsaye kusa da Nilu,
And it came to pass at the end of two full years, that Pharaoh dreamed: and behold, he stood by the river.
2 sai ga shanu bakwai masu ƙiba mulmul, suka fito daga kogin, suna kiwo a cikin kyauro.
And behold, there came up out of the river seven well-favored cows and fat-fleshed; and they fed in a meadow.
3 Bayansu, sai ga waɗansu shanu bakwai, munana, ramammu, suka fito daga Nilu, suka tsaya kusa da waɗancan masu ƙiban, a bakin kogin.
And behold, seven other cows came up after them out of the river, ill-favored and lean-fleshed; and stood by the [other] cows upon the brink of the river.
4 Shanun nan da suke munana ramammu, suka cinye shanu bakwai nan masu ƙiba mulmul. Sai Fir’auna ya farka.
And the ill-favored and lean-fleshed cows ate up the seven well-favored and fat cows. So Pharaoh awoke.
5 Ya sāke yin barci, sai ya yi mafarki na biyu; ya ga kawuna bakwai na dawa, ƙosassu masu kyau, suka yi girma a kara guda.
And he slept and dreamed the second time: and behold, seven ears of corn came up upon one stalk, rank and good.
6 Bayansu, sai ga waɗansu kawuna bakwai na dawa, suka fito sirara waɗanda iskar gabas ta sa suka yanƙwane.
And behold, seven thin ears and blasted with the east wind sprung up after them.
7 Siraran dawan suka haɗiye kawuna bakwai nan ƙosassu masu kyau. Sai Fir’auna ya farka, ashe, mafarki ne.
And the seven thin ears devoured the seven rank and full ears. And Pharaoh awoke, and behold, [it was] a dream.
8 Da safe sai hankalinsa ya tashi, saboda haka sai ya aika a kawo dukan masu duba da masu hikima na Masar. Fir’auna ya faɗa musu mafarkansa, amma babu wanda ya iya ba shi fassararsu.
And it came to pass in the morning, that his spirit was troubled; and he sent and called for all the magicians of Egypt, and all the wise men thereof: and Pharaoh told them his dream; but [there was] none that could interpret them to Pharaoh.
9 Sai shugaban masu shayarwa ya ce wa Fir’auna, “Yau an tuna mini da kāsawata.
Then spoke the chief butler to Pharaoh, saying, I do remember my faults this day:
10 Sai ya ci gaba ya ce, Fir’auna ya taɓa husata da bayinsa, ya kuma jefa ni da shugaban masu tuya a cikin kurkuku a gidan shugaban masu tsaro.
Pharaoh was wroth with his servants, and put me in custody in the captain of the guard's house, [both] me, and the chief baker:
11 Kowannenmu ya yi mafarki a wani dare, kowane mafarki kuma ya kasance da ma’anarsa.
And we dreamed a dream in one night, I and he: we dreamed each man according to the interpretation of his dream.
12 To, wani saurayi, mutumin Ibraniyawa ya kasance a can tare da mu, bawan shugaban masu tsaro. Sai muka faɗa masa mafarkanmu, ya kuwa fassara mana su, yana ba wa kowane mutum fassarar mafarkinsa.
And [there was] there with us a young man, a Hebrew, servant to the captain of the guard; and we told him, and he interpreted to us our dreams; to each man according to his dream he interpreted.
13 Abubuwan kuwa suka kasance daidai yadda ya fassara su gare mu; aka mai da ni a matsayina, ɗaya mutumin kuwa aka rataye shi.”
And it came to pass, as he interpreted to us, so it was: me he restored to my office, and him he hanged.
14 Sai Fir’auna ya aika a kawo Yusuf, aka kuwa kawo shi da sauri daga kurkuku. Sa’ad da ya yi aski, ya kuma canja tufafinsa, sai ya zo gaban Fir’auna.
Then Pharaoh sent and called Joseph, and they brought him hastily out of the dungeon: and he shaved [himself], and changed his raiment, and came before Pharaoh.
15 Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Na yi mafarki, kuma babu wanda ya iya fassara shi. Amma na ji an ce sa’ad da ka ji mafarki, kana iya fassara shi.”
And Pharaoh said to Joseph, I have dreamed a dream, and [there is] none that can interpret it: and I have heard it said of thee, [that] thou canst understand a dream to interpret it.
16 Yusuf ya amsa wa Fir’auna ya ce, “Ba ni ne da iyawar ba, Allah zai iya ba wa Fir’auna amsar da yake nema.”
And Joseph answered Pharaoh, saying, [It is] not in me: God will give Pharaoh an answer of peace.
17 Sa’an nan Fir’auna ya ce wa Yusuf, “A cikin mafarkina, na ga ina tsaye a bakin Nilu,
And Pharaoh said to Joseph, In my dream, behold, I stood upon the bank of the river:
18 sai ga shanu bakwai masu ƙiba mulmul, suka fito daga kogin, suna kiwo a cikin kyauro.
And behold, there came out of the river seven cows, fat-fleshed, and well-favored; and they fed in a meadow:
19 Bayansu kuma, sai ga waɗansu shanu bakwai suka fito ƙanjamammu, munana, ramammu. Ban taɓa ganin irin munanan shanu haka a cikin dukan ƙasar Masar ba.
And behold, seven other cows came out after them, poor, and very ill-favored, and lean-fleshed, such as I never saw in all the land of Egypt for badness:
20 Ramammun shanun nan munana, suka cinye shanun nan bakwai masu ƙiba da suka fito da fari.
And the lean and the ill-favored cows ate up the first seven fat cows:
21 Amma ko bayan da suka cinye su, babu wanda zai iya faɗa cewa sun yi haka; suna nan dai munana kamar yadda suke a dā. Sai na farka.
And when they had eaten them up, it could not be known that they had eaten them; but they [were] still ill-favored, as at the beginning. So I awoke.
22 “Har yanzu kuma, a cikin mafarkina na ga kawuna bakwai na dawa ƙosassu masu kyau, suna girma a kara guda.
And I saw in my dream, and behold, seven ears came up on one stalk, full and good:
23 Bayansu, sai ga waɗansu kawuna bakwai suka fito, yanƙwananne sirara waɗanda iskar gabas ta yanƙwane.
And behold, seven ears, withered, thin, [and] blasted with the east wind, sprung up after them:
24 Siraran kawunan dawan nan suka haɗiye kawuna bakwai nan masu kyau. Na faɗa wannan wa masu duba, amma ba wanda ya iya fassara mini shi.”
And the thin ears devoured the seven good ears: and I told [this] to the magicians; but [there was] none that could explain [it] to me.
25 Sai Yusuf ya ce wa Fir’auna, “Mafarkan Fir’auna, ɗaya ne. Allah ya bayyana wa Fir’auna abin da yake shirin yi.
And Joseph said to Pharaoh, The dream of Pharaoh [is] one; God hath showed Pharaoh what he [is] about to do.
26 Shanu masu kyau nan, shekaru bakwai ne, kawunan dawa bakwai ƙosassun nan kuwa shekaru bakwai ne; mafarkan iri ɗaya ne.
The seven good cows [are] seven years; and the seven good ears [are] seven years: the dream [is] one.
27 Shanun nan ramammu, munana, da suka zo daga baya, shekaru bakwai ne, haka ma kawuna dawan nan shanyayyu da iskar gabas ta yanƙwane. Shekaru ne bakwai na yunwa.
And the seven thin and ill-favored cows that came up after them [are] seven years; and the seven empty ears blasted with the east wind will be seven years of famine.
28 “Haka yake kamar yadda na faɗa wa Fir’auna cewa Allah ya nuna wa Fir’auna abin da yake shirin yi.
This [is] the thing which I have spoken to Pharaoh: What God [is] about to do he showeth to Pharaoh.
29 Shekaru bakwai na yalwar abinci suna zuwa a dukan ƙasar Masar,
Behold, there come seven years of great plenty throughout all the land of Egypt:
30 amma shekaru bakwai na yunwa za su biyo bayansu. Tsananin yunwar za tă sa a manta da dukan isashen abincin da aka samu a ƙasar Masar, yunwa kuwa za tă rufe dukan ƙasar.
And there shall arise after them seven years of famine; and all the plenty shall be forgotten in the land of Egypt; and the famine shall consume the land;
31 Ba za a tuna da isashen abincin da aka samu a ƙasar ba, domin yunwar da za tă biyo baya za tă zama da tsanani ƙwarai.
And the plenty shall not be known in the land by reason of the famine following: for it [will be] very grievous.
32 Dalilin da aka ba wa Fir’auna mafarkan nan kashi biyu kuwa shi ne cewa Allah ya riga ya ƙaddara al’amarin. Allah zai aikata shi, ba da daɗewa ba.
And for that the dream was doubled to Pharaoh twice; [it is] because the thing [is] established by God, and God will shortly bring it to pass.
33 “Yanzu fa, bari Fir’auna yă nemi mutum mai basira da kuma hikima, yă sa shi yă shugabanci ƙasar Masar.
Now therefore let Pharaoh look out a man discreet and wise, and set him over the land of Egypt.
34 Bari Fir’auna yă naɗa komishinoni a kan ƙasar don su karɓi kashi ɗaya bisa biyar na girbin Masar a lokacin shekaru bakwai na yalwar abinci.
Let Pharaoh do [this], and let him appoint officers over the land, and take up the fifth part of the land of Egypt in the seven plenteous years.
35 Ya kamata su tara dukan abincin waɗannan shekaru masu kyau da suke zuwa, su yi ajiyar hatsin a ƙarƙashin ikon Fir’auna, don a ajiye a birane don abinci.
And let them gather all the food of those good years that come, and lay up corn under the hand of Pharaoh; and let them keep food in the cities.
36 Ya kamata a adana abincin nan don ƙasar, kāriya shekaru bakwai na yunwa, domin a yi amfani da shi a lokacin shekarun yunwan da za su zo wa Masar, saboda kada ƙasar ta lalace da yunwa.”
And that food shall be for store to the land against the seven years of famine, which shall be in the land of Egypt; that the land may not perish through the famine.
37 Shirin ya yi wa Fir’auna da kuma dukan hafsoshinsa kyau.
And the thing was good in the eyes of Pharaoh, and in the eyes of all his servants.
38 Saboda haka Fir’auna ya tambaye su, “Za mu iya samun wani kamar wannan mutum, wannan wanda Ruhun Allah yake cikinsa?”
And Pharaoh said to his servants, Can we find [such a man] as this [is], a man in whom the spirit of God [is]?
39 Sai Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Da yake Allah ya ba ka sanin dukan waɗannan, babu wani mai basira da kuma hikima kamar ka.
And Pharaoh said to Joseph, Forasmuch as God hath shown thee all this, [there is] none so discreet and wise as thou [art]:
40 Za ka shugabanci fadata, kuma dukan mutanena za su zama a ƙarƙashinka. Da sarauta kaɗai zan fi ka girma.”
Thou shalt be over my house, and according to thy word shall all my people be ruled: only in the throne will I be greater than thou.
41 Saboda haka Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Ga shi na sa ka zama shugaban dukan ƙasar Masar.”
And Pharaoh said to Joseph, See, I have set thee over all the land of Egypt.
42 Sa’an nan Fir’auna ya zare zoben sarauta daga yatsarsa, ya sa shi a yatsan Yusuf. Ya sanya masa rigar lallausan lilin, ya kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa.
And Pharaoh took off his ring from his hand, and put it upon Joseph's hand, and arrayed him in vestures of fine linen, and put a gold chain about his neck;
43 Ya sa shi ya hau keken yaƙi a matsayi mai binsa na biyu, mutane kuwa suka yi shela a gabansa suna cewa, “A ba da hanya!” Ta haka ya sa shi shugaba a kan dukan ƙasar Masar.
And he made him to ride in the second chariot which he had: and they cried before him, Bow the knee: and he made him [ruler] over all the land of Egypt.
44 Sa’an nan Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Ni ne Fir’auna, amma in ba tare da umarninka ba, ba wanda zai ɗaga hannu ko ƙafa a cikin dukan Masar.”
And Pharaoh said to Joseph, I [am] Pharaoh, and without thee shall no man lift up his hand or foot in all the land of Egypt.
45 Fir’auna ya ba wa Yusuf suna Zafenat-Faneya, ya kuma ba shi Asenat’yar Fotifera firist na On, ta zama matarsa. Yusuf kuwa ya zaga dukan ƙasar Masar.
And Pharaoh called Joseph's name Zaphnath-paaneah; and he gave him for a wife Asenath the daughter of Poti-pherah priest of On: and Joseph went over [all] the land of Egypt.
46 Yusuf yana zuwa shekara talatin sa’ad da ya shiga hidimar Fir’auna sarkin Masar. Yusuf kuwa ya fita daga gaban Fir’auna, ya zaga ko’ina a Masar.
And Joseph [was] thirty years old when he stood before Pharaoh king of Egypt: and Joseph went out from the presence of Pharaoh, and went throughout all the land of Egypt.
47 A shekaru bakwai na yalwa, ƙasar ta ba da amfani mai yawa.
And in the seven plenteous years the earth brought forth by handfulls.
48 Yusuf ya tattara dukan abincin da aka samu a waɗannan shekaru bakwai na yalwa a Masar, ya kuma yi ajiyarsu a cikin birane. A kowane birni, ya sa abincin da aka nome a kewayensa.
And he gathered all the food of the seven years which were in the land of Egypt, and laid up the food in the cities: the food of the field which [was] around every city, he laid up in the same.
49 Sai Yusuf ya tara hatsi da yawan gaske, kamar yashi a bakin teku, har sai da ya kāsa iya auna shi, gama ba a iya aunawa.
And Joseph gathered corn as the sand of the sea, very much, until he left numbering; for [it was] without number.
50 Kafin shekarun yunwa su zo, Asenat’yar Fotifera, firist na On, ta haifa wa Yusuf’ya’ya maza biyu.
And to Joseph were born two sons before the years of famine came: which Asenath the daughter of Poti-pherah priest of On bore to him.
51 Yusuf ya ba wa ɗansa na fari suna Manasse ya ce, “Gama Allah ya sa na mance dukan wahalata da dukan gidan mahaifina.”
And Joseph called the name of the first-born Manasseh: For God, [said he], hath made me forget all my toil, and all my father's house.
52 Ya ba wa ɗansa na biyu suna Efraim ya ce, “Gama Allah ya wadata ni cikin wahalata.”
And the name of the second called he Ephraim: for God hath caused me to be fruitful in the land of my affliction.
53 Shekaru bakwai na yalwa a Masar suka zo ga ƙarshe,
And the seven years of plenteousness that was in the land of Egypt, were ended.
54 sai shekaru bakwai na yunwa suka soma shigowa, kamar yadda Yusuf ya faɗa. Aka yi yunwa ko’ina amma ban da ƙasar Masar. Don akwai abinci.
And the seven years of dearth began to come, according as Joseph had said: and the dearth was in all lands; but in all the land of Egypt there was bread.
55 Sa’ad da dukan Masar ta fara jin yunwa, sai mutane suka yi wa Fir’auna kuka don abinci. Sai Fir’auna ya ce wa dukan Masarawa, “Ku tafi wurin Yusuf, ku kuma yi abin da ya faɗa muku.”
And when all the land of Egypt was famished, the people cried to Pharaoh for bread: and Pharaoh said to all the Egyptians, Go to Joseph; what he saith to you, do.
56 Sa’ad da yunwa ta bazu a dukan ƙasar, sai Yusuf ya buɗe gidajen ajiya, ya kuma sayar da hatsi ga Masarawa, gama yunwa ta yi tsanani a dukan Masar.
And the famine was over all the face of the earth; and Joseph opened all the store-houses, and sold to the Egyptians; and the famine became severe in the land of Egypt.
57 Dukan ƙasashe kuwa suka zo Masar don saya hatsi daga Yusuf, gama yunwa ta yi tsanani a dukan duniya.
And all countries came into Egypt to Joseph to buy [corn]; because the famine was distressing in all lands.

< Farawa 41 >