< Farawa 41 >

1 Bayan shekaru biyu cif, Fir’auna ya yi mafarki. A mafarkin, ya ga yana tsaye kusa da Nilu,
Te phoeiah om tih kum a thok tue vaengah Pharaoh loh mang a man tih sokko taengah ana pai.
2 sai ga shanu bakwai masu ƙiba mulmul, suka fito daga kogin, suna kiwo a cikin kyauro.
Te vaengah vaito pumrhih, a mueimae sakthen neh a pum aka toitup te sokko lamkah lawt halo tih capu ding ah luem uh.
3 Bayansu, sai ga waɗansu shanu bakwai, munana, ramammu, suka fito daga Nilu, suka tsaya kusa da waɗancan masu ƙiban, a bakin kogin.
Amih hnukah a mueimae thae tih a pum aka cangkhawk vaito pumrhih te khaw sokko lamkah lawt ha thoeng bal tih sokko kaeng kah vaito kaepah pai uh.
4 Shanun nan da suke munana ramammu, suka cinye shanu bakwai nan masu ƙiba mulmul. Sai Fir’auna ya farka.
Tedae a mueimae thae tih a pum aka cangkhawk vaito pumrhih loh a mueimae sakthen neh aka toitup vaito te a caak uh, vaengah Pharaoh haenghang.
5 Ya sāke yin barci, sai ya yi mafarki na biyu; ya ga kawuna bakwai na dawa, ƙosassu masu kyau, suka yi girma a kara guda.
Te phoeiah ip tih a pabae la mang a man hatah cangvuei thamkom neh aka then parhih te a cangkong pakhat dongah tarha vuei.
6 Bayansu, sai ga waɗansu kawuna bakwai na dawa, suka fito sirara waɗanda iskar gabas ta sa suka yanƙwane.
Te phoeiah aka om cangvuei thamyit parhih te tah a hnukah kanghawn loh a yah tih a hum sak.
7 Siraran dawan suka haɗiye kawuna bakwai nan ƙosassu masu kyau. Sai Fir’auna ya farka, ashe, mafarki ne.
Tedae cangvuei thamyit parhih loh cangvuei thamkom neh cangtak te a yoop vaengah Pharaoh haenghang hatah a mang la pawk.
8 Da safe sai hankalinsa ya tashi, saboda haka sai ya aika a kawo dukan masu duba da masu hikima na Masar. Fir’auna ya faɗa musu mafarkansa, amma babu wanda ya iya ba shi fassararsu.
Te dongah mincang a pha vaengah tah a mueihla a cahoeh. Egypt hmayuep boeih neh aka cueih boeih te khaw a tah tih a khue. Tedae Pharaoh loh amih taengah a mang te a thui hatah Pharaoh ham aka thuicaih thai om pawh.
9 Sai shugaban masu shayarwa ya ce wa Fir’auna, “Yau an tuna mini da kāsawata.
Te daengah tuitul mangpa loh Pharaoh taengah, “Tihnin ah ni kamah tholh te ka poek.
10 Sai ya ci gaba ya ce, Fir’auna ya taɓa husata da bayinsa, ya kuma jefa ni da shugaban masu tuya a cikin kurkuku a gidan shugaban masu tsaro.
Pharaoh loh a sal rhoek taengah a thintoek tih kai neh buh thong mangpa te imtawt mangpa kah im thongim la n'khoh.
11 Kowannenmu ya yi mafarki a wani dare, kowane mafarki kuma ya kasance da ma’anarsa.
Tedae hlaem pakhat ah kai khaw anih khaw mang ka man rhoi hatah mang thuingaihnah te rhirha aka om te ka man rhoi.
12 To, wani saurayi, mutumin Ibraniyawa ya kasance a can tare da mu, bawan shugaban masu tsaro. Sai muka faɗa masa mafarkanmu, ya kuwa fassara mana su, yana ba wa kowane mutum fassarar mafarkinsa.
Te vaengah imtawt mangpa kah sal, Hebrew cadong te kaimih taengah om. Te dongah anih ham ka thui pah rhoi dongah kaimih rhoi kah mang te kaimih rhoi ham a thuicaih. Hlang kah a mang khaw a thuicaih.
13 Abubuwan kuwa suka kasance daidai yadda ya fassara su gare mu; aka mai da ni a matsayina, ɗaya mutumin kuwa aka rataye shi.”
Kaimih rhoi taengah a thuicaih vanbangla om tih a thoeng dongah kai he ka hmuen koep han khueh vaengah anih te a kuiok sak,” a ti nah tih a thui pah.
14 Sai Fir’auna ya aika a kawo Yusuf, aka kuwa kawo shi da sauri daga kurkuku. Sa’ad da ya yi aski, ya kuma canja tufafinsa, sai ya zo gaban Fir’auna.
Te dongah Pharaoh loh Joseph te a tah tih khue sak vanbangla anih te tangrhom khui lamkah koe a doek uh tih sam a vok, himbai a tho phoeiah Pharaoh taengla cet.
15 Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Na yi mafarki, kuma babu wanda ya iya fassara shi. Amma na ji an ce sa’ad da ka ji mafarki, kana iya fassara shi.”
Te vaengah Pharaoh loh Joseph la, “Mang ka man tih aka thuicaih a om pawt vaengah aka thuicaih ham nang loh mang na yakming a ti tih nang kawng te ka yaak,” a ti nah.
16 Yusuf ya amsa wa Fir’auna ya ce, “Ba ni ne da iyawar ba, Allah zai iya ba wa Fir’auna amsar da yake nema.”
Tedae Joseph loh Pharaoh te a doo tih, “Kai moenih, Pharaoh te Pathen loh ngaimongnah neh doo bitni,” a ti nah.
17 Sa’an nan Fir’auna ya ce wa Yusuf, “A cikin mafarkina, na ga ina tsaye a bakin Nilu,
Te dongah Pharaoh loh Joseph te, “Ka mang ah sokko kaeng la ka pai. dae,
18 sai ga shanu bakwai masu ƙiba mulmul, suka fito daga kogin, suna kiwo a cikin kyauro.
Tedae vaito a pumsa aka toitup tih a suisak sakthen pumrhih te sokko lamkah lawt halo tih capu ding ah luem uh.
19 Bayansu kuma, sai ga waɗansu shanu bakwai suka fito ƙanjamammu, munana, ramammu. Ban taɓa ganin irin munanan shanu haka a cikin dukan ƙasar Masar ba.
Amih hnukah vaito a tloe pumrhih halo bal dae tattloel la a suisak khaw bahoeng thae tih a pum pim. Tetla thaenah tah Egypt kho tom ah ka hmu pawh.
20 Ramammun shanun nan munana, suka cinye shanun nan bakwai masu ƙiba da suka fito da fari.
Te vaengah vaito aka pim neh a thae pumrhih loh lamhma kah vaito aka tha rhoek te a caak uh.
21 Amma ko bayan da suka cinye su, babu wanda zai iya faɗa cewa sun yi haka; suna nan dai munana kamar yadda suke a dā. Sai na farka.
Tedae amih ko khuila a kun uh thuk lalah a moecuek vaengkah bangla a mueimae a thae dongah amih ko khuila a kun uh te thui la a hut pawt vaengah ka haenghang.
22 “Har yanzu kuma, a cikin mafarkina na ga kawuna bakwai na dawa ƙosassu masu kyau, suna girma a kara guda.
Te phoeikah ka mang ah khaw cangvuei thamkom neh a then thamrhih te a cangkong pakhat dongah ha thoeng te lawt ka hmuh.
23 Bayansu, sai ga waɗansu kawuna bakwai suka fito, yanƙwananne sirara waɗanda iskar gabas ta yanƙwane.
Amih hnukkah cangvuei parih thamyit neh aka rhae, kanghawn loh a yah tih aka hum te tarha halo van.
24 Siraran kawunan dawan nan suka haɗiye kawuna bakwai nan masu kyau. Na faɗa wannan wa masu duba, amma ba wanda ya iya fassara mini shi.”
Te vaengah cangvuei aka yit rhoek loh cangvuei a then thamrhih te a dolh dongah hmayuep rhoek ham ka thui pah dae kai taengah aka puen om pawh,” a ti nah.
25 Sai Yusuf ya ce wa Fir’auna, “Mafarkan Fir’auna, ɗaya ne. Allah ya bayyana wa Fir’auna abin da yake shirin yi.
Te dongah Joseph loh Pharaoh la, “Pharaoh kah a mang he pakhat ni. Pathen loh a saii te Pharaoh taengah a phoe coeng.
26 Shanu masu kyau nan, shekaru bakwai ne, kawunan dawa bakwai ƙosassun nan kuwa shekaru bakwai ne; mafarkan iri ɗaya ne.
Vaito aka then pumrhih khaw kum rhih la om tih cangvuei a then parhih kum rih la om tih a mang te pakhat ni.
27 Shanun nan ramammu, munana, da suka zo daga baya, shekaru bakwai ne, haka ma kawuna dawan nan shanyayyu da iskar gabas ta yanƙwane. Shekaru ne bakwai na yunwa.
Amih hnukah aka thoeng vaito pumrhih aka pim tih aka thae te khaw kum rhih la om tih, cangvuei aka hi tih kanghawn loh a hum sak parhih te khokha kum rhih ni.
28 “Haka yake kamar yadda na faɗa wa Fir’auna cewa Allah ya nuna wa Fir’auna abin da yake shirin yi.
Pharaoh taengah kan thui vanbangla Pathen loh a saii hno he Pharaoh a tueng coeng.
29 Shekaru bakwai na yalwar abinci suna zuwa a dukan ƙasar Masar,
Aka lo ham kum rhih te Egypt kho tom ah khobuh khungdaeng ni te.
30 amma shekaru bakwai na yunwa za su biyo bayansu. Tsananin yunwar za tă sa a manta da dukan isashen abincin da aka samu a ƙasar Masar, yunwa kuwa za tă rufe dukan ƙasar.
Tedae a hnukah khokha kum rhih pai vetih Egypt kho kah khobuh te boeih a hnilh. Te vaengah khohmuen khaw khokha loh a khah ni.
31 Ba za a tuna da isashen abincin da aka samu a ƙasar ba, domin yunwar da za tă biyo baya za tă zama da tsanani ƙwarai.
Te dongah a hnuk lamtah khokha bahoeng nah tih khobuh te vang khui loh ming mahpawh.
32 Dalilin da aka ba wa Fir’auna mafarkan nan kashi biyu kuwa shi ne cewa Allah ya riga ya ƙaddara al’amarin. Allah zai aikata shi, ba da daɗewa ba.
Pharaoh taengah a pabalae la mang a rhaep he khaw Pathen taeng lamloh olka a cikngae sak dongah Pathen loh tlek a saii ni.
33 “Yanzu fa, bari Fir’auna yă nemi mutum mai basira da kuma hikima, yă sa shi yă shugabanci ƙasar Masar.
Te dongah Pharaoh loh, aka yakming tih aka cueih hlang te so lamtah anih te Egypt kho ah khueh laeh saeh.
34 Bari Fir’auna yă naɗa komishinoni a kan ƙasar don su karɓi kashi ɗaya bisa biyar na girbin Masar a lokacin shekaru bakwai na yalwar abinci.
Khohmuen ah hlangtawt rhoek te Pharaoh loh tuek saeh lamtah khobuh kum kumrhih khuiah Egypt kho kah panga pakhat aka coi la om saeh.
35 Ya kamata su tara dukan abincin waɗannan shekaru masu kyau da suke zuwa, su yi ajiyar hatsin a ƙarƙashin ikon Fir’auna, don a ajiye a birane don abinci.
Te daengah ni kum then a pai vaengkah caak boeih te a coi uh eh. Te phoeiah Pharaoh kut hmuiah cangpai a tung uh vetih khopuei ah caak khaw a cuem eh.
36 Ya kamata a adana abincin nan don ƙasar, kāriya shekaru bakwai na yunwa, domin a yi amfani da shi a lokacin shekarun yunwan da za su zo wa Masar, saboda kada ƙasar ta lalace da yunwa.”
Kho kah hnokhueh dongah caak a om daengah ni khokha loh Egypt khokhui la kum kumrhih a om halo vaengah khohmuen te khokha loh a tulnoi pawt eh?,” a ti nah.
37 Shirin ya yi wa Fir’auna da kuma dukan hafsoshinsa kyau.
Tekah olka ngawn tah Pharaoh mik neh a sal rhoek boeih kah mik ah a thuem sak.
38 Saboda haka Fir’auna ya tambaye su, “Za mu iya samun wani kamar wannan mutum, wannan wanda Ruhun Allah yake cikinsa?”
Te dongah Pharaoh loh a sal rhoek la, “Hekah hlang bangla a khuiah Pathen mueihla aka om te m'hmuh noek nim?,” a ti nah.
39 Sai Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Da yake Allah ya ba ka sanin dukan waɗannan, babu wani mai basira da kuma hikima kamar ka.
Te dongah Pharaoh loh Joseph la, “Hekah boeih he Pathen loh nang m'ming sak dongah nang bangla aka thuep neh aka cueih he om pawh.
40 Za ka shugabanci fadata, kuma dukan mutanena za su zama a ƙarƙashinka. Da sarauta kaɗai zan fi ka girma.”
Kai im ah nang om lamtah nang kah olpaek te ka pilnam boeih loh ngai saeh. Ka ngolkhoel bueng nen mah nang lakah ka ham mai eh,” a ti nah.
41 Saboda haka Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Ga shi na sa ka zama shugaban dukan ƙasar Masar.”
Te phoeiah Pharaoh loh Joseph la, “So lah, Egypt kho pum kah a soah nang ni kan hut sak coeng,” a ti nah.
42 Sa’an nan Fir’auna ya zare zoben sarauta daga yatsarsa, ya sa shi a yatsan Yusuf. Ya sanya masa rigar lallausan lilin, ya kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa.
Pharaoh loh a kut dongkah a kutcaeng te a dul tih Joseph kah kut ah a buen pah. Hnitang himbai neh a khuk phoeiah a rhawn ah sui oi a oi sak.
43 Ya sa shi ya hau keken yaƙi a matsayi mai binsa na biyu, mutane kuwa suka yi shela a gabansa suna cewa, “A ba da hanya!” Ta haka ya sa shi shugaba a kan dukan ƙasar Masar.
Leng dongah khaw a hnukthoi la a ngol sak tih, “Anih hmai ah cungkueng uh,” hlo a phoek uh tih Egypt kho boeih kah a soah Joseph te a khueh.
44 Sa’an nan Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Ni ne Fir’auna, amma in ba tare da umarninka ba, ba wanda zai ɗaga hannu ko ƙafa a cikin dukan Masar.”
Te phoeiah Pharaoh loh Joseph la, “Kai he Pharaoh coeng dae nang muehah hlang loh a kut khaw a kho khaw Egypt kho tom ah thueng boel saeh,” a ti nah.
45 Fir’auna ya ba wa Yusuf suna Zafenat-Faneya, ya kuma ba shi Asenat’yar Fotifera firist na On, ta zama matarsa. Yusuf kuwa ya zaga dukan ƙasar Masar.
Joseph ming khaw Pharaoh loh Zephenathpaneah la a khue tih a yuu la Oni khosoih Potiphera canu Asenath te a paek. Te phoeiah Joseph loh Egypt kho tom a hil.
46 Yusuf yana zuwa shekara talatin sa’ad da ya shiga hidimar Fir’auna sarkin Masar. Yusuf kuwa ya fita daga gaban Fir’auna, ya zaga ko’ina a Masar.
Egypt manghai Pharaoh taengla a kun vaengah Joseph te kum sawmthum lo ca pueng. Tedae Pharaoh mikhmuh lamloh Joseph nong tih Egypt kho tom boeih a hil.
47 A shekaru bakwai na yalwa, ƙasar ta ba da amfani mai yawa.
Te phoeiah khobuhnah kum rhih khuiah tah khohmuen te kutvang long khaw a thaih sak.
48 Yusuf ya tattara dukan abincin da aka samu a waɗannan shekaru bakwai na yalwa a Masar, ya kuma yi ajiyarsu a cikin birane. A kowane birni, ya sa abincin da aka nome a kewayensa.
Te dongah Egypt kho kah aka thoeng kho kum rhih kah caak boeih te a coi tih khopuei boeih ah caak a tung. Khopuei kaepvai kah khohmuen cang khaw a khui ah a khueh.
49 Sai Yusuf ya tara hatsi da yawan gaske, kamar yashi a bakin teku, har sai da ya kāsa iya auna shi, gama ba a iya aunawa.
Joseph loh cang a tung vaengah tuitunli kah laivin bangla muep a yet dongah a loeng tloel tih a tae ham khaw a toeng.
50 Kafin shekarun yunwa su zo, Asenat’yar Fotifera, firist na On, ta haifa wa Yusuf’ya’ya maza biyu.
Khokha kum halo hlanah Oni khosoih Potiphera canu Asenath loh ca a cun pah tih Joseph loh capa panit a sak.
51 Yusuf ya ba wa ɗansa na fari suna Manasse ya ce, “Gama Allah ya sa na mance dukan wahalata da dukan gidan mahaifina.”
Te vaengah Joseph loh, “Ka thakthaenah boeih neh a pa cako boeih te Pathen loh kai n'hnilh sak,” a ti dongah a caming te a ming Manasseh a sui.
52 Ya ba wa ɗansa na biyu suna Efraim ya ce, “Gama Allah ya wadata ni cikin wahalata.”
A ca pabae ming te khaw, “Kai kah phacip phabaem kho ah Pathen loh kai m'pungtai sak,” a ti dongah Ephraim a sui.
53 Shekaru bakwai na yalwa a Masar suka zo ga ƙarshe,
Tedae Egypt kho ah khobuh kum rhih aka om te bawt.
54 sai shekaru bakwai na yunwa suka soma shigowa, kamar yadda Yusuf ya faɗa. Aka yi yunwa ko’ina amma ban da ƙasar Masar. Don akwai abinci.
Joseph loh a thui vanbangla aka lo ham khokha kum rhih a tong dongah paeng tom ah khokha om coeng dae Egypt kho pum ah caak om pueng.
55 Sa’ad da dukan Masar ta fara jin yunwa, sai mutane suka yi wa Fir’auna kuka don abinci. Sai Fir’auna ya ce wa dukan Masarawa, “Ku tafi wurin Yusuf, ku kuma yi abin da ya faɗa muku.”
Tedae Egypt kho kho boeih loh a lamlum van vaengah tah pilnam loh caak ham ham te Pharaoh taengla pang uh. Te dongah Pharaoh loh Egypt rhoek boeih te, “Joseph taengla cet uh lamtah nangmih taengah a thui bangla saii uh,” a ti nah.
56 Sa’ad da yunwa ta bazu a dukan ƙasar, sai Yusuf ya buɗe gidajen ajiya, ya kuma sayar da hatsi ga Masarawa, gama yunwa ta yi tsanani a dukan Masar.
Khokha loh diklai hman boeih te a pha vaengah a kho khuikah aka om cangpai boeih te Joseph loh a hlah tih Egypt rhoek ham a yoih pah dongah Egypt kho kah khokha te a noeng.
57 Dukan ƙasashe kuwa suka zo Masar don saya hatsi daga Yusuf, gama yunwa ta yi tsanani a dukan duniya.
Paeng tom long khaw koivawn ham Egypt kah Joseph te a paan uh dongah paeng tom kah khokha khaw a talong.

< Farawa 41 >