< Farawa 4 >

1 Adamu ya kwana da matarsa Hawwa’u, ta kuwa yi ciki ta haifi Kayinu. Sai ta ce, “Da taimakon Ubangiji na sami ɗa namiji.”
Nandrèndreke i Haova, vali’e t’i Dame, le nivesatse naho nisamake i Kàine vaho nanao ty hoe: Nahazoako lahilahy t’Iehovà.
2 Daga baya ta haifi ɗan’uwansa, ta kuma ba shi suna Habila. Sa’ad da suka yi girma sai Habila ya zama makiyayin tumaki, Kayinu kuwa ya zama manomi.
Nisamake indraike re, le i Hèbele zai’e. Nimpihare añondry t’i Hèbele le nimpiava tane t’i Kàine.
3 Ana nan sai Kayinu ya kawo waɗansu amfanin gona a matsayin hadaya ga Ubangiji.
Ie te indraike, nibanabana ty lengom-boñe’ i taney am’ Iehovà t’i Kàine,
4 Amma Habila ya kawo mafi kyau daga’ya’yan fari na garkensa. Ubangiji ya yi farin ciki da sadakar da Habila ya kawo,
le ninday ty valohan’ ana’ o hare’eo naho ty sabora’e t’i Hèbele. Aa le nitoliha’ Iehovà t’i Hèbele naho i banabana’ey,
5 amma bai yi farin ciki da sadakar da Kayinu ya kawo ba. Saboda haka Kayinu ya ji fushi sosai, fuskarsa kuma ta ɓace.
fe tsy hinao’e t’i Kàine naho i enga’ey. Niforoforo ami’ty habose’e amy zao t’i Kàine vaho nilonjom-bintañe
6 Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Don me kake fushi? Don me fuskarka ta ɓace?
Inoñe ty iviñera’o hoe t’Iehovà amy Kàine vaho ino ty mahalonjets’ azo?
7 Da ka yi abin da yake daidai, ai, da ka sami karɓuwa. Amma tun da ba ka yi abin da ba daidai ba, zunubi zai yi fakonka don yă rinjaye ka kamar naman jeji. Yana so yă mallake ka, amma tilas ka rinjaye shi.”
Tsy hiampokòfañe hao irehe naho toloñe’o ty hiti’e? Aa naho tsy soa ty anoe’o le mangonònoke anjili-dalañe ao ty hakeo milelalela te hahazo azo, f’ie feheo.
8 To, Kayinu ya ce wa ɗan’uwansa Habila, “Mu tafi gona.” Yayinda suke a gona, sai Kayinu ya tasar wa Habila ya buge shi ya kashe.
Nifanaontsy amy Hèbele rahalahi’e t’i Kàine, aa ie nimb’an-teteke mb’ eo, niambotraha’ i Kàine t’i Hèbele naho nañohofa’e loza.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Ina ɗan’uwanka Habila?” Sai Kayinu ya ce, “Ban sani ba, ni mai gadin ɗan’uwana ne?”
Aa le hoe t’Iehovà amy Kàine, Aia t’i Hèbele rahalahi’o? Tsy fantako, hoe re, mpiambeñ’ an-drahalahiko hao iraho?
10 Ubangiji ya ce, “Me ke nan ka yi? Saurara! Ga jinin ɗan’uwanka yana mini kuka daga ƙasa.
Hoe re: Ino o nanoe’oo? Inao! mitoreo amako boak’ an-tane ao ty feon-dion-drahalahi’o;
11 Yanzu, kai la’ananne ne, an kuma kore ka daga ƙasa wadda ta buɗe bakinta ta shanye jinin ɗan’uwanka daga hannunka.
le fa nafà’ i taney irehe henane zao, ie nanoka-bava handrambe an-taña’o i lion-drahalahi’oy.
12 In ka nome ƙasa, ba za tă ƙara ba ka hatsinta ba. Za ka kuma zama mai yawo barkatai a duniya.”
Aa ie miava tane henane zao le tsy hafoe’e ama’o ty haozara’e; ie ho mpirererere naho mpitralantralañe an-tane atoy.
13 Kayinu ya ce wa Ubangiji, “Horon nan ya sha ƙarfina.
Hoe t’i Kàine am’ Iehovà, Tsy leoko babeñe o fandilovañe ahio;
14 Ga shi, yau kana kori na daga ƙasar, zan zama a ɓoye daga fuskarka, zan kuma zama mai yawo barkatai, duk wanda ya same ni kuwa zai kashe ni.”
anindroany irehe nanao soik’ ahy amo tarehe’ ty tane toio, naho hampietaheñe amy lahara’oy iraho, le ho mpiriorio naho mpirererere an-tane atoy, vaho songa hañoho-doza amako ze mifanojeha amako.
15 Amma Ubangiji ya ce masa, “Ba haka ba ne! Duk wanda ya kashe Kayinu, za a ninƙa hukuncinsa har sau bakwai.” Sa’an nan Ubangiji ya sa wa Kayinu alama don duk wanda ya same shi kada yă kashe shi.
Le hoe t’Iehovà ama’e, Aiy! ho valeñe im-pito ze mamono i Kàine; vaho namiloñe i Kàine t’i Andrianañahare tsy ho vonoe’ ze hifanalaka ama’e.
16 Saboda haka Kayinu ya yi tafiyarsa ya rabu da Ubangiji, ya je ya zauna ƙasar Nod a gabashin Eden.
Aa le nienga boak’ añatrefa’ Iehovà t’i Kàine, noly an-tane Rererere, atiñana’ i Edene añe.
17 Kayinu ya kwana da matarsa, ta kuwa yi ciki, ta haifi Enok. A lokacin Kayinu yana gina birni, sai ya sa wa birnin sunan ɗansa Enok.
Nifohi’ i Kàine ty vali’e, le niareñe, nisamake i Kanòke; ie nañoren-drova vaho nitokave’e ami’ty añara’ i Kanoke ana’e.
18 Aka haifa wa Enok Irad, Irad kuma ya haifi Mehujayel, Mehujayel kuma ya haifi Metushayel, Metushayel kuma ya haifin Lamek.
Nisamake Irade t’i Kanoke; le nisamak’ i Mehojaèle t’Irade le nisamak’ i Metosaele t’i Mehojaèle vaho nisamake i Lemeke t’i Metosaele.
19 Lamek ya auri mata biyu, ana ce da ɗaya Ada, ɗayan kuma Zilla.
Nampirafe roe t’i Lemeke; le natao ty hoe Adae ty raike naho i Zilae ty raike.
20 Ada ta haifi Yabal, shi ne mahaifi waɗanda suke zama a tentuna, suna kuma kiwon dabbobi.
Nisamake Iabale t’i Adae; ie ty raem-pimoneñe an-kibohotse naho mpihare.
21 Sunan ɗan’uwansa Yubal, shi ne mahaifin dukan makaɗan garaya da masu hura sarewa.
Natao Iobale ty rahalahi’e, ie ty rae’ o mpititike kararàke naho solio.
22 Zilla ma ta haifi ɗa, Tubal-Kayinu, shi ne wanda ya ƙera kowane iri kayan aiki daga tagulla da kuma ƙarfe.’Yar’uwar Tubal-Kayinu ita ce Na’ama.
Nisamake i Tobale-kaine t’i Zilae, ie ty nitsene ze hene haraotse torisìke naho viñe. I Naamae ty rahavave’ i Tobale-kaine.
23 Wata rana, Lamek ya ce wa matansa, Ada da Zilla, “Ku saurara, matan Lamek, ku ji maganata. Na kashe wani saboda ya yi mini rauni, na kashe wani saurayi saboda ya ji mini ciwo.
Hoe t’i Lemek’ amo vali’eo: Tsanoño ty feoko ry Adae naho Zilae; Ry vali’ i Lemekeo: mitsendreña o entakoo: Vinonoko t’indaty nandratse ahy, naho ty ajalahy nandafa ahiko.
24 Idan za a rama wa Kayinu har sau bakwai, lalle za a rama wa Lamek sau saba’in da bakwai ke nan.”
Aa naho i Kàine ro valeañe im-pito, Le toe impitompolo fito amby ka t’i Lemeke.
25 Sai Adamu ya sāke kwana da matarsa, ta haifi ɗa, aka kuma ba shi suna Set, gama ta ce, “Allah ya ba ni wani yaro a madadin Habila, tun da yake Kayinu ya kashe shi.”
Nifohi’ i Dame indraike i vali’ey, le nisamak’ ana-dahy vaho natao’e Sete ty añara’e, fa hoe i rakembay: Fa nanendre anake ho ahy t’i Andrianañahare handimbe i Hèbele vinono’ i Kàine.
26 Set ma ya haifi ɗa, ya kuma kira shi Enosh. A lokaci ne, mutane suka fara kira ga sunan Ubangiji.
Nahatoly anake ka t’i Sete, le natao’e Enose ty añara’e. Nifototse amy zay te nikanjy ty tahina’ Iehovà ondatio. izay ty takelam-piantoño’ i Dame.

< Farawa 4 >