< Farawa 38 >

1 A wannan lokaci, Yahuda ya bar’yan’uwansa ya gangara don yă zauna da mutumin Adullam, mai suna Hira.
Dans le même temps, Juda, s’éloignant de ses frères, alla loger chez un homme d’Odollam, du nom d’Hiras.
2 A can Yahuda ya sadu da’yar wani Bakan’ane, mai suna Shuwa. Ya aure ta, ya kuma kwana da ita;
Et il vit là la fille d’un homme de Chanaan, du nom de Sué, et l’ayant prise pour femme, il vécut avec elle.
3 ta yi ciki, ta kuma haifi ɗa, wanda aka kira Er.
Elle conçut et enfanta un fils, et elle lui donna le nom de Her.
4 Ta sāke yin ciki, ta haifi wani ɗa, ta kira shi Onan.
Et ayant conçu une seconde fois, elle nomma le fils qui naquit Onan.
5 Ta kuma haifi wani ɗa har yanzu, aka kuwa ba shi suna Shela. A Kezib ne ta haife shi.
Elle en enfanta aussi un troisième, qu’elle appela Séla: celui-ci né, elle cessa d’enfanter davantage.
6 Sai Yahuda ya auro wa Er mata, ɗansa na fari, sunanta Tamar.
Or Juda donna à son premier-né Her une femme du nom de Thamar.
7 Amma Er, ɗan farin Yahuda mugu ne a fuskar Ubangiji, saboda haka Ubangiji ya kashe shi.
Mais Her, le premier-né de Juda, fut très méchant eu la présence du Seigneur; et par le Seigneur il fut frappé de mort.
8 Sa’an nan Yahuda ya ce wa Onan, “Ka kwana da matar ɗan’uwanka ka cika wajibinka gare ta a matsayin ɗan’uwan miji, don ka samar wa ɗan’uwanka’ya’ya.”
Juda dit donc à Onan, son fils: Prends la femme de ton frère, et unis-toi à elle pour susciter des enfants à ton frère.
9 Amma Onan ya san cewa’ya’yan ba za su zama nasa ba; saboda haka a duk sa’ad da ya kwana da matar ɗan’uwansa, sai yă zub da maniyyinsa a ƙasa don kada yă samar wa ɗan’uwansa’ya’ya.
Mais celui-ci sachant que les enfants qui naîtraient de son union avec la femme de son frère ne seraient pas à lui, empêchait qu’elle ne devînt mère, pour ne pas qu’il naquît des enfants du nom de son frère.
10 Abin nan da ya yi mugunta ce a gaban Ubangiji, saboda haka Ubangiji ya kashe shi, shi ma.
Et c’est pourquoi le Seigneur le frappa, parce qu’il faisait une chose détestable.
11 Sai Yahuda ya ce wa surukarsa Tamar, “Ki yi zama kamar gwauruwa a gidan mahaifinki sai ɗana Shela ya yi girma.” Gama ya yi tunani, “Shi ma zai mutu, kamar’yan’uwansa.” Saboda haka Tamar ta je ta zauna a gidan mahaifinta.
A cause de cela Juda dit à Thamar sa belle-fille: Reste veuve dans la maison de ton père, jusqu’à ce que Séla mon fils soit devenu grand; car il craignait que lui aussi ne mourût comme ses frères. Celle-ci s’en alla et habita dans la maison de son père.
12 Bayan an daɗe sai matar Yahuda,’yar Shuwa ta rasu. Sa’ad da Yahuda ya gama makoki, sai ya haura zuwa Timna, zuwa wurin mutanen da suke askin tumakinsa, abokinsa Hira mutumin Adullam kuwa ya tafi tare da shi.
Mais bien des jours s’étant écoulés, mourut la fille de Sué, femme de Juda, qui s’étant consolé après le deuil, montait à Thamnas vers les tondeurs de brebis, lui et Hiras d’Odollam, pasteur de ses troupeaux.
13 Sa’ad da aka faɗa wa Tamar cewa, “Surukinki yana kan hanyarsa zuwa Timna don askin tumakinsa,”
Or on annonça à Thamar que son beau-père montait à Thamnas pour tondre ses brebis.
14 sai ta tuɓe rigunan gwaurancinta ta rufe kanta da lulluɓi don ta ɓad da kamanninta, sa’an nan ta je ta zauna a ƙofar shigar Enayim, wadda take a hanyar zuwa Timna. Gama ta lura cewa ko da yake Shela yanzu ya yi girma, ba a ba da ita gare shi ta zama matarsa ba.
Celle-ci, ses habits de veuvage quittés, prit un voile, et s’étant déguisée, elle s’assit dans le carrefour du chemin qui conduit à Thamnas, parce que Séla était déjà devenu grand, et qu’elle ne l’avait pas eu pour époux.
15 Sa’ad da Yahuda ya gan ta, ya yi tsammani karuwa ce, gama ta lulluɓe fuskarta.
Lorsque Juda l’eut aperçue, il crut que c’était une femme de mauvaise vie; car elle avait couvert son visage, afin qu’elle ne fût pas reconnue.
16 Bai san cewa ita surukarsa ce ba, sai ya ratse zuwa wurinta a gefen hanya ya ce, “Zo mana, in kwana da ke.” Sai ta ce, “Me za ka ba ni in na kwana da kai?”
Et s’approchant d’elle, il dit: Laisse-moi aller avec toi; car il ne savait pas qu’elle fût sa belle-fille. Elle répondant: Que me donneras-tu pour que tu viennes avec moi?
17 Ya ce, “Zan aika miki da ɗan akuya daga garkena.” Sai ta ce, “Za ka ba ni wani abu jingina, kafin ka aika da shi?”
Il dit: Je t’enverrai un chevreau de mes troupeaux. Mais elle reprenant: Je consentirai à ce que tu veux, si tu me donnes un gage, en attendant que tu envoies ce que tu promets.
18 Ya ce, “Wace jingina zan ba ki?” Sai ta amsa, “Hatiminka da ka rataye a wuya da kuma sandan da yake a hannunka.” Ya ba da su gare ta, ya kuma kwana da ita, sai ta yi ciki.
Juda lui demanda: Que veux-tu que je te donne pour gage? Elle répondit: Ton anneau, ton bracelet et le bâton que tu liens à la main. Ayant donc vu Juda une seule fois, cette femme conçut,
19 Bayan ta tafi, sai ta tuɓe lulluɓin, ta sāke sa tufafin gwaurancinta.
Et se levant, elle s’en alla; puis ayant quitté le vêtement qu’elle avait pris, elle se revêtit de ses habits de veuvage.
20 Ana cikin haka sai Yahuda ya aika da ɗan akuya ta hannun abokinsa mutumin Adullam don yă karɓo masa jinginar daga wurin macen, amma bai same ta a can ba.
Or Juda envoya le chevreau par son pasteur qui était d’Odollam, afin qu’il retirât le gage qu’il avait donné à cette femme; celui-ci ne l’ayant pas trouvée,
21 Ya tambayi mutanen da suke zama a can ya ce, “Ina karuwar haikalin da take a bakin hanya a Enayim?” Sai suka ce, “Ba a taɓa kasance da karuwar haikali a nan ba.”
Demanda aux hommes de ce lieu: Où est cette femme qui était assise dans le carrefour? Tous répondant: Il n’y a pas eu en ce lieu de femme de mauvaise vie.
22 Saboda haka sai ya koma zuwa wurin Yahuda ya ce, “Ban same ta ba. Ban da haka ma, mutanen da suke zama a can, sun ce, ‘Ba a taɓa kasance da wata karuwar haikali a nan ba.’”
Il revint vers Juda et lui dit: Je ne l’ai pas trouvée; et les hommes même de ce lieu m’ont dit que jamais là ne s’est assise femme débauchée.
23 Sa’an nan Yahuda ya ce, “Bari tă riƙe kayan kiɗa garin nema mu zama abin dariya. Ni kam, na aika da tunkiyar amma ba a same ta ba.”
Juda répondit: Qu’elle le garde; elle ne peut pas au moins nous accuser de mensonge; moi, j’ai envoyé le chevreau que j’avais promis, et toi, tu ne l’as pas trouvée.
24 Bayan misalin wata uku sai aka faɗa wa Yahuda cewa, “Tamar, surukarka ta yi laifin karuwanci, a sakamakon haka yanzu ta yi ciki.” Yahuda ya ce, “A fid da ita, a ƙone!”
Mais voilà qu’après trois mois on annonça à Juda cette nouvelle: Thamar ta belle-fille a forniqué, et elle paraît être enceinte. Juda répondit: Produisez-la en public, afin qu’elle soit brûlée.
25 Yayinda ake fitar da ita, sai ta aika saƙo zuwa wurin surukinta, ta ce, “Mutumin da yake da waɗannan kayan ne ya yi mini ciki.” Ta kuma ƙara da cewa, “Duba ko za ka gane da hatimin nan, da abin ɗamaran nan, da kuma sandan nan, ko na wane ne?”
Thamar, comme elle était conduite au supplice, envoya vers son beau-père, disant: C’est de l’homme à qui sont ces gages que j’ai conçu: vois à qui sont cet anneau, ce bracelet et ce bâton.
26 Yahuda ya gane su, sai ya ce, “Ai, ta fi ni gaskiya, da yake ban ba da ita ga ɗana Shela ba.” Bai kuwa ƙara kwana da ita ba.
Juda, les gages reconnus, dit: Elle est plus juste que moi, puisque je ne l’ai pas donnée à Séla mon fils. Toutefois il ne la connut pas depuis.
27 Sa’ad da lokaci ya yi da za tă haihu, ashe, tagwaye’yan maza ne suke cikinta.
Or les couches pressant, parurent deux jumeaux dans son sein; et à la sortie même des enfants, l’un présenta sa main, à laquelle la sage-femme lia un fil d’écarlate, disant:
28 Yayinda take haihuwa, ɗaya daga cikinsu ya fid da hannunsa; sai ungonzomar ta ɗauki jan zare ta ɗaura a hannun, ta ce, “Wannan ne ya fito da farko.”
Celui-ci sortira le premier.
29 Amma sa’ad da ya janye hannunsa, sai ɗan’uwansa ya fito, sai ta ce, “Wato, haka ne ka keta ka fito!” Sai aka ba shi suna Ferez.
Mais, lui retirant sa main, l’autre sortit; et la sage-femme dit: Pourquoi le mur a-t-il été rompu à cause de toi? Or pour cette raison elle lui donna le nom de Pharès.
30 Sa’an nan ɗan’uwansa wanda yake da jan zare a hannunsa ya fito, aka kuma ba shi suna Zera.
Ensuite sortit son frère, à la main duquel était le fil d’écarlate; elle l’appela Zara.

< Farawa 38 >