< Farawa 40 >
1 Bayan ɗan lokaci, sai mai riƙon kwaf da mai tuyan sarkin Masar suka yi wa maigidansu, sarkin Masar laifi.
Bangʼ ndalo moko jagam divai kod jated makati mar Farao ruodh Misri nochwanyo ruoth.
2 Fir’auna ya yi fushi da hafsoshin nan nasa guda biyu, shugaban masu shayarwa da shugaban masu tuya,
Mirima nomako Farao gi jotichge ariyogo, ma gin jotend jagam divai kod jatend joma tedo makati.
3 ya kuma sa su a kurkuku a cikin gidan shugaban masu tsaro, a wannan kurkukun da aka sa Yusuf.
Kendo noketogi e od twech kama jatend askeche mar od twech notweyoe Josef.
4 Sai shugaban masu tsaro ya danƙa su a hannun Yusuf, ya kuwa yi musu hidima. Bayan sun jima cikin kurkuku,
Jatend askeche noketogi e lwet Josef mondo oritgi. Bangʼ kane gisebedo e od twech kuom kinde moko,
5 sai kowanne a cikin mutum biyun nan, mai riƙon kwaf da mai tuya na sarkin Masar, waɗanda aka sa a kurkuku, suka yi mafarki a dare ɗaya, kuma kowane mafarki ya kasance da fassara irin tasa.
moro ka moro kuom ji ariyogi mane gin jatend jogam divai kod jatend joted makati mar ruodh Misri mane oyudo otwe, noleko lek otienono moro ka moro, kendo lek ka lek ne nigi tiende mopogore gi machielo.
6 Sa’ad da Yusuf ya zo wurinsu kashegari, sai ya ga duk sun damu.
Kane Josef obiro irgi kinyne gokinyi, noneno ka chunygi ool.
7 Saboda haka ya tambayi hafsoshin Fir’auna, waɗanda suke a kurkuku tare da shi, a gidan maigidansa ya ce, “Me ya sa fuskokinku suke a ɓace haka?”
Kuom mano nopenjo jatich Farao mane ni kode e od twechgo niya, “Angʼo ma omiyo uol kawuono?”
8 Sai suka amsa, “Mu biyu, mun yi mafarki, amma babu wani da zai fassara mana su.” Sa’an nan Yusuf ya ce musu, “Fassara ba daga Allah take zuwa ba? Ku faɗa mini mafarkanku.”
Negidwoke niya, “Waduto nyoro waleko lek mopogore opogore, to onge ngʼama nyalo lokonwa tiendgi.” Eka Josef nowachonegi niya, “Donge fwenyo tiend lek aa mane kuom Nyasaye? Emomiyo yieuru unyisa lekugo.”
9 Sai shugaban masu shayarwa ya faɗa wa Yusuf mafarkinsa. Ya ce masa, “A cikin mafarkina, na ga kuringa a gabana,
Kuom mano jatend jogam Divai nonyiso Josef lek mane oleko. Nowachone niya, “E lekna nende aleko ni aneno yadh mzabibu e nyima,
10 kuma a kuringar, akwai rassa uku. Nan da nan kuringar ta yi toho, ta huda, ta kuma yi nonna har suka nuna, suka zama inabi.
kendo e yadh mzabibuno ne nitie bede adek. Kane ochako loth, nogolo thiepene kendo neginyago mzabibu mochiek mana gikanyono.
11 Kwaf Fir’auna kuwa yana a hannuna, na kuma ɗiba inabin na matse su cikin kwaf Fir’auna, na kuma sa kwaf ɗin a hannunsa.”
Kikombe Farao ne ni e lweta, kendo nakawo olembe mag mzabibu mi abiyogi e kikombe mar Farao kendo aketo kikombe e lwete.”
12 Yusuf ya ce masa, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Rassan nan uku, kwana uku ne.
Josef nowachone niya, “Ma e tiend lek mane ilekono. Bede yadh mzabibu adekgo nyiso ndalo adek.
13 Cikin kwana uku, Fir’auna zai fitar da kai, yă maido da kai a matsayinka, za ka kuwa sa kwaf Fir’auna cikin hannunsa, kamar yadda ka saba yi sa’ad da kake mai riƙon kwaf nasa.
Bangʼ ndalo adek Farao biro gonyi kendo dwoki e tiji, kendo ibiro keto kikombe Farao e lwete mana kaka yande kitimo kane in jatingʼ divai mare.
14 Amma fa, sa’ad da kome ya zama maka da kyau, ka tuna da ni, ka kuma yi mini alheri, ka ambace ni wa Fir’auna, ka fid da ni daga wannan kurkuku.
To ka gik moko duto otimoreni maber, ipara kendo itimna ngʼwono; iwuona gi Farao mondo ogola e od twech.
15 Gama da ƙarfi ne aka ɗauke ni daga ƙasar Ibraniyawa, ko a nan ma ban yi wani abin da ya cancanci a sa ni cikin kurkuku ba.’”
Nikech nomaka githuon ka igola e piny jo-Hibrania, kendo kata mana kaonge gima rach ma asetimo manyalo miyo abedie od twech ka.”
16 Sa’ad da shugaban masu tuya ya ga cewa Yusuf ya ba da fassara mai gamsarwa, sai ya ce, wa Yusuf, “Ni ma na yi mafarki. A kaina, akwai kwanduna uku na burodi.
Kane jatend joted makati oneno ni Josef oloko tiend lek maber, nowachone Josef niya, “An bende ne aleko kama: Atonge adek mag makati ne ni e wiya.
17 A kwandon na bisa, akwai kayan iri-iri da aka toya, masu kyau domin Fir’auna, amma tsuntsaye suka ci su a kwandon da yake kaina.”
Ei atonga mamalo ne nitie chiemo duto motedi ni Farao, to winy ne chamogi ei atonga mamalono.”
18 Yusuf ya ce, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Kwanduna uku, kwanaki uku ne.
Josef nowachone niya, “Ma e tiend leknino. Atonge adek nyiso ndalo adek.
19 Cikin kwana uku, Fir’auna zai fid da kai, yă rataye ka a kan itace. Tsuntsaye kuwa za su ci naman jikinka.’”
Kapok okadho ndalo adek Farao biro golie od twech, kendo obiro ngʼado wiyi oko manolieri e yath kendo winy biro chamo ringri.”
20 To, a rana ta uku ne, ranar tunawa da haihuwar Fir’auna, ya kuwa yi biki wa dukan hafsoshinsa. Ya fid da shugaban masu shayarwa da kuma shugaban masu tuya a gaban hafsoshinsa.
Koro odiechiengʼ mar adek ne en odiechieng rapar mar nywol Farao, kendo noloso nyasi ne jotije duto. Nogonyo jatend jogam divai kod jatend joted makati moketogi e nyim jodonge.
21 Ya mai da shugaban masu shayarwa a matsayinsa, saboda haka shugaban masu shayarwa ya sāke sa kwaf a hannun Fir’auna,
Nodwoko jatend jogam divai e tije, mondo omi ochak oket kikombe e lwet Farao,
22 amma ya rataye shugaban masu tuya, kamar dai yadda Yusuf ya faɗa musu a fassarar mafarkan da suka yi.
to jatend joted makati nonego, mana kaka Josef noselokonegi tiend lekgi.
23 Shugaban masu shayarwa fa, bai tuna da Yusuf ba; ya mance da shi.
To kata kamano jatend jogam divai ne ok oparo Josef; wiye nowil kode.