< Farawa 4 >
1 Adamu ya kwana da matarsa Hawwa’u, ta kuwa yi ciki ta haifi Kayinu. Sai ta ce, “Da taimakon Ubangiji na sami ɗa namiji.”
Adam ni a yu Evi a panue teh, camo a vawn. Capa a khe teh, BAWIPA ni na kabawp dawk ca tongpa ka khe ati teh, Kain telah min a phung.
2 Daga baya ta haifi ɗan’uwansa, ta kuma ba shi suna Habila. Sa’ad da suka yi girma sai Habila ya zama makiyayin tumaki, Kayinu kuwa ya zama manomi.
Hahoi, a nawngha Abel bout a khe. Abel teh tu kakhoumkung lah ao teh, Kain teh law kasakkung lah ao.
3 Ana nan sai Kayinu ya kawo waɗansu amfanin gona a matsayin hadaya ga Ubangiji.
Atueng akuep torei teh, Kain ni amae law thung e a pawhiknaw hah BAWIPA koe a sin.
4 Amma Habila ya kawo mafi kyau daga’ya’yan fari na garkensa. Ubangiji ya yi farin ciki da sadakar da Habila ya kawo,
Abel ni hai tu pasuek ka khe e hoi, kathâwnaw a sin. Hatdawkvah, BAWIPA ni Abel hoi a sin e hno teh a dâw pouh.
5 amma bai yi farin ciki da sadakar da Kayinu ya kawo ba. Saboda haka Kayinu ya ji fushi sosai, fuskarsa kuma ta ɓace.
Hatei Kain hoi a sin e hno teh dâw pouh hoeh. Hatdawkvah, Kain teh a lung puenghoi a khuek dawkvah minhmai a mathoe.
6 Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Don me kake fushi? Don me fuskarka ta ɓace?
BAWIPA ni Kain koevah, Bangkongmaw na lungkhuek teh minhmai a mathoe.
7 Da ka yi abin da yake daidai, ai, da ka sami karɓuwa. Amma tun da ba ka yi abin da ba daidai ba, zunubi zai yi fakonka don yă rinjaye ka kamar naman jeji. Yana so yă mallake ka, amma tilas ka rinjaye shi.”
Kahawicalah na sak pawiteh ka dâw mahoeh maw. Kahawicalah na sak hoehpawiteh yon thuengnae sathei teh longkha koe a tabo. Ahnie a ngainae teh nange doeh. Hatei nang ni ahni na uk telah atipouh.
8 To, Kayinu ya ce wa ɗan’uwansa Habila, “Mu tafi gona.” Yayinda suke a gona, sai Kayinu ya tasar wa Habila ya buge shi ya kashe.
Kain ni a nawngha Abel koevah law lah cet sei atipouh. Law a pha roi torei teh Kain ni a nawngha a taran teh a thei.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Ina ɗan’uwanka Habila?” Sai Kayinu ya ce, “Ban sani ba, ni mai gadin ɗan’uwana ne?”
Hatdawkvah, BAWIPA ni Kain koe, na maw na nawngha Abel te, telah a pacei navah, ahni ni ka panuek hoeh, ka nawngha ka khoum e nahoeh telah atipouh.
10 Ubangiji ya ce, “Me ke nan ka yi? Saurara! Ga jinin ɗan’uwanka yana mini kuka daga ƙasa.
Hahoi, BAWIPA ni bangmaw na sak na nawngha e thi ni talai dawk hoi kai koe a hram toe.
11 Yanzu, kai la’ananne ne, an kuma kore ka daga ƙasa wadda ta buɗe bakinta ta shanye jinin ɗan’uwanka daga hannunka.
Na kut hoi na palawng e na nawngha thi, dâw hanelah apâhni ka ang e talai dawk hoi nang teh atu thoebo lah na o toe.
12 In ka nome ƙasa, ba za tă ƙara ba ka hatsinta ba. Za ka kuma zama mai yawo barkatai a duniya.”
Talai dawk thaw na tawk navah a thaonae nang koe tâcawt mahoeh toe. Nang teh talai vah, ka yawng e tami hoi ka kâva a e tami lah na o han telah atipouh.
13 Kayinu ya ce wa Ubangiji, “Horon nan ya sha ƙarfina.
Kain ni BAWIPA koevah, reknae ka hmu e heh ka phu thai e hlak a lenhnawn.
14 Ga shi, yau kana kori na daga ƙasar, zan zama a ɓoye daga fuskarka, zan kuma zama mai yawo barkatai, duk wanda ya same ni kuwa zai kashe ni.”
Sahnin teh talai hoi na pâlei toe ti ka panue. Na hmaitung hoi hro lah ka o toe. Talai van vah ka yawng e hoi yuengyoe kâva e tami lah kaawm vaiteh, ka hmawt e pueng ni na thei han doeh telah atipouh.
15 Amma Ubangiji ya ce masa, “Ba haka ba ne! Duk wanda ya kashe Kayinu, za a ninƙa hukuncinsa har sau bakwai.” Sa’an nan Ubangiji ya sa wa Kayinu alama don duk wanda ya same shi kada yă kashe shi.
Hatei, BAWIPA ni Kain koe nang ka thet e pueng teh let sari touh hoi a moi ka pathung han atipouh. Hahoi, BAWIPA ni Kain ka hmawt e tami, buet touh ni hai a thei hoeh nahanlah ahni dawk noutnae a ta pouh.
16 Saboda haka Kayinu ya yi tafiyarsa ya rabu da Ubangiji, ya je ya zauna ƙasar Nod a gabashin Eden.
Hathnukkhu, Kain teh BAWIPA e hmaitung hoi a tâco teh, Eden kanîtholah, Nod ram dawk kho a sak.
17 Kayinu ya kwana da matarsa, ta kuwa yi ciki, ta haifi Enok. A lokacin Kayinu yana gina birni, sai ya sa wa birnin sunan ɗansa Enok.
Kain ni a yu a panue teh, camo a vawn teh Enok a khe. Kho a thawng teh a capa min lah Enok kho telah min a poe.
18 Aka haifa wa Enok Irad, Irad kuma ya haifi Mehujayel, Mehujayel kuma ya haifi Metushayel, Metushayel kuma ya haifin Lamek.
Hahoi Enok ni Irad a khe. Irad ni Mehujael a khe. Mehujael ni Methushael a khe. Methushael ni Lamek a khe.
19 Lamek ya auri mata biyu, ana ce da ɗaya Ada, ɗayan kuma Zilla.
Hathnukkhu, Lamek ni a yu kahni touh a la teh, apasueke min teh Adah, apâhni e min teh Zillah doeh.
20 Ada ta haifi Yabal, shi ne mahaifi waɗanda suke zama a tentuna, suna kuma kiwon dabbobi.
Adah ni Jabal a khe. Ahni teh rimnaw dawk kho ka sak e lah ao teh saringnaw kapacakung e na pa lah ao.
21 Sunan ɗan’uwansa Yubal, shi ne mahaifin dukan makaɗan garaya da masu hura sarewa.
A nawngha e min teh Jubal. Ahni teh ratoung hoi vovitnaw ka pâtu e na pa lah ao.
22 Zilla ma ta haifi ɗa, Tubal-Kayinu, shi ne wanda ya ƙera kowane iri kayan aiki daga tagulla da kuma ƙarfe.’Yar’uwar Tubal-Kayinu ita ce Na’ama.
Zillah ni hai Tubal-kain a khe. Ahni teh rahum hoi sum ka dei pueng e na pa lah ao. Naamah teh Tubal-kain e tawncanu lah ao.
23 Wata rana, Lamek ya ce wa matansa, Ada da Zilla, “Ku saurara, matan Lamek, ku ji maganata. Na kashe wani saboda ya yi mini rauni, na kashe wani saurayi saboda ya ji mini ciwo.
Hahoi, Lamek ni a yu roi Adah hoi Zillah koevah, ka lawk thai roi haw, patawnae na poe dawkvah tongpa buet touh ka thei. Na pacekpahlek dawkvah, thoundoun buet touh ka thei toe.
24 Idan za a rama wa Kayinu har sau bakwai, lalle za a rama wa Lamek sau saba’in da bakwai ke nan.”
Kain ni let sari touh e moipathungnae khang pawiteh, Lamek ni teh a let 70 touh hoi a khang han.
25 Sai Adamu ya sāke kwana da matarsa, ta haifi ɗa, aka kuma ba shi suna Set, gama ta ce, “Allah ya ba ni wani yaro a madadin Habila, tun da yake Kayinu ya kashe shi.”
Hahoi, Adam ni a yu bout a panue teh, ca tongpa a khe. Seth telah min a phung. Bangkongtetpawiteh, Kain ni Abel a thei dawkvah Cathut ni alouke cati bout na poe telah ati.
26 Set ma ya haifi ɗa, ya kuma kira shi Enosh. A lokaci ne, mutane suka fara kira ga sunan Ubangiji.
Seth ni hai capa a khe teh Enosh telah min a phung. Hahoi tami ni Jehovah min kaw han a kamtawng awh.