< Farawa 4 >
1 Adamu ya kwana da matarsa Hawwa’u, ta kuwa yi ciki ta haifi Kayinu. Sai ta ce, “Da taimakon Ubangiji na sami ɗa namiji.”
Иза тога Адам позна Јеву жену своју, а она затрудне и роди Кајина, и рече: Добих човека од Господа.
2 Daga baya ta haifi ɗan’uwansa, ta kuma ba shi suna Habila. Sa’ad da suka yi girma sai Habila ya zama makiyayin tumaki, Kayinu kuwa ya zama manomi.
И роди опет брата његовог Авеља. И Авељ поста пастир а Кајин ратар.
3 Ana nan sai Kayinu ya kawo waɗansu amfanin gona a matsayin hadaya ga Ubangiji.
А после неког времена догоди се, те Кајин принесе Господу принос од рода земаљског;
4 Amma Habila ya kawo mafi kyau daga’ya’yan fari na garkensa. Ubangiji ya yi farin ciki da sadakar da Habila ya kawo,
А и Авељ принесе од првина стада свог и од њихове претилине. И Господ погледа на Авеља и на његов принос,
5 amma bai yi farin ciki da sadakar da Kayinu ya kawo ba. Saboda haka Kayinu ya ji fushi sosai, fuskarsa kuma ta ɓace.
А на Кајина и на његов принос не погледа. Зато се Кајин расрди веома, и лице му се промени.
6 Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Don me kake fushi? Don me fuskarka ta ɓace?
Тада рече Господ Кајину: Што се срдиш? Што ли ти се лице промени?
7 Da ka yi abin da yake daidai, ai, da ka sami karɓuwa. Amma tun da ba ka yi abin da ba daidai ba, zunubi zai yi fakonka don yă rinjaye ka kamar naman jeji. Yana so yă mallake ka, amma tilas ka rinjaye shi.”
Нећеш ли бити мио, кад добро чиниш? А кад не чиниш добро, грех је на вратима. А воља је његова под твојом влашћу, и ти си му старији.
8 To, Kayinu ya ce wa ɗan’uwansa Habila, “Mu tafi gona.” Yayinda suke a gona, sai Kayinu ya tasar wa Habila ya buge shi ya kashe.
После говораше Кајин с Авељем братом својим. Али кад беху у пољу, скочи Кајин на Авеља брата свог, и уби га.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Ina ɗan’uwanka Habila?” Sai Kayinu ya ce, “Ban sani ba, ni mai gadin ɗan’uwana ne?”
Тада рече Господ Кајину: Где ти је брат Авељ? А он одговори: Не знам; зар сам ја чувар брата свог?
10 Ubangiji ya ce, “Me ke nan ka yi? Saurara! Ga jinin ɗan’uwanka yana mini kuka daga ƙasa.
А Бог рече: Шта учини! Глас крви брата твог виче са земље к мени.
11 Yanzu, kai la’ananne ne, an kuma kore ka daga ƙasa wadda ta buɗe bakinta ta shanye jinin ɗan’uwanka daga hannunka.
И сада, да си проклет на земљи, која је отворила уста своја да прими крв брата твог из руке твоје.
12 In ka nome ƙasa, ba za tă ƙara ba ka hatsinta ba. Za ka kuma zama mai yawo barkatai a duniya.”
Кад земљу узрадиш, неће ти више давати блага свог. Бићеш потукач и бегунац на земљи.
13 Kayinu ya ce wa Ubangiji, “Horon nan ya sha ƙarfina.
А Кајин рече Господу: Кривица је моја велика да ми се не може опростити.
14 Ga shi, yau kana kori na daga ƙasar, zan zama a ɓoye daga fuskarka, zan kuma zama mai yawo barkatai, duk wanda ya same ni kuwa zai kashe ni.”
Ево ме тераш данас из ове земље да се кријем испред Тебе, и да се скитам и потуцам по земљи, па ће ме убити ко ме удеси.
15 Amma Ubangiji ya ce masa, “Ba haka ba ne! Duk wanda ya kashe Kayinu, za a ninƙa hukuncinsa har sau bakwai.” Sa’an nan Ubangiji ya sa wa Kayinu alama don duk wanda ya same shi kada yă kashe shi.
А Господ му рече: Зато ко убије Кајина, седам ће се пута то покајати. И начини Господ знак на Кајину да га не убије ко га удеси.
16 Saboda haka Kayinu ya yi tafiyarsa ya rabu da Ubangiji, ya je ya zauna ƙasar Nod a gabashin Eden.
И отиде Кајин испред Господа, и насели се у земљи наидској на истоку према Едему.
17 Kayinu ya kwana da matarsa, ta kuwa yi ciki, ta haifi Enok. A lokacin Kayinu yana gina birni, sai ya sa wa birnin sunan ɗansa Enok.
И позна Кајин жену своју, а она затрудне и роди Еноха. И сазида град и прозва га по имену сина свог Енох.
18 Aka haifa wa Enok Irad, Irad kuma ya haifi Mehujayel, Mehujayel kuma ya haifi Metushayel, Metushayel kuma ya haifin Lamek.
А Еноху роди се Гаидад; а Гаидад роди Малелеила: а Малелеило роди Матусала; а Матусал роди Ламеха.
19 Lamek ya auri mata biyu, ana ce da ɗaya Ada, ɗayan kuma Zilla.
И узе Ламех две жене: једној беше име Ада а другој Села.
20 Ada ta haifi Yabal, shi ne mahaifi waɗanda suke zama a tentuna, suna kuma kiwon dabbobi.
И Ада роди Јовила; од њега се народише који живе под шаторима и стоку пасу.
21 Sunan ɗan’uwansa Yubal, shi ne mahaifin dukan makaɗan garaya da masu hura sarewa.
А брату његовом беше име Јувал; од њега се народише гудачи и свирачи.
22 Zilla ma ta haifi ɗa, Tubal-Kayinu, shi ne wanda ya ƙera kowane iri kayan aiki daga tagulla da kuma ƙarfe.’Yar’uwar Tubal-Kayinu ita ce Na’ama.
А и Села роди Товела, који беше вешт ковати свашта од бронзе и од гвожђа; а сестра Товелу беше Ноема.
23 Wata rana, Lamek ya ce wa matansa, Ada da Zilla, “Ku saurara, matan Lamek, ku ji maganata. Na kashe wani saboda ya yi mini rauni, na kashe wani saurayi saboda ya ji mini ciwo.
И рече Ламех својим женама, Ади и Сели: Чујте глас мој, жене Ламехове, послушајте речи моје: убићу човека за рану своју и младића за масницу своју.
24 Idan za a rama wa Kayinu har sau bakwai, lalle za a rama wa Lamek sau saba’in da bakwai ke nan.”
Кад ће се Кајин осветити седам пута, Ламех ће седамдесет и седам пута.
25 Sai Adamu ya sāke kwana da matarsa, ta haifi ɗa, aka kuma ba shi suna Set, gama ta ce, “Allah ya ba ni wani yaro a madadin Habila, tun da yake Kayinu ya kashe shi.”
А Адам опет позна жену своју, и она роди сина, и наде му име Сит, јер ми, рече, Бог даде другог сина за Авеља, ког уби Кајин.
26 Set ma ya haifi ɗa, ya kuma kira shi Enosh. A lokaci ne, mutane suka fara kira ga sunan Ubangiji.
И Ситу се роди син, коме надеде име Енос. Тада се поче призивати име Господње.