< Farawa 40 >
1 Bayan ɗan lokaci, sai mai riƙon kwaf da mai tuyan sarkin Masar suka yi wa maigidansu, sarkin Masar laifi.
После тога догоди се, те пехарник цара мисирског и хлебар скривише господару свом, цару мисирском.
2 Fir’auna ya yi fushi da hafsoshin nan nasa guda biyu, shugaban masu shayarwa da shugaban masu tuya,
И Фараон се разгневи на та два дворанина, на старешину над пехарницима и на старешину над хлебарима;
3 ya kuma sa su a kurkuku a cikin gidan shugaban masu tsaro, a wannan kurkukun da aka sa Yusuf.
И баци их у тамницу у кући заповедника стражарског, где Јосиф беше сужањ.
4 Sai shugaban masu tsaro ya danƙa su a hannun Yusuf, ya kuwa yi musu hidima. Bayan sun jima cikin kurkuku,
А заповедник стражарски одреди им Јосифа да их служи; и беху дуго у тамници.
5 sai kowanne a cikin mutum biyun nan, mai riƙon kwaf da mai tuya na sarkin Masar, waɗanda aka sa a kurkuku, suka yi mafarki a dare ɗaya, kuma kowane mafarki ya kasance da fassara irin tasa.
И уснише сан обојица у једну ноћ, сваки по значењу свог сна за себе, и пехарник и хлебар цара мисирског, који беху сужњи у тамници.
6 Sa’ad da Yusuf ya zo wurinsu kashegari, sai ya ga duk sun damu.
И сутрадан кад дође Јосиф к њима, погледа их, а они беху врло невесели.
7 Saboda haka ya tambayi hafsoshin Fir’auna, waɗanda suke a kurkuku tare da shi, a gidan maigidansa ya ce, “Me ya sa fuskokinku suke a ɓace haka?”
Па запита дворане Фараонове, који беху сужњи с њим у кући господара његовог, и рече: Што сте данас лица невеселог?
8 Sai suka amsa, “Mu biyu, mun yi mafarki, amma babu wani da zai fassara mana su.” Sa’an nan Yusuf ya ce musu, “Fassara ba daga Allah take zuwa ba? Ku faɗa mini mafarkanku.”
А они му рекоше: Сан уснисмо обојица, а нема ко да нам каже шта значе. А Јосиф им рече: Шта значе, није ли у Бога? Али приповедите ми.
9 Sai shugaban masu shayarwa ya faɗa wa Yusuf mafarkinsa. Ya ce masa, “A cikin mafarkina, na ga kuringa a gabana,
И старешина над пехарницима приповеди сан свој Јосифу говорећи: Сних, а преда мном чокот;
10 kuma a kuringar, akwai rassa uku. Nan da nan kuringar ta yi toho, ta huda, ta kuma yi nonna har suka nuna, suka zama inabi.
И на чокоту беху три лозе, и напупи и процвате, и грожђе на њему узре;
11 Kwaf Fir’auna kuwa yana a hannuna, na kuma ɗiba inabin na matse su cikin kwaf Fir’auna, na kuma sa kwaf ɗin a hannunsa.”
А у руци ми беше чаша Фараонова, те побрах зрело грожђе и исцедих га у чашу Фараонову, и додадох чашу Фараону.
12 Yusuf ya ce masa, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Rassan nan uku, kwana uku ne.
А Јосиф му рече: Ово значи: три су лозе три дана.
13 Cikin kwana uku, Fir’auna zai fitar da kai, yă maido da kai a matsayinka, za ka kuwa sa kwaf Fir’auna cikin hannunsa, kamar yadda ka saba yi sa’ad da kake mai riƙon kwaf nasa.
Још три дана, и Фараон бројећи своје дворане узеће и тебе, и опет те поставити у пређашњу службу, и опет ћеш му додавати чашу као и пре док си му био пехарник.
14 Amma fa, sa’ad da kome ya zama maka da kyau, ka tuna da ni, ka kuma yi mini alheri, ka ambace ni wa Fir’auna, ka fid da ni daga wannan kurkuku.
Али немој заборавити мене кад будеш у добру, учини милост и помени за ме Фараону, и изведи ме из ове куће.
15 Gama da ƙarfi ne aka ɗauke ni daga ƙasar Ibraniyawa, ko a nan ma ban yi wani abin da ya cancanci a sa ni cikin kurkuku ba.’”
Јер су ме украли из земље јеврејске, а овде нисам ништа учинио да ме баце у ову јаму.
16 Sa’ad da shugaban masu tuya ya ga cewa Yusuf ya ba da fassara mai gamsarwa, sai ya ce, wa Yusuf, “Ni ma na yi mafarki. A kaina, akwai kwanduna uku na burodi.
А кад виде старешина над хлебарима како лепо каза сан, рече Јосифу: и ја сних, а мени на глави три котарице беле;
17 A kwandon na bisa, akwai kayan iri-iri da aka toya, masu kyau domin Fir’auna, amma tsuntsaye suka ci su a kwandon da yake kaina.”
И у најгорњој котарици беше свакојаких колача за Фараона, и птице јеђаху из котарице на мојој глави.
18 Yusuf ya ce, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Kwanduna uku, kwanaki uku ne.
А Јосиф одговори и рече: Ово значи: три котарице три су дана.
19 Cikin kwana uku, Fir’auna zai fid da kai, yă rataye ka a kan itace. Tsuntsaye kuwa za su ci naman jikinka.’”
Још три дана, и Фараон бројећи дворане своје избациће те и обесиће те на вешала, и птице ће јести с тебе месо.
20 To, a rana ta uku ne, ranar tunawa da haihuwar Fir’auna, ya kuwa yi biki wa dukan hafsoshinsa. Ya fid da shugaban masu shayarwa da kuma shugaban masu tuya a gaban hafsoshinsa.
И кад дође трећи дан, то беше дан у који се родио Фараон, и учини Фараон гозбу свим слугама својим, и наиђе међу слугама својим на старешину над пехарницима и на старешину над хлебарима;
21 Ya mai da shugaban masu shayarwa a matsayinsa, saboda haka shugaban masu shayarwa ya sāke sa kwaf a hannun Fir’auna,
И поврати старешину над пехарницима у службу да додаје чашу Фараону;
22 amma ya rataye shugaban masu tuya, kamar dai yadda Yusuf ya faɗa musu a fassarar mafarkan da suka yi.
А старешину над хлебарима обеси, као што каза Јосиф.
23 Shugaban masu shayarwa fa, bai tuna da Yusuf ba; ya mance da shi.
И старешина над пехарницима не опомену се Јосифа, него га заборави.