< Farawa 40 >

1 Bayan ɗan lokaci, sai mai riƙon kwaf da mai tuyan sarkin Masar suka yi wa maigidansu, sarkin Masar laifi.
En tid härefter hände sig att den egyptiske konungens munskänk och hans bagare försyndade sig mot sin herre, konungen av Egypten.
2 Fir’auna ya yi fushi da hafsoshin nan nasa guda biyu, shugaban masu shayarwa da shugaban masu tuya,
Och Farao blev förtörnad på sina två hovmän, överste munskänken och överste bagaren,
3 ya kuma sa su a kurkuku a cikin gidan shugaban masu tsaro, a wannan kurkukun da aka sa Yusuf.
och lät sätta dem i förvar i drabanthövitsmannens hus, i samma fängelse där Josef satt fången.
4 Sai shugaban masu tsaro ya danƙa su a hannun Yusuf, ya kuwa yi musu hidima. Bayan sun jima cikin kurkuku,
Och hövitsmannen för drabanterna anställde Josef hos dem till att betjäna dem; och de sutto där i förvar en tid.
5 sai kowanne a cikin mutum biyun nan, mai riƙon kwaf da mai tuya na sarkin Masar, waɗanda aka sa a kurkuku, suka yi mafarki a dare ɗaya, kuma kowane mafarki ya kasance da fassara irin tasa.
Medan nu den egyptiske konungens munskänk och bagare sutto fångna i fängelset, hade de båda under samma natt var sin dröm, vardera med sin särskilda betydelse.
6 Sa’ad da Yusuf ya zo wurinsu kashegari, sai ya ga duk sun damu.
Och när Josef om morgonen kom in till dem, fick han se att de voro bedrövade.
7 Saboda haka ya tambayi hafsoshin Fir’auna, waɗanda suke a kurkuku tare da shi, a gidan maigidansa ya ce, “Me ya sa fuskokinku suke a ɓace haka?”
Då frågade han Faraos hovmän, som med honom sutto i förvar i hans herres hus: "Varför sen I så sorgsna ut i dag?"
8 Sai suka amsa, “Mu biyu, mun yi mafarki, amma babu wani da zai fassara mana su.” Sa’an nan Yusuf ya ce musu, “Fassara ba daga Allah take zuwa ba? Ku faɗa mini mafarkanku.”
De svarade honom: "Vi hava haft en dröm, och ingen finnes, som kan uttyda den." Josef sade till dem: "Att giva uttydningen är ju Guds sak; förtäljen drömmen för mig."
9 Sai shugaban masu shayarwa ya faɗa wa Yusuf mafarkinsa. Ya ce masa, “A cikin mafarkina, na ga kuringa a gabana,
Då förtäljde överste munskänken sin dröm för Josef och sade till honom: "Jag drömde att ett vinträd stod framför mig;
10 kuma a kuringar, akwai rassa uku. Nan da nan kuringar ta yi toho, ta huda, ta kuma yi nonna har suka nuna, suka zama inabi.
på vinträdet voro tre rankor, och knappt hade det skjutit skott, så slogo dess blommor ut och dess klasar buro mogna druvor.
11 Kwaf Fir’auna kuwa yana a hannuna, na kuma ɗiba inabin na matse su cikin kwaf Fir’auna, na kuma sa kwaf ɗin a hannunsa.”
Och jag hade Faraos bägare i min hand, och jag tog druvorna och pressade ut dem i Faraos bägare och gav Farao bägaren i handen."
12 Yusuf ya ce masa, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Rassan nan uku, kwana uku ne.
Då sade Josef till honom: "Detta är uttydningen: de tre rankorna betyda tre dagar;
13 Cikin kwana uku, Fir’auna zai fitar da kai, yă maido da kai a matsayinka, za ka kuwa sa kwaf Fir’auna cikin hannunsa, kamar yadda ka saba yi sa’ad da kake mai riƙon kwaf nasa.
om tre dagar skall Farao upphöja ditt huvud och sätta dig åter på din plats, så att du får giva Farao bägaren i handen likasom förut, då du var hans munskänk.
14 Amma fa, sa’ad da kome ya zama maka da kyau, ka tuna da ni, ka kuma yi mini alheri, ka ambace ni wa Fir’auna, ka fid da ni daga wannan kurkuku.
Men tänk på mig, när det går dig väl, så att du gör barmhärtighet med mig och nämner om mig för Farao och skaffar mig ut från detta hus;
15 Gama da ƙarfi ne aka ɗauke ni daga ƙasar Ibraniyawa, ko a nan ma ban yi wani abin da ya cancanci a sa ni cikin kurkuku ba.’”
ty jag är med orätt bortförd från hebréernas land, och icke heller här har jag gjort något varför jag borde sättas i fängelse."
16 Sa’ad da shugaban masu tuya ya ga cewa Yusuf ya ba da fassara mai gamsarwa, sai ya ce, wa Yusuf, “Ni ma na yi mafarki. A kaina, akwai kwanduna uku na burodi.
Då nu överste bagaren såg att Josef hade givit en god uttydning, sade han till honom: "Också jag hade en dröm. Jag tyckte att jag bar tre vetebrödskorgar på mitt huvud.
17 A kwandon na bisa, akwai kayan iri-iri da aka toya, masu kyau domin Fir’auna, amma tsuntsaye suka ci su a kwandon da yake kaina.”
Och i den översta korgen funnos bakverk av alla slag, sådant som Farao plägar äta; men fåglarna åto därav ur korgen på mitt huvud."
18 Yusuf ya ce, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Kwanduna uku, kwanaki uku ne.
Då svarade Josef och sade: "Detta är uttydningen: de tre korgarna betyda tre dagar;
19 Cikin kwana uku, Fir’auna zai fid da kai, yă rataye ka a kan itace. Tsuntsaye kuwa za su ci naman jikinka.’”
om tre dagar skall Farao upphöja ditt huvud och taga det av dig; han skall upphänga dig på trä, och fåglarna skola äta ditt kött."
20 To, a rana ta uku ne, ranar tunawa da haihuwar Fir’auna, ya kuwa yi biki wa dukan hafsoshinsa. Ya fid da shugaban masu shayarwa da kuma shugaban masu tuya a gaban hafsoshinsa.
På tredje dagen därefter, då det var Faraos födelsedag, gjorde denne ett gästabud för alla sina tjänare. Då upphöjde han, bland sina tjänare, såväl överste munskänkens huvud som överste bagarens.
21 Ya mai da shugaban masu shayarwa a matsayinsa, saboda haka shugaban masu shayarwa ya sāke sa kwaf a hannun Fir’auna,
Han insatte överste munskänken åter i hans ämbete, så att han fick giva Farao bägaren i handen;
22 amma ya rataye shugaban masu tuya, kamar dai yadda Yusuf ya faɗa musu a fassarar mafarkan da suka yi.
men överste bagaren lät han upphänga, såsom Josef hade sagt dem i sin uttydning.
23 Shugaban masu shayarwa fa, bai tuna da Yusuf ba; ya mance da shi.
Men överste munskänken tänkte icke på Josef, utan glömde honom.

< Farawa 40 >