< Farawa 39 >
1 To, aka kai Yusuf Masar, Fotifar wani mutumin Masar wanda yake ɗaya daga cikin hafsoshin Fir’auna, shugaban masu tsaro, ya saye shi daga mutanen Ishmayel waɗanda suka kai shi can.
Jožef je bil priveden dol v Egipt, in faraonov častnik Potifár, poveljnik straže, Egipčan, ga je kupil iz roke Izmaelcev, ki so ga privedli tja dol.
2 Ubangiji kuwa yana tare da Yusuf, Yusuf kuwa yi nasara, ya zauna a gidan mutumin Masar maigidansa.
Gospod pa je bil z Jožefom in bil je uspešen človek in bil je v hiši svojega gospodarja Egipčana.
3 Sa’ad da maigidansa ya ga cewa Ubangiji yana tare da Yusuf, kuma cewa Ubangiji ya ba shi nasara a kome da ya yi,
Njegov gospodar je videl, da je bil z njim Gospod in da je Gospod naredil, da je v njegovi roki vse uspevalo.
4 sai Yusuf ya sami tagomashi a idanunsa, ya kuma zama mai hidimarsa. Fotifar ya sa shi yă zama shugaba a gidansa, ya kuma danƙa masa kome da yake da shi.
Jožef je našel naklonjenost v njegovih očeh in mu služil. Postavil ga je za nadzornika nad svojo hišo in vse, kar je imel, je položil v njegovo roko.
5 Daga lokacin da ya sa shi shugaban gidansa da kuma a kan dukan abin da yake da shi, sai Ubangiji ya albarkaci gidan mutumin Masar saboda Yusuf. Albarkar Ubangiji tana a kan kome da Fotifar yake da shi a gida da kuma a jeji.
Pripetilo se je čez čas, ko ga je postavil za nadzornika v svoji hiši in nad vsem, kar je imel, da je Gospod zaradi Jožefa blagoslovil Egipčanovo hišo in Gospodov blagoslov je bil nad vsem, kar je imel v hiši in na polju.
6 Saboda haka sai ya bar kome a ƙarƙashin kulawar Yusuf, bai dame kansa a wani abu ba sai dai abincin da yake ci. To, fa, Yusuf ƙaƙƙarfa ne, kyakkyawa kuma,
Vse, kar je imel, je pustil v Jožefovi roki in ni vedel, kar bi moral, razen kruha, ki ga je jedel. Jožef pa je bil čedne zunanjosti in lepega videza.
7 bayan an ɗan jima sai matar maigidansa ta fara sha’awar Yusuf, sai ta ce, “Zo ka kwana da ni!”
Pripetilo se je po teh stvareh, da je gospodarjeva žena vrgla svoje oči na Jožefa in rekla: »Lezi z menoj.«
8 Amma ya ƙi. Ya ce mata, “Ga shi kome yana a ƙarƙashina, don haka ne ma maigidana bai dami kansa da wani abu a cikin gidan nan ba; kome da ya mallaka, ya danƙa ga kulawata.
Toda odklonil je in ženi svojega gospodarja rekel: »Glej, moj gospodar ne ve kaj je z menoj v hiši in vse, kar ima, je zaupal v mojo roko.
9 Babu wani da ya fi ni a wannan gida. Maigidana bai hana ni kome ba sai ke, saboda ke matarsa ce. Yaya fa, zan yi irin wannan mugun abu, in yi zunubi wa Allah?”
Nikogar večjega v tej hiši ni kakor jaz niti ni nobene stvari zadržal pred menoj, razen tebe, ker si njegova žena; kako lahko jaz potem storim to veliko zlobnost in grešim zoper Boga?«
10 Ko da yake ta yi ta yin wa Yusuf maganar kowace rana, amma ya ƙi yă kwana da ita, ko ma yă zauna da ita.
Pripetilo se je, ko je dan za dnem govorila Jožefu, da ji ni prisluhnil, da leži z njo ali da bi bil z njo.
11 Wata rana, ya shiga cikin gida don yă yi ayyukansa, ba wani daga cikin bayin gidan da yake ciki.
Pripetilo se je okoli tega časa, da je Jožef odšel v hišo, da opravi svoje opravilo in tam v hiši ni bilo nikogar od ljudi.
12 Sai ta cafke shi a riga, ta ce, “Zo ka kwana da ni!” Amma ya bar rigarsa a hannunta, ya gudu ya fita daga gidan.
Ona pa ga je ujela za njegovo obleko, rekoč: »Lezi z menoj« in pustil je svojo obleko v njeni roki, pobegnil in izginil ven.
13 Sa’ad da ta ga ya bar rigarsa a hannunta ya gudu ya fita daga gidan,
Pripetilo se je, ko je videla, da je v njeni roki pustil svojo obleko in je pobegnil naprej,
14 sai ta kira bayin gidan ta ce musu, “Duba, an kawo mana wannan mutumin Ibraniyawa don yă ci mutuncinmu! Ya zo nan don yă kwana da ni, amma na yi ihu.
da je zaklicala k možem svoje hiše in jim govorila, rekoč: »Vidite, k nam je privedel Hebrejca, da nas zasmehuje. Prišel je k meni, da leži z menoj, jaz pa sem zaklicala z močnim glasom.
15 Sa’ad da ya ji na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
Pripetilo se je, ko je zaslišal, da sem povzdignila svoj glas in zakričala, da je svojo obleko pustil pri meni, pobegnil in izginil ven.«
16 Ta ajiye rigar kusa da ita sai da maigidansa ya dawo gida.
Njegovo obleko je položila poleg sebe, dokler njen gospodar ni prišel domov.
17 Sa’an nan ta faɗa masa wannan labari, “Mutumin Ibraniyawan, bawan da ka kawo mana, ya zo wurina don yă ci mutuncina.
Govorila mu je glede na te besede, rekoč: »Hebrejski služabnik, ki si ga privedel k nam, je prišel noter k meni in me zasmehoval
18 Amma da zarar na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
in pripetilo se je, ko sem povzdignila svoj glas in zakričala, da je svojo obleko pustil pri meni in pobegnil.«
19 Sa’ad da maigidansa ya ji labarin da matarsa ta faɗa masa cewa, “Ga yadda bawanka ya yi da ni,” sai ya husata.
Pripetilo se je, ko je njegov gospodar slišal besede svoje žene, ki mu jih je govorila, rekoč: »Na ta način mi je storil tvoj služabnik, « da je bil vžgan njegov bes.
20 Maigidan Yusuf ya ɗauke shi ya sa a kurkuku, wurin da ake tsare’yan kurkukun sarki. Amma yayinda Yusuf yake can a cikin kurkuku,
Jožefov gospodar ga je vzel in ga vtaknil v ječo, kraj, kjer so bili zvezani kraljevi jetniki in bil je tam v ječi.
21 Ubangiji ya kasance tare da shi; ya nuna masa alheri, ya kuma sa ya sami tagomashi a idanun mai gadin kurkukun.
Toda Gospod je bil z Jožefom in mu izkazal usmiljenje in mu dal naklonjenost v očeh čuvaja ječe.
22 Saboda haka mai gadin ya sa Yusuf ya zama shugaban dukan waɗanda aka tsare a kurkukun, Yusuf ne kuma yake lura da dukan abin da ake yi a can.
Čuvaj ječe je v Jožefovo roko zaupal vse jetnike, ki so bili v ječi in karkoli so tam storili, je bil on izvršitelj tega.
23 Mai gadin ba ya sa kansa game da kome da yake ƙarƙashin kulawar Yusuf, gama Ubangiji yana tare da Yusuf, ya kuma ba shi nasara a cikin dukan abin da ya yi.
Čuvaj ječe ni gledal na nobeno stvar, ki je bila pod njegovo roko, ker je bil z njim Gospod in tisto, kar je naredil, je Gospod storil, da je to uspevalo.