< Farawa 4 >

1 Adamu ya kwana da matarsa Hawwa’u, ta kuwa yi ciki ta haifi Kayinu. Sai ta ce, “Da taimakon Ubangiji na sami ɗa namiji.”
Un Ādams atzina Ievu, savu sievu, un tā tapa grūta un dzemdēja Kainu un sacīja: es esmu dabūjusi vīru ar To Kungu.
2 Daga baya ta haifi ɗan’uwansa, ta kuma ba shi suna Habila. Sa’ad da suka yi girma sai Habila ya zama makiyayin tumaki, Kayinu kuwa ya zama manomi.
Un tā vēl dzemdēja viņa brāli, Ābelu; un Ābels palika par avju ganu, bet Kains palika par zemes kopēju.
3 Ana nan sai Kayinu ya kawo waɗansu amfanin gona a matsayin hadaya ga Ubangiji.
Un notikās pēc kāda laika, ka Kains Tam Kungam upuri nesa no zemes augļiem.
4 Amma Habila ya kawo mafi kyau daga’ya’yan fari na garkensa. Ubangiji ya yi farin ciki da sadakar da Habila ya kawo,
Un Ābels arīdzan nesa no savu avju pirmdzimtiem un no viņu taukiem. Un Tas Kungs uzlūkoja Ābelu un viņa upuri.
5 amma bai yi farin ciki da sadakar da Kayinu ya kawo ba. Saboda haka Kayinu ya ji fushi sosai, fuskarsa kuma ta ɓace.
Bet Kainu un viņa upuri Viņš neuzlūkoja. Tad iedegās Kaina bardzība, un viņa vaigs raudzījās nikni.
6 Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Don me kake fushi? Don me fuskarka ta ɓace?
Un Tas Kungs sacīja uz Kainu: kam tu esi apskaities, un kādēļ tavs vaigs raugās nikni?
7 Da ka yi abin da yake daidai, ai, da ka sami karɓuwa. Amma tun da ba ka yi abin da ba daidai ba, zunubi zai yi fakonka don yă rinjaye ka kamar naman jeji. Yana so yă mallake ka, amma tilas ka rinjaye shi.”
Vai nav tā: ja tu darīsi pareizi, tad vari savu vaigu pacelt; bet ja tu darīsi nepareizi, tad grēks guļ priekš durvīm un tīko pēc tevis, - bet tu, valdi pār viņu. Un Kains runāja ar savu brāli Ābelu.
8 To, Kayinu ya ce wa ɗan’uwansa Habila, “Mu tafi gona.” Yayinda suke a gona, sai Kayinu ya tasar wa Habila ya buge shi ya kashe.
Un notikās, kad tie bija laukā, tad Kains cēlās pret Ābelu, savu brāli, un to nokāva.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Ina ɗan’uwanka Habila?” Sai Kayinu ya ce, “Ban sani ba, ni mai gadin ɗan’uwana ne?”
Un Tas Kungs sacīja uz Kainu: kur ir Ābels, tavs brālis? Un tas sacīja: es nezinu. Vai tad es sava brāļa sargs?
10 Ubangiji ya ce, “Me ke nan ka yi? Saurara! Ga jinin ɗan’uwanka yana mini kuka daga ƙasa.
Un Viņš sacīja: ko tu esi darījis? Tava brāļa asiņu balss brēc uz Mani no zemes.
11 Yanzu, kai la’ananne ne, an kuma kore ka daga ƙasa wadda ta buɗe bakinta ta shanye jinin ɗan’uwanka daga hannunka.
Un nu esi nolādēts, nost no zemes, kas savu muti atpletusi, tava brāļa asinis saņemt no tavām rokām.
12 In ka nome ƙasa, ba za tă ƙara ba ka hatsinta ba. Za ka kuma zama mai yawo barkatai a duniya.”
Kad tu zemi strādāsi, tad tā vairs tev nedos savu spēku; tekulis un bēglis tu būsi virs zemes.
13 Kayinu ya ce wa Ubangiji, “Horon nan ya sha ƙarfina.
Un Kains sacīja uz To Kungu: mans noziegums ir lielāks, nekā to varētu panest.
14 Ga shi, yau kana kori na daga ƙasar, zan zama a ɓoye daga fuskarka, zan kuma zama mai yawo barkatai, duk wanda ya same ni kuwa zai kashe ni.”
Redzi, Tu mani šodien izdzen no zemes, un man būs paslēpties no Tava vaiga un es būšu tekulis un bēglis virs zemes, un notiks, ka ikviens, kas mani atrod, tas mani nokaus.
15 Amma Ubangiji ya ce masa, “Ba haka ba ne! Duk wanda ya kashe Kayinu, za a ninƙa hukuncinsa har sau bakwai.” Sa’an nan Ubangiji ya sa wa Kayinu alama don duk wanda ya same shi kada yă kashe shi.
Un Tas Kungs uz to sacīja: tādēļ, kas Kainu nokauj, tas taps septiņkārt atriebts. Un Tas Kungs pielika Kainam zīmi, lai to nenokautu, kas to atrastu.
16 Saboda haka Kayinu ya yi tafiyarsa ya rabu da Ubangiji, ya je ya zauna ƙasar Nod a gabashin Eden.
Un Kains aizgāja no Tā Kunga vaiga un mita Nodzemē, Ēdenei pret rītiem.
17 Kayinu ya kwana da matarsa, ta kuwa yi ciki, ta haifi Enok. A lokacin Kayinu yana gina birni, sai ya sa wa birnin sunan ɗansa Enok.
Un Kains atzina savu sievu, un tā tapa grūta un dzemdēja Ēnohu; un viņš uztaisīja pilsētu un nosauca tās pilsētas vārdu pēc sava dēla vārda Ēnohu.
18 Aka haifa wa Enok Irad, Irad kuma ya haifi Mehujayel, Mehujayel kuma ya haifi Metushayel, Metushayel kuma ya haifin Lamek.
Un Ēnoham dzima Īrads, un Īrads dzemdināja Meūjaēlu, un Meūjaēls dzemdināja Metusaēlu, un Metusaēls dzemdināja Lāmehu.
19 Lamek ya auri mata biyu, ana ce da ɗaya Ada, ɗayan kuma Zilla.
Un Lāmehs apņēma divas sievas; pirmai bija vārds Ada, un otrai bija vārds Cilla.
20 Ada ta haifi Yabal, shi ne mahaifi waɗanda suke zama a tentuna, suna kuma kiwon dabbobi.
Un Ada dzemdēja Jabalu; tas ir tēvs bijis tiem, kas teltīs dzīvoja un lopus audzināja.
21 Sunan ɗan’uwansa Yubal, shi ne mahaifin dukan makaɗan garaya da masu hura sarewa.
Un viņa brāļa vārds bija Jubals; tas ir tēvs bijis visiem koklētājiem un stabulniekiem.
22 Zilla ma ta haifi ɗa, Tubal-Kayinu, shi ne wanda ya ƙera kowane iri kayan aiki daga tagulla da kuma ƙarfe.’Yar’uwar Tubal-Kayinu ita ce Na’ama.
Un Cilla arīdzan dzemdēja Tubalkaīnu, kas bija visādu vara un dzelzs rīku kalējs. Un Tubalkaīna māsa bija Naēma.
23 Wata rana, Lamek ya ce wa matansa, Ada da Zilla, “Ku saurara, matan Lamek, ku ji maganata. Na kashe wani saboda ya yi mini rauni, na kashe wani saurayi saboda ya ji mini ciwo.
Un Lāmehs sacīja uz savām sievām: Ada un Cilla, klausiet manu balsi, jūs Lāmeha sievas, ņemiet vērā manus vārdus! Jo es vīru nokauju par savu vāti un jaunekli par savu brūci.
24 Idan za a rama wa Kayinu har sau bakwai, lalle za a rama wa Lamek sau saba’in da bakwai ke nan.”
Jo Kains taps septiņkārt atriebts, bet Lāmehs septiņdesmit septiņkārt.
25 Sai Adamu ya sāke kwana da matarsa, ta haifi ɗa, aka kuma ba shi suna Set, gama ta ce, “Allah ya ba ni wani yaro a madadin Habila, tun da yake Kayinu ya kashe shi.”
Un Ādams atzina atkal savu sievu, un tā dzemdēja dēlu un nosauca viņa vārdu Setu; jo (tā sacīja: ) Dievs man ir licis citu dzimumu Ābela vietā, jo Kains to ir nokāvis.
26 Set ma ya haifi ɗa, ya kuma kira shi Enosh. A lokaci ne, mutane suka fara kira ga sunan Ubangiji.
Un Setam arī dzima dēls, un tas nosauca viņa vārdu Enosu. Tai laikā iesāka piesaukt Tā Kunga vārdu.

< Farawa 4 >