< Farawa 39 >
1 To, aka kai Yusuf Masar, Fotifar wani mutumin Masar wanda yake ɗaya daga cikin hafsoshin Fir’auna, shugaban masu tsaro, ya saye shi daga mutanen Ishmayel waɗanda suka kai shi can.
Ioseph was brought vnto Egipte ad Putiphar a lorde of Pharaos: ad his chefe marshall an Egiptian bought him of ye Ismaelites which brought hi thither
2 Ubangiji kuwa yana tare da Yusuf, Yusuf kuwa yi nasara, ya zauna a gidan mutumin Masar maigidansa.
And the LORde was with Ioseph and he was a luckie felowe and continued in the house of his master the Egiptian.
3 Sa’ad da maigidansa ya ga cewa Ubangiji yana tare da Yusuf, kuma cewa Ubangiji ya ba shi nasara a kome da ya yi,
And his master sawe that the ORde was with him and that the LORde made all that he dyd prosper in his hande:
4 sai Yusuf ya sami tagomashi a idanunsa, ya kuma zama mai hidimarsa. Fotifar ya sa shi yă zama shugaba a gidansa, ya kuma danƙa masa kome da yake da shi.
Wherfore he founde grace in his masters syghte and serued him. And his master made him ruelar of his house and put all that he had in his hande.
5 Daga lokacin da ya sa shi shugaban gidansa da kuma a kan dukan abin da yake da shi, sai Ubangiji ya albarkaci gidan mutumin Masar saboda Yusuf. Albarkar Ubangiji tana a kan kome da Fotifar yake da shi a gida da kuma a jeji.
And as soone as he had made him ruelar ouer his house ad ouer all that he had the LORde blessed this Egiptians house for Iosephs sake and the blessynge of the LORde was vpon all that he had: both in the house and also in the feldes.
6 Saboda haka sai ya bar kome a ƙarƙashin kulawar Yusuf, bai dame kansa a wani abu ba sai dai abincin da yake ci. To, fa, Yusuf ƙaƙƙarfa ne, kyakkyawa kuma,
And therfore he left all that he had in Iosephs hande and loked vpon nothinge that was with him saue only on the bread which he ate. And Ioseph was a goodly persone and a well favored
7 bayan an ɗan jima sai matar maigidansa ta fara sha’awar Yusuf, sai ta ce, “Zo ka kwana da ni!”
And it fortuned after this that his masters wife cast hir eyes vpon Ioseph and sayde come lye with me.
8 Amma ya ƙi. Ya ce mata, “Ga shi kome yana a ƙarƙashina, don haka ne ma maigidana bai dami kansa da wani abu a cikin gidan nan ba; kome da ya mallaka, ya danƙa ga kulawata.
But he denyed and sayde to her: Beholde my master woteth not what he hath in the house with me but hath commytted all that he hath to my hande
9 Babu wani da ya fi ni a wannan gida. Maigidana bai hana ni kome ba sai ke, saboda ke matarsa ce. Yaya fa, zan yi irin wannan mugun abu, in yi zunubi wa Allah?”
He him selfe is not greatter in the house than I ad hath kepte nothige fro me but only the because thou art his wife. How than cam I do this great wykydnes for to synne agaynst God?
10 Ko da yake ta yi ta yin wa Yusuf maganar kowace rana, amma ya ƙi yă kwana da ita, ko ma yă zauna da ita.
And after this maner spake she to Ioseph daye by daye: but he harkened not vnto her to slepe nere her or to be in her company.
11 Wata rana, ya shiga cikin gida don yă yi ayyukansa, ba wani daga cikin bayin gidan da yake ciki.
And it fortuned aboute the same season that Ioseph entred in to the house to do his busynes: and there was none of the houshold by in the house.
12 Sai ta cafke shi a riga, ta ce, “Zo ka kwana da ni!” Amma ya bar rigarsa a hannunta, ya gudu ya fita daga gidan.
And she caught him by the garment saynge: come slepe with me. And he left his garment in hir hande ad fled and gott him out
13 Sa’ad da ta ga ya bar rigarsa a hannunta ya gudu ya fita daga gidan,
when she sawe that he had left his garmet in hir hande and was fled out
14 sai ta kira bayin gidan ta ce musu, “Duba, an kawo mana wannan mutumin Ibraniyawa don yă ci mutuncinmu! Ya zo nan don yă kwana da ni, amma na yi ihu.
she called vnto the men of the house and tolde them saynge: Se he hath brought in an Hebrewe vnto vs to do vs shame. for he came in to me for to haue slept myth me. But I cried with a lowde voyce.
15 Sa’ad da ya ji na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
And when he harde that I lyfte vp my voyce and cryed he left his garment with me and fled awaye and got him out.
16 Ta ajiye rigar kusa da ita sai da maigidansa ya dawo gida.
And she layed vp his garment by her vntill hir lorde came home.
17 Sa’an nan ta faɗa masa wannan labari, “Mutumin Ibraniyawan, bawan da ka kawo mana, ya zo wurina don yă ci mutuncina.
And she told him acordynge to these wordes saynge. This Hebrues servaunte which thou hast brought vnto vs came in to me to do me shame.
18 Amma da zarar na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
But as soone as I lyft vp my voyce and cryed he left his garment with me and fled out.
19 Sa’ad da maigidansa ya ji labarin da matarsa ta faɗa masa cewa, “Ga yadda bawanka ya yi da ni,” sai ya husata.
When his master herde the woordes of his wyfe which she tolde him saynge: after this maner dyd thy servaunte to me he waxed wrooth.
20 Maigidan Yusuf ya ɗauke shi ya sa a kurkuku, wurin da ake tsare’yan kurkukun sarki. Amma yayinda Yusuf yake can a cikin kurkuku,
And he toke Ioseph and put him in pryson: euen in the place where the kinges prisoners laye bounde. And there contynued he in preson.
21 Ubangiji ya kasance tare da shi; ya nuna masa alheri, ya kuma sa ya sami tagomashi a idanun mai gadin kurkukun.
But the LORde was with Ioseph ad shewed him mercie and gott him fauoure in the syghte of the keper of ye preson
22 Saboda haka mai gadin ya sa Yusuf ya zama shugaban dukan waɗanda aka tsare a kurkukun, Yusuf ne kuma yake lura da dukan abin da ake yi a can.
which commytted to Iosephe hade all the presoners that were in the preson housse. And what soeuer was done there yt dyd he.
23 Mai gadin ba ya sa kansa game da kome da yake ƙarƙashin kulawar Yusuf, gama Ubangiji yana tare da Yusuf, ya kuma ba shi nasara a cikin dukan abin da ya yi.
And the keper of the preso loked vnto nothinge that was vnder his hande because the LORde was with him and because that what soeuer he dyd the LORde made it come luckely to passe.