< Farawa 39 >

1 To, aka kai Yusuf Masar, Fotifar wani mutumin Masar wanda yake ɗaya daga cikin hafsoshin Fir’auna, shugaban masu tsaro, ya saye shi daga mutanen Ishmayel waɗanda suka kai shi can.
Meanwhile, Joseph was led into Egypt. And Putiphar, a eunuch of Pharaoh, a leader of the army, an Egyptian man, purchased him from the hand of the Ishmaelites, by whom he was brought.
2 Ubangiji kuwa yana tare da Yusuf, Yusuf kuwa yi nasara, ya zauna a gidan mutumin Masar maigidansa.
And the Lord was with him, and he was a man who prospered in everything that he did. And he lived in the house of his lord,
3 Sa’ad da maigidansa ya ga cewa Ubangiji yana tare da Yusuf, kuma cewa Ubangiji ya ba shi nasara a kome da ya yi,
who knew very well that the Lord was with him, and that all the things that were done by him were directed by his hand.
4 sai Yusuf ya sami tagomashi a idanunsa, ya kuma zama mai hidimarsa. Fotifar ya sa shi yă zama shugaba a gidansa, ya kuma danƙa masa kome da yake da shi.
And Joseph found favor in the sight of his lord, and he ministered to him. And, having been placed in charge of everything by him, he governed the house that was entrusted to him and all the things that had been delivered to him.
5 Daga lokacin da ya sa shi shugaban gidansa da kuma a kan dukan abin da yake da shi, sai Ubangiji ya albarkaci gidan mutumin Masar saboda Yusuf. Albarkar Ubangiji tana a kan kome da Fotifar yake da shi a gida da kuma a jeji.
And the Lord blessed the house of the Egyptian, because of Joseph, and he multiplied all his substance, as much in the buildings, as in the fields.
6 Saboda haka sai ya bar kome a ƙarƙashin kulawar Yusuf, bai dame kansa a wani abu ba sai dai abincin da yake ci. To, fa, Yusuf ƙaƙƙarfa ne, kyakkyawa kuma,
Neither did he know anything other than the bread that he ate. Now Joseph was beautiful in form, and stately in appearance.
7 bayan an ɗan jima sai matar maigidansa ta fara sha’awar Yusuf, sai ta ce, “Zo ka kwana da ni!”
And so, after many days, his mistress cast her eyes on Joseph, and she said, “Sleep with me.”
8 Amma ya ƙi. Ya ce mata, “Ga shi kome yana a ƙarƙashina, don haka ne ma maigidana bai dami kansa da wani abu a cikin gidan nan ba; kome da ya mallaka, ya danƙa ga kulawata.
And without consenting at all to the wicked act, he said to her: “Behold, my lord has delivered all things to me, and he does not know what he has in his own house.
9 Babu wani da ya fi ni a wannan gida. Maigidana bai hana ni kome ba sai ke, saboda ke matarsa ce. Yaya fa, zan yi irin wannan mugun abu, in yi zunubi wa Allah?”
Neither is there anything which is not in my power, or that he has not delivered to me, except you, for you are his wife. How then can I do this evil act and sin against my God?”
10 Ko da yake ta yi ta yin wa Yusuf maganar kowace rana, amma ya ƙi yă kwana da ita, ko ma yă zauna da ita.
With such words as these, throughout each day, the woman was pestering the young man, and he was refusing the adultery.
11 Wata rana, ya shiga cikin gida don yă yi ayyukansa, ba wani daga cikin bayin gidan da yake ciki.
Then it happened, on a certain day, that Joseph entered the house, and he was doing something, without any witnesses.
12 Sai ta cafke shi a riga, ta ce, “Zo ka kwana da ni!” Amma ya bar rigarsa a hannunta, ya gudu ya fita daga gidan.
And she, grasping the hem of his garment, said, “Sleep with me.” But he, leaving behind the cloak in her hand, fled and went outside.
13 Sa’ad da ta ga ya bar rigarsa a hannunta ya gudu ya fita daga gidan,
And when the woman saw the garment in her hands and herself being treated with disrespect,
14 sai ta kira bayin gidan ta ce musu, “Duba, an kawo mana wannan mutumin Ibraniyawa don yă ci mutuncinmu! Ya zo nan don yă kwana da ni, amma na yi ihu.
she called to herself the men of her house, and she said to them: “Lo, he has brought in a Hebrew man to abuse us. He entered toward me, in order to join with me; and when I had shouted out,
15 Sa’ad da ya ji na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
and he had heard my voice, he left behind the cloak that I held, and he fled outside.”
16 Ta ajiye rigar kusa da ita sai da maigidansa ya dawo gida.
As a proof, therefore, of her fidelity, she retained the cloak, and she showed it to her husband, when he returned home.
17 Sa’an nan ta faɗa masa wannan labari, “Mutumin Ibraniyawan, bawan da ka kawo mana, ya zo wurina don yă ci mutuncina.
And she said: “The Hebrew servant, whom you have brought in to me, approached me to abuse me.
18 Amma da zarar na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
And when he had heard me cry out, he left behind the cloak that I held, and he fled outside.”
19 Sa’ad da maigidansa ya ji labarin da matarsa ta faɗa masa cewa, “Ga yadda bawanka ya yi da ni,” sai ya husata.
His lord, upon hearing these things, and having excessive trust in the words of his mate, was very angry.
20 Maigidan Yusuf ya ɗauke shi ya sa a kurkuku, wurin da ake tsare’yan kurkukun sarki. Amma yayinda Yusuf yake can a cikin kurkuku,
And he delivered Joseph into prison, where the prisoners of the king were kept, and he was enclosed in that place.
21 Ubangiji ya kasance tare da shi; ya nuna masa alheri, ya kuma sa ya sami tagomashi a idanun mai gadin kurkukun.
But the Lord was with Joseph, and, having mercy on him, he gave him favor in the sight of the leader of the prison,
22 Saboda haka mai gadin ya sa Yusuf ya zama shugaban dukan waɗanda aka tsare a kurkukun, Yusuf ne kuma yake lura da dukan abin da ake yi a can.
who delivered into his hand all the prisoners who were held in custody. And whatever was done, was under him.
23 Mai gadin ba ya sa kansa game da kome da yake ƙarƙashin kulawar Yusuf, gama Ubangiji yana tare da Yusuf, ya kuma ba shi nasara a cikin dukan abin da ya yi.
Neither did he himself know anything, having entrusted all things to him. For the Lord was with him, and he directed everything that he did.

< Farawa 39 >