< Farawa 4 >
1 Adamu ya kwana da matarsa Hawwa’u, ta kuwa yi ciki ta haifi Kayinu. Sai ta ce, “Da taimakon Ubangiji na sami ɗa namiji.”
Och Adam kände sina hustru Heva, och hon aflade och födde Cain, och sade: Jag hafver fått Herrans man.
2 Daga baya ta haifi ɗan’uwansa, ta kuma ba shi suna Habila. Sa’ad da suka yi girma sai Habila ya zama makiyayin tumaki, Kayinu kuwa ya zama manomi.
Och hon födde framdeles Habel hans broder. Och vardt Habel en fåraherde, men Cain vardt en åkerman.
3 Ana nan sai Kayinu ya kawo waɗansu amfanin gona a matsayin hadaya ga Ubangiji.
Och det begaf sig efter några dagar, att Cain offrade Herranom gåfvor af jordenes frukt.
4 Amma Habila ya kawo mafi kyau daga’ya’yan fari na garkensa. Ubangiji ya yi farin ciki da sadakar da Habila ya kawo,
Och Habel offrade desslikes af förstlingene af sin får, och af deras talg: Och Herren såg täckeliga till Habel och hans offer.
5 amma bai yi farin ciki da sadakar da Kayinu ya kawo ba. Saboda haka Kayinu ya ji fushi sosai, fuskarsa kuma ta ɓace.
Men till Cain och hans offer såg han icke täckeliga. Då vardt Cain svårliga vred, och hans hy förvandlades.
6 Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Don me kake fushi? Don me fuskarka ta ɓace?
Sade Herren till Cain: Hvi äst du vred? Eller hvi förvandlas din hy?
7 Da ka yi abin da yake daidai, ai, da ka sami karɓuwa. Amma tun da ba ka yi abin da ba daidai ba, zunubi zai yi fakonka don yă rinjaye ka kamar naman jeji. Yana so yă mallake ka, amma tilas ka rinjaye shi.”
Är det icke så? Om du äst from, så äst du tacknämlig; men äst du icke from, så blifver icke synden säker eller fördold; men städ henne icke hennes vilja, utan råd öfver henne.
8 To, Kayinu ya ce wa ɗan’uwansa Habila, “Mu tafi gona.” Yayinda suke a gona, sai Kayinu ya tasar wa Habila ya buge shi ya kashe.
Då talade Cain med sin broder Habel. Och det begaf sig, då de voro på markene, gaf Cain sig upp emot sin broder Habel, och slog honom ihjäl.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Ina ɗan’uwanka Habila?” Sai Kayinu ya ce, “Ban sani ba, ni mai gadin ɗan’uwana ne?”
Då sade Herren till Cain: Hvar är din broder Habel? Han svarade: Jag vet det icke; skall jag taga vara på min broder?
10 Ubangiji ya ce, “Me ke nan ka yi? Saurara! Ga jinin ɗan’uwanka yana mini kuka daga ƙasa.
Och han sade till honom: Hvad hafver du gjort? Dins broders blods röst ropar till mig utaf jordene.
11 Yanzu, kai la’ananne ne, an kuma kore ka daga ƙasa wadda ta buɗe bakinta ta shanye jinin ɗan’uwanka daga hannunka.
Och nu, förbannad vare du på jordene, som sin mun öppnat hafver, och tagit dins broders blod utu dina händer.
12 In ka nome ƙasa, ba za tă ƙara ba ka hatsinta ba. Za ka kuma zama mai yawo barkatai a duniya.”
Då du brukar jordena, skall hon icke straxt gifva dig efter sin förmågo; ostadig och flyktig skall du blifva på jordene.
13 Kayinu ya ce wa Ubangiji, “Horon nan ya sha ƙarfina.
Och Cain sade till Herran: Min missgerning är större, än att hon må mig förlåten varda.
14 Ga shi, yau kana kori na daga ƙasar, zan zama a ɓoye daga fuskarka, zan kuma zama mai yawo barkatai, duk wanda ya same ni kuwa zai kashe ni.”
Si, du drifver mig i dag utaf landet, och jag måste gömma mig undan ditt ansigte, och måste ostadig och flyktig blifva på jordene. Så varder mig gående, att hvilken som helst mig finner, han slår mig ihjäl.
15 Amma Ubangiji ya ce masa, “Ba haka ba ne! Duk wanda ya kashe Kayinu, za a ninƙa hukuncinsa har sau bakwai.” Sa’an nan Ubangiji ya sa wa Kayinu alama don duk wanda ya same shi kada yă kashe shi.
Men Herren sade till honom: Nej, utan den som slår Cain ihjäl, det skall sjufalt hämnadt varda. Och Herren satte ett tecken på Cain, att hvilken som helst honom funne, skulle icke slå honom ihjäl.
16 Saboda haka Kayinu ya yi tafiyarsa ya rabu da Ubangiji, ya je ya zauna ƙasar Nod a gabashin Eden.
Och så gick Cain ifrå Herrans ansigte, och bodde i det landet Nod öster ut, på hinsidan Eden.
17 Kayinu ya kwana da matarsa, ta kuwa yi ciki, ta haifi Enok. A lokacin Kayinu yana gina birni, sai ya sa wa birnin sunan ɗansa Enok.
Och Cain kände sina hustru, och hon aflade och födde Hanoch, och han byggde en stad, hvilken han nämnde efter sin sons namn Hanoch.
18 Aka haifa wa Enok Irad, Irad kuma ya haifi Mehujayel, Mehujayel kuma ya haifi Metushayel, Metushayel kuma ya haifin Lamek.
Men Hanoch födde Yrad: Yrad födde Mahujael: Mahujael födde Methusael: Methusael födde Lamech.
19 Lamek ya auri mata biyu, ana ce da ɗaya Ada, ɗayan kuma Zilla.
Men Lamech tog sig två hustrur: Den ena het Ada, den andra Zilla.
20 Ada ta haifi Yabal, shi ne mahaifi waɗanda suke zama a tentuna, suna kuma kiwon dabbobi.
Och Ada födde Jabal; af honom kommo de som bodde under tjäll, och hade boskap.
21 Sunan ɗan’uwansa Yubal, shi ne mahaifin dukan makaɗan garaya da masu hura sarewa.
Och hans broder het Jubal, af honom kommo de, som brukade harpor och pipor.
22 Zilla ma ta haifi ɗa, Tubal-Kayinu, shi ne wanda ya ƙera kowane iri kayan aiki daga tagulla da kuma ƙarfe.’Yar’uwar Tubal-Kayinu ita ce Na’ama.
Födde ock desslikes Zilla, nemliga Tubalkain, som var en mästare i allahanda koppars och jerns verk; och Tubalkains syster var Naema.
23 Wata rana, Lamek ya ce wa matansa, Ada da Zilla, “Ku saurara, matan Lamek, ku ji maganata. Na kashe wani saboda ya yi mini rauni, na kashe wani saurayi saboda ya ji mini ciwo.
Och Lamech sade till sina hustrur Ada och Zilla: I Lamechs hustrur, hörer mina röst, och märker hvad jag säger: Jag hafver dräpit en man mig till sår, och en yngling mig till blånad.
24 Idan za a rama wa Kayinu har sau bakwai, lalle za a rama wa Lamek sau saba’in da bakwai ke nan.”
Cain skall varda hämnad sjufalt, men Lamech sju och sjutiofalt.
25 Sai Adamu ya sāke kwana da matarsa, ta haifi ɗa, aka kuma ba shi suna Set, gama ta ce, “Allah ya ba ni wani yaro a madadin Habila, tun da yake Kayinu ya kashe shi.”
Adam kände åter sina hustru, och hon födde en son, och kallade honom Seth, sägandes: Gud hafver satt mig en annor säd för Habel, som Cain ihjäl slog.
26 Set ma ya haifi ɗa, ya kuma kira shi Enosh. A lokaci ne, mutane suka fara kira ga sunan Ubangiji.
Vardt också Seth född en son, den han kallade Enos. Och på den samma tiden begynte man predika om Herrans namn.