< Farawa 40 >

1 Bayan ɗan lokaci, sai mai riƙon kwaf da mai tuyan sarkin Masar suka yi wa maigidansu, sarkin Masar laifi.
Kwasekusithi emva kwalezizinto umphathinkezo wenkosi yeGibhithe lomphekizinkwa bona enkosini yabo, enkosini yeGibhithe.
2 Fir’auna ya yi fushi da hafsoshin nan nasa guda biyu, shugaban masu shayarwa da shugaban masu tuya,
Ngakho uFaro wabathukuthelela abathenwa bakhe ababili, induna yabaphathinkezo lenduna yabaphekizinkwa.
3 ya kuma sa su a kurkuku a cikin gidan shugaban masu tsaro, a wannan kurkukun da aka sa Yusuf.
Wazinikela esitokisini, endlini yenduna yabalindi, entolongweni, indawo lapho uJosefa ayebotshelwe khona.
4 Sai shugaban masu tsaro ya danƙa su a hannun Yusuf, ya kuwa yi musu hidima. Bayan sun jima cikin kurkuku,
Induna yabalindi yasimlaya uJosefa ukuba lazo, wazisebenzela; njalo zaba lensuku esitokisini.
5 sai kowanne a cikin mutum biyun nan, mai riƙon kwaf da mai tuya na sarkin Masar, waɗanda aka sa a kurkuku, suka yi mafarki a dare ɗaya, kuma kowane mafarki ya kasance da fassara irin tasa.
Zombili zaseziphupha amaphupho, ngamunye iphupho lakhe, ngabusuku bunye, ngamunye njengengcazelo yephupho lakhe, umphathinkezo lomphekizinkwa ababengabenkosi yeGibhithe ababebotshiwe entolongweni.
6 Sa’ad da Yusuf ya zo wurinsu kashegari, sai ya ga duk sun damu.
UJosefa wasengena kibo ekuseni, wababona, khangela-ke, benyukumele.
7 Saboda haka ya tambayi hafsoshin Fir’auna, waɗanda suke a kurkuku tare da shi, a gidan maigidansa ya ce, “Me ya sa fuskokinku suke a ɓace haka?”
Wasebabuza abathenwa bakaFaro ababelaye esitokisini endlini yenkosi yakhe, esithi: Kungani ubuso benu budanile lamuhla?
8 Sai suka amsa, “Mu biyu, mun yi mafarki, amma babu wani da zai fassara mana su.” Sa’an nan Yusuf ya ce musu, “Fassara ba daga Allah take zuwa ba? Ku faɗa mini mafarkanku.”
Basebesithi kuye: Siphuphile iphupho, njalo kakho umchasisi walo. UJosefa wasesithi kubo: Ingcazelo kayisizo zikaNkulunkulu yini? Ake lingilandisele wona.
9 Sai shugaban masu shayarwa ya faɗa wa Yusuf mafarkinsa. Ya ce masa, “A cikin mafarkina, na ga kuringa a gabana,
Induna yabaphathinkezo yalandisa iphupho layo kuJosefa, yathi kuye: Ephutsheni lami, khangela-ke, kwakukhona ivini phambi kwami;
10 kuma a kuringar, akwai rassa uku. Nan da nan kuringar ta yi toho, ta huda, ta kuma yi nonna har suka nuna, suka zama inabi.
evinini-ke kwakukhona ingatsha ezintathu; njalo kwakungathi liyahluma, impoko zalo zaphuma, amahlukuzo alo athela izithelo zevini ezivuthiweyo.
11 Kwaf Fir’auna kuwa yana a hannuna, na kuma ɗiba inabin na matse su cikin kwaf Fir’auna, na kuma sa kwaf ɗin a hannunsa.”
Njalo inkezo kaFaro yayisesandleni sami; ngasengithatha izithelo zevini, ngazikhamela enkezweni kaFaro, nganika inkezo esandleni sikaFaro.
12 Yusuf ya ce masa, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Rassan nan uku, kwana uku ne.
UJosefa wasesithi kuyo: Le yingcazelo yalo. Ingatsha ezintathu ziyizinsuku ezintathu;
13 Cikin kwana uku, Fir’auna zai fitar da kai, yă maido da kai a matsayinka, za ka kuwa sa kwaf Fir’auna cikin hannunsa, kamar yadda ka saba yi sa’ad da kake mai riƙon kwaf nasa.
kusesephakathi kwensuku ezintathu uFaro uzaphakamisa ikhanda lakho, akubuyisele esikhundleni sakho; njalo uzanika inkezo kaFaro esandleni sakhe, njengendlela yakuqala lapho wawungumphathinkezo wakhe.
14 Amma fa, sa’ad da kome ya zama maka da kyau, ka tuna da ni, ka kuma yi mini alheri, ka ambace ni wa Fir’auna, ka fid da ni daga wannan kurkuku.
Kodwa ungikhumbule lawe, lapho uhlezi kuhle, ake ungenzele umusa, ungibike kuFaro, ungikhuphe kulindlu.
15 Gama da ƙarfi ne aka ɗauke ni daga ƙasar Ibraniyawa, ko a nan ma ban yi wani abin da ya cancanci a sa ni cikin kurkuku ba.’”
Ngoba ngebiwa lokwebiwa elizweni lamaHebheru, lalapha futhi kangenzanga lutho ukuze bangifake emgodini.
16 Sa’ad da shugaban masu tuya ya ga cewa Yusuf ya ba da fassara mai gamsarwa, sai ya ce, wa Yusuf, “Ni ma na yi mafarki. A kaina, akwai kwanduna uku na burodi.
Lapho induna yabaphekizinkwa ibona ukuthi uchasise kuhle, yathi kuJosefa: Lami bengisephutsheni; khangela-ke, bekukhona izitsha ezintathu zilezinkwa ezimhlophe ekhanda lami;
17 A kwandon na bisa, akwai kayan iri-iri da aka toya, masu kyau domin Fir’auna, amma tsuntsaye suka ci su a kwandon da yake kaina.”
njalo esitsheni esingaphezulu kwakukhona okokudla konke kukaFaro, umsebenzi obhakiweyo; njalo inyoni zakudla lokho esitsheni esisekhanda lami.
18 Yusuf ya ce, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Kwanduna uku, kwanaki uku ne.
UJosefa wasephendula wathi: Le yingcazelo yalo. Izitsha ezintathu ziyizinsuku ezintathu;
19 Cikin kwana uku, Fir’auna zai fid da kai, yă rataye ka a kan itace. Tsuntsaye kuwa za su ci naman jikinka.’”
kusesephakathi kwensuku ezintathu uFaro uzaphakamisa ikhanda lakho lisuke kuwe, akulengise esihlahleni; inyoni zizakudla inyama yakho ziyisuse kuwe.
20 To, a rana ta uku ne, ranar tunawa da haihuwar Fir’auna, ya kuwa yi biki wa dukan hafsoshinsa. Ya fid da shugaban masu shayarwa da kuma shugaban masu tuya a gaban hafsoshinsa.
Kwasekusithi ngosuku lwesithathu, usuku lokuzalwa kukaFaro, wenzela inceku zakhe zonke idili; waphakamisa ikhanda lenduna yabaphathinkezo lekhanda lenduna yabaphekizinkwa phakathi kwenceku zakhe.
21 Ya mai da shugaban masu shayarwa a matsayinsa, saboda haka shugaban masu shayarwa ya sāke sa kwaf a hannun Fir’auna,
Wayibuyisela induna yabaphathinkezo ekuphatheni kwayo inkezo; yasinika inkezo esandleni sikaFaro.
22 amma ya rataye shugaban masu tuya, kamar dai yadda Yusuf ya faɗa musu a fassarar mafarkan da suka yi.
Kodwa wayilengisa induna yabaphekizinkwa, njengoba uJosefa ezichasisele.
23 Shugaban masu shayarwa fa, bai tuna da Yusuf ba; ya mance da shi.
Kodwa induna yabaphathinkezo kayimkhumbulanga uJosefa, kodwa yamkhohlwa.

< Farawa 40 >