< Farawa 4 >

1 Adamu ya kwana da matarsa Hawwa’u, ta kuwa yi ciki ta haifi Kayinu. Sai ta ce, “Da taimakon Ubangiji na sami ɗa namiji.”
Adam pak poznal Evu ženu svou, kterážto počavši, porodila Kaina a řekla: Obdržela jsem muže na Hospodinu.
2 Daga baya ta haifi ɗan’uwansa, ta kuma ba shi suna Habila. Sa’ad da suka yi girma sai Habila ya zama makiyayin tumaki, Kayinu kuwa ya zama manomi.
A opět porodila bratra jeho Abele. I byl Abel pastýř ovcí, a Kain byl oráč.
3 Ana nan sai Kayinu ya kawo waɗansu amfanin gona a matsayin hadaya ga Ubangiji.
Po mnohých pak dnech stalo se, že obětoval Kain z úrody zemské obět Hospodinu.
4 Amma Habila ya kawo mafi kyau daga’ya’yan fari na garkensa. Ubangiji ya yi farin ciki da sadakar da Habila ya kawo,
Ano i Abel také obětoval z prvorozených věcí stáda svého, a z tuku jejich. I vzhlédl Hospodin na Abele a na obět jeho.
5 amma bai yi farin ciki da sadakar da Kayinu ya kawo ba. Saboda haka Kayinu ya ji fushi sosai, fuskarsa kuma ta ɓace.
Na Kaina pak a na obět jeho nevzhlédl. Protož rozlítil se Kain náramně, a opadla tvář jeho.
6 Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Don me kake fushi? Don me fuskarka ta ɓace?
I řekl Hospodin Kainovi: Proč jsi se tak rozpálil hněvem? A proč jest opadla tvář tvá?
7 Da ka yi abin da yake daidai, ai, da ka sami karɓuwa. Amma tun da ba ka yi abin da ba daidai ba, zunubi zai yi fakonka don yă rinjaye ka kamar naman jeji. Yana so yă mallake ka, amma tilas ka rinjaye shi.”
Zdaliž nebudeš příjemný, budeš-li dobře činiti? Pakli nebudeš dobře činiti, hřích ve dveřích leží; a pod mocí tvou bude žádost jeho, a ty panovati budeš nad ním.
8 To, Kayinu ya ce wa ɗan’uwansa Habila, “Mu tafi gona.” Yayinda suke a gona, sai Kayinu ya tasar wa Habila ya buge shi ya kashe.
I mluvil Kain k Abelovi bratru svému. Stalo se pak, když byli na poli, že povstav Kain proti Abelovi bratru svému, zabil jej.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Ina ɗan’uwanka Habila?” Sai Kayinu ya ce, “Ban sani ba, ni mai gadin ɗan’uwana ne?”
I řekl Hospodin Kainovi: Kdež jest Abel bratr tvůj? Kterýž odpověděl: Nevím. Zdaliž jsem já strážným bratra svého?
10 Ubangiji ya ce, “Me ke nan ka yi? Saurara! Ga jinin ɗan’uwanka yana mini kuka daga ƙasa.
I řekl Bůh: Co jsi učinil? Hlas krve bratra tvého volá ke mně z země.
11 Yanzu, kai la’ananne ne, an kuma kore ka daga ƙasa wadda ta buɗe bakinta ta shanye jinin ɗan’uwanka daga hannunka.
Protož nyní zlořečený budeš i od té země, kteráž otevřela ústa svá, aby přijala krev bratra tvého z ruky tvé.
12 In ka nome ƙasa, ba za tă ƙara ba ka hatsinta ba. Za ka kuma zama mai yawo barkatai a duniya.”
Když budeš dělati zemi, nebude více vydávati moci své tobě; tulákem a běhounem budeš na zemi.
13 Kayinu ya ce wa Ubangiji, “Horon nan ya sha ƙarfina.
I řekl Kain Hospodinu: Většíť jest nepravost má, než aby mi odpuštěna býti mohla.
14 Ga shi, yau kana kori na daga ƙasar, zan zama a ɓoye daga fuskarka, zan kuma zama mai yawo barkatai, duk wanda ya same ni kuwa zai kashe ni.”
Aj, vyháníš mne dnes z země této, a před tváří tvou skrývati se budu, a budu tulákem a běhounem na zemi. I přijde na to, že kdo mne koli nalezne, zabije mne.
15 Amma Ubangiji ya ce masa, “Ba haka ba ne! Duk wanda ya kashe Kayinu, za a ninƙa hukuncinsa har sau bakwai.” Sa’an nan Ubangiji ya sa wa Kayinu alama don duk wanda ya same shi kada yă kashe shi.
I řekl mu Hospodin: Zajisté kdo by koli zabil Kaina, nad tím sedmnásobně mštěno bude. Pročež vložil Hospodin znamení naKaina, aby ho žádný nezabil, kdo by jej koli nalezl.
16 Saboda haka Kayinu ya yi tafiyarsa ya rabu da Ubangiji, ya je ya zauna ƙasar Nod a gabashin Eden.
Tedy odšed Kain od tváři Hospodinovy, bydlil v zemi Nód, k východní straně naproti Eden.
17 Kayinu ya kwana da matarsa, ta kuwa yi ciki, ta haifi Enok. A lokacin Kayinu yana gina birni, sai ya sa wa birnin sunan ɗansa Enok.
Poznal pak Kain ženu svou, kterážto počala a porodila Enocha. I stavěl město, a nazval jméno města toho jménem syna svého Enoch.
18 Aka haifa wa Enok Irad, Irad kuma ya haifi Mehujayel, Mehujayel kuma ya haifi Metushayel, Metushayel kuma ya haifin Lamek.
I narodil se Enochovi Irád, a Irád zplodil Maviaele, Maviael pak zplodil Matuzaele, a Matuzael zplodil Lámecha.
19 Lamek ya auri mata biyu, ana ce da ɗaya Ada, ɗayan kuma Zilla.
Vzal sobě pak Lámech dvě ženy; jméno jedné Ada, a jméno druhé Zilla.
20 Ada ta haifi Yabal, shi ne mahaifi waɗanda suke zama a tentuna, suna kuma kiwon dabbobi.
I porodila Ada Jábale, kterýž byl otec přebývajících v staních a stádo pasoucích.
21 Sunan ɗan’uwansa Yubal, shi ne mahaifin dukan makaɗan garaya da masu hura sarewa.
A jméno bratra jeho Jubal; ten byl otec všech hrajících na harfu a nástroje hudebné.
22 Zilla ma ta haifi ɗa, Tubal-Kayinu, shi ne wanda ya ƙera kowane iri kayan aiki daga tagulla da kuma ƙarfe.’Yar’uwar Tubal-Kayinu ita ce Na’ama.
A Zilla také porodila Tubalkaina, kterýž byl řemeslník všelikého díla od mědi a od železa. Sestra pak Tubalkainova byla Noéma.
23 Wata rana, Lamek ya ce wa matansa, Ada da Zilla, “Ku saurara, matan Lamek, ku ji maganata. Na kashe wani saboda ya yi mini rauni, na kashe wani saurayi saboda ya ji mini ciwo.
I řekl Lámech ženám svým, Adě a Zille: Slyšte hlas můj, ženy Lámechovy, poslouchejte řeči mé, že jsem zabil muže k ráně své a mládence k zsinalosti své.
24 Idan za a rama wa Kayinu har sau bakwai, lalle za a rama wa Lamek sau saba’in da bakwai ke nan.”
Jestližeť sedmnásobně pomštěno bude pro Kaina, tedy pro Lámecha sedmdesátekrát sedmkrát.
25 Sai Adamu ya sāke kwana da matarsa, ta haifi ɗa, aka kuma ba shi suna Set, gama ta ce, “Allah ya ba ni wani yaro a madadin Habila, tun da yake Kayinu ya kashe shi.”
Poznal pak ještě Adam ženu svou, i porodila syna a nazvala jméno jeho Set; nebo řekla: Dal mi Bůh jiné símě místo Abele, kteréhož zabil Kain.
26 Set ma ya haifi ɗa, ya kuma kira shi Enosh. A lokaci ne, mutane suka fara kira ga sunan Ubangiji.
Setovi pak také narodil se syn, a nazval jméno jeho Enos. Tehdáž začalo se vzývání jména Hospodinova.

< Farawa 4 >