< Farawa 39 >

1 To, aka kai Yusuf Masar, Fotifar wani mutumin Masar wanda yake ɗaya daga cikin hafsoshin Fir’auna, shugaban masu tsaro, ya saye shi daga mutanen Ishmayel waɗanda suka kai shi can.
U A laweia'ku la o Iosepa ilalo i Aigupita; kuaiia'ku la oia no Potipara, he luna na Parao, he luna o ka poe koa, a he kanaka no Aigupita, mai na lima aku o ka Isemaela, nana ia i lawe aku ilalo.
2 Ubangiji kuwa yana tare da Yusuf, Yusuf kuwa yi nasara, ya zauna a gidan mutumin Masar maigidansa.
Me Iosepa no o Iehova, he kanaka ia i hoopomaikaiia, aia no ia ma ka hale o kona haku, he Aigupita.
3 Sa’ad da maigidansa ya ga cewa Ubangiji yana tare da Yusuf, kuma cewa Ubangiji ya ba shi nasara a kome da ya yi,
Ike ae la kona haku, aia no o Iehova me Iosepa, a na Iehova no i pono ai ka hana a pau a kona lima.
4 sai Yusuf ya sami tagomashi a idanunsa, ya kuma zama mai hidimarsa. Fotifar ya sa shi yă zama shugaba a gidansa, ya kuma danƙa masa kome da yake da shi.
A loaa ia Iosepa ka lokomaikaiia imua ona, a hookauwa aku ia nana, a hoolilo aku la oia ia ia i luna no kona ohua, a no kona waiwai a pau, a waiho aku la ia i kana mea a pau i kona lima.
5 Daga lokacin da ya sa shi shugaban gidansa da kuma a kan dukan abin da yake da shi, sai Ubangiji ya albarkaci gidan mutumin Masar saboda Yusuf. Albarkar Ubangiji tana a kan kome da Fotifar yake da shi a gida da kuma a jeji.
Eia hoi kekahi, mai ka wa mai o kona hoolilo ana ia ia i luna no kona ohua, a maluna o kona mea a pau, hoopomaikai mai ke Akua i ko ka hale o ua kanaka Aigupita nei no Iosepa; a na Iehova no ka pomaikai o na mea a pau ona, ma ka hale, a ma ke kula.
6 Saboda haka sai ya bar kome a ƙarƙashin kulawar Yusuf, bai dame kansa a wani abu ba sai dai abincin da yake ci. To, fa, Yusuf ƙaƙƙarfa ne, kyakkyawa kuma,
A waiho iho la oia i kona mea a pau i na lima o Iosepa, aole ia i ike aku i kekahi mea nona, o ka ai ana i ai ai wale no. Ua maikai ke kino o Iosepa, he maikai no hoi ka maka.
7 bayan an ɗan jima sai matar maigidansa ta fara sha’awar Yusuf, sai ta ce, “Zo ka kwana da ni!”
A mahope iho o keia mau mea, ike mai la na maka o ka wahine a kona haku ia Iosepa, i mai la ia, E moe kaua.
8 Amma ya ƙi. Ya ce mata, “Ga shi kome yana a ƙarƙashina, don haka ne ma maigidana bai dami kansa da wani abu a cikin gidan nan ba; kome da ya mallaka, ya danƙa ga kulawata.
Hoole aku la ia, i aku la i ka wahine a kona haku, Aia hoi, aole ike kuu haku i na mea ia'u ma keia hale, ua waiho mai nei ko'u haku i kana mea a pau i kuu lima:
9 Babu wani da ya fi ni a wannan gida. Maigidana bai hana ni kome ba sai ke, saboda ke matarsa ce. Yaya fa, zan yi irin wannan mugun abu, in yi zunubi wa Allah?”
Aohe mea nui e ae oloko o keia hale, owau wale no; aole keia i paa aku i kekahi mea ia'u, o oe wale no, no ka mea, o kana wahine no oe. Pehea la wau e hana'i i keia hewa nui, a hana ino aku i ke Akua?
10 Ko da yake ta yi ta yin wa Yusuf maganar kowace rana, amma ya ƙi yă kwana da ita, ko ma yă zauna da ita.
Koi mai la oia ia Iosepa i keia la a i keia la, aole loa ia i hoolohe iki aku ia ia, e moe me ia, a e noho me ia.
11 Wata rana, ya shiga cikin gida don yă yi ayyukansa, ba wani daga cikin bayin gidan da yake ciki.
Ia manawa iho, komo ae la o Iosepa iloko o ka hale, e hana i kana hana, aohe kanaka o ka hale iloko.
12 Sai ta cafke shi a riga, ta ce, “Zo ka kwana da ni!” Amma ya bar rigarsa a hannunta, ya gudu ya fita daga gidan.
Apo mai la kela ia ia ma ke kapa ona, i mai la, E moe kaua. Haalele iho la ia i kona kapa ma ka lima ona, holo aku la a hiki iwaho.
13 Sa’ad da ta ga ya bar rigarsa a hannunta ya gudu ya fita daga gidan,
A ike aku la ua wahine la, ua haalele ia i kona kapa ma kona lima, a ua holo aku la iwaho,
14 sai ta kira bayin gidan ta ce musu, “Duba, an kawo mana wannan mutumin Ibraniyawa don yă ci mutuncinmu! Ya zo nan don yă kwana da ni, amma na yi ihu.
Kahea aku la ua wahine la i na kanaka o kona hale, olelo aku la ia lakou, i aku la, E nana oukou, ua lawe mai nei kela i ke kanaka no ka poe Hebera io kakou nei, e hoomaewaewa mai ia kakou. Hele mai la oia io'u nei e moe me au, a kahea aku la au me ka leo nui;
15 Sa’ad da ya ji na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
A lohe mai la kela i kuu hookiekie ana i kuu leo iluna, a i kuu hea ana aku, haalele iho nei oia i ke kapa ona ia'u, holo aku la a hiki iwaho.
16 Ta ajiye rigar kusa da ita sai da maigidansa ya dawo gida.
Malama iho la ua wahine la i kona kapa, a hoi mai la kona haku i ka hale.
17 Sa’an nan ta faɗa masa wannan labari, “Mutumin Ibraniyawan, bawan da ka kawo mana, ya zo wurina don yă ci mutuncina.
Olelo aku la ua wahine la ia ia i keia mau olelo, i aku la, O ko kauwa Hebera, au i lawe mai ai io kakou nei, ua komo mai ia io'u nei e hoomaewaewa mai ia'u.
18 Amma da zarar na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
A hookiekie au i kuu leo iluna a kahea aku au, alaila, haalele iho la ia i ke kapa ona ia'u, a holo aku la iwaho.
19 Sa’ad da maigidansa ya ji labarin da matarsa ta faɗa masa cewa, “Ga yadda bawanka ya yi da ni,” sai ya husata.
A lohe ae la kona haku i ka olelo a kana wahine i olelo mai ni ia ia, i ka i ana mai, E like me keia mau olelo i hana mai ai kau kauwa ia'u; nui iho la ka huhu ona.
20 Maigidan Yusuf ya ɗauke shi ya sa a kurkuku, wurin da ake tsare’yan kurkukun sarki. Amma yayinda Yusuf yake can a cikin kurkuku,
Lalau mai la ka haku o Iosepa ia in, hahao aku la ia ia iloko o ka halepaahao, i kahi i paa ai ka poe paa o ke alii, a paa no ia maluila ma ka halepaahao.
21 Ubangiji ya kasance tare da shi; ya nuna masa alheri, ya kuma sa ya sami tagomashi a idanun mai gadin kurkukun.
Me Iosepa no o Iehova, aloha nui mai la ia ia, a haawi mai la ia ia i ka pono imua o na maka o ka mea nana i malama ka halepaahao.
22 Saboda haka mai gadin ya sa Yusuf ya zama shugaban dukan waɗanda aka tsare a kurkukun, Yusuf ne kuma yake lura da dukan abin da ake yi a can.
Waiho ae la ka mea nana i malama ka halepaahao i ka poe paa a pau oloko o ka halepaahao i ka lima o Iosepa, a o na mea a pau i hanaia malaila, nana no ia i hana.
23 Mai gadin ba ya sa kansa game da kome da yake ƙarƙashin kulawar Yusuf, gama Ubangiji yana tare da Yusuf, ya kuma ba shi nasara a cikin dukan abin da ya yi.
Aole hoi i nana aku ka luna o ka halepaahao i kekahi mea malalo iho o kona lima, no ka mea, aia no o Iehova me ia, a hoopomaikai mai la o Iehova i ka hana a pau ana i hana'i.

< Farawa 39 >