< Farawa 38 >

1 A wannan lokaci, Yahuda ya bar’yan’uwansa ya gangara don yă zauna da mutumin Adullam, mai suna Hira.
And it fortuned at that tyme that Iudas went from his brethren and gatt him to a man called Hira of Odollam
2 A can Yahuda ya sadu da’yar wani Bakan’ane, mai suna Shuwa. Ya aure ta, ya kuma kwana da ita;
and there he sawe the doughter of a man called Sua a Canaanyte. And he toke her ad went in vnto her.
3 ta yi ciki, ta kuma haifi ɗa, wanda aka kira Er.
And she conceaued and bare a sonne and called his name Er.
4 Ta sāke yin ciki, ta haifi wani ɗa, ta kira shi Onan.
And she conceaued agayne and bare a sonne and called him Onan.
5 Ta kuma haifi wani ɗa har yanzu, aka kuwa ba shi suna Shela. A Kezib ne ta haife shi.
And she conceaued the thyrde tyme and bare a sonne whom she called Scla: and he was at Chesyb when she bare hem.
6 Sai Yahuda ya auro wa Er mata, ɗansa na fari, sunanta Tamar.
And Iudas gaue Er his eldest sonne a wife whose name was Thamar.
7 Amma Er, ɗan farin Yahuda mugu ne a fuskar Ubangiji, saboda haka Ubangiji ya kashe shi.
But this Er Iudas eldest sonne was wicked in the syghte of the LORde wherfore the LORde slewe him.
8 Sa’an nan Yahuda ya ce wa Onan, “Ka kwana da matar ɗan’uwanka ka cika wajibinka gare ta a matsayin ɗan’uwan miji, don ka samar wa ɗan’uwanka’ya’ya.”
Than sayde Iudas vnto Onan: goo in to thi brothers wyfe and Marie her and styrre vp seed vnto thy brother.
9 Amma Onan ya san cewa’ya’yan ba za su zama nasa ba; saboda haka a duk sa’ad da ya kwana da matar ɗan’uwansa, sai yă zub da maniyyinsa a ƙasa don kada yă samar wa ɗan’uwansa’ya’ya.
And when Onan perceaued that the seed shulde not be his: therfore when he went in to his brothers wife he spylled it on the grounde because he wold not geue seed vnto his brother.
10 Abin nan da ya yi mugunta ce a gaban Ubangiji, saboda haka Ubangiji ya kashe shi, shi ma.
And the thinge which he dyd displeased the LORde wherfore he slew him also.
11 Sai Yahuda ya ce wa surukarsa Tamar, “Ki yi zama kamar gwauruwa a gidan mahaifinki sai ɗana Shela ya yi girma.” Gama ya yi tunani, “Shi ma zai mutu, kamar’yan’uwansa.” Saboda haka Tamar ta je ta zauna a gidan mahaifinta.
Than sayde Iudas to Thamar his doughter in lawe: remayne a wydow at thi fathers house tyll Sela my sonne be growne: for he feared lest he shulde haue dyed also as his brethren did. Thus went Thamar and dwelt in hir fathers house.
12 Bayan an daɗe sai matar Yahuda,’yar Shuwa ta rasu. Sa’ad da Yahuda ya gama makoki, sai ya haura zuwa Timna, zuwa wurin mutanen da suke askin tumakinsa, abokinsa Hira mutumin Adullam kuwa ya tafi tare da shi.
And in processe of tyme the doughter of Sua Iudas wife dyed. Than Iudas when he had left mornynge went vnto his shepe sherers to Thimnath with his frende Hira of Odollam.
13 Sa’ad da aka faɗa wa Tamar cewa, “Surukinki yana kan hanyarsa zuwa Timna don askin tumakinsa,”
And one told Thamar saynge: beholde thy father in lawe goth vp to Thimnath to shere his shepe.
14 sai ta tuɓe rigunan gwaurancinta ta rufe kanta da lulluɓi don ta ɓad da kamanninta, sa’an nan ta je ta zauna a ƙofar shigar Enayim, wadda take a hanyar zuwa Timna. Gama ta lura cewa ko da yake Shela yanzu ya yi girma, ba a ba da ita gare shi ta zama matarsa ba.
And she put hyr wydows garmetes of from her and couered her with a clooke and disgyssed herself: And sat her downe at the entrynge of Enaim which is by the hye wayes syde to Thimnath for because she sawe that Sela was growne and she was not geue vnto him to wife.
15 Sa’ad da Yahuda ya gan ta, ya yi tsammani karuwa ce, gama ta lulluɓe fuskarta.
When Iuda sawe her he thought it had bene an hoore because she had couered hyr face.
16 Bai san cewa ita surukarsa ce ba, sai ya ratse zuwa wurinta a gefen hanya ya ce, “Zo mana, in kwana da ke.” Sai ta ce, “Me za ka ba ni in na kwana da kai?”
And turned to her vnto the waye and sayde come I praye the let me lye with the for he knewe not that it was his doughter in lawe. And she sayde what wylt thou gyue me for to lye with me?
17 Ya ce, “Zan aika miki da ɗan akuya daga garkena.” Sai ta ce, “Za ka ba ni wani abu jingina, kafin ka aika da shi?”
Tha sayde he I will sende the a kydd fro the flocke. She answered Than geue me a pledge till thou sende it.
18 Ya ce, “Wace jingina zan ba ki?” Sai ta amsa, “Hatiminka da ka rataye a wuya da kuma sandan da yake a hannunka.” Ya ba da su gare ta, ya kuma kwana da ita, sai ta yi ciki.
Than sayde he what pledge shall I geue the? And she sayde: they sygnett thy necke lace and thy staffe that is in thy hande. And he gaue it her and lay by her and she was with child by him.
19 Bayan ta tafi, sai ta tuɓe lulluɓin, ta sāke sa tufafin gwaurancinta.
And she gatt her vp and went and put her mantell from her ad put on hir widowes rayment agayne.
20 Ana cikin haka sai Yahuda ya aika da ɗan akuya ta hannun abokinsa mutumin Adullam don yă karɓo masa jinginar daga wurin macen, amma bai same ta a can ba.
And Iudas sent the kydd by his neybure of Odollam for to fetch out his pledge agayne from the wifes hande. But he fownde her not.
21 Ya tambayi mutanen da suke zama a can ya ce, “Ina karuwar haikalin da take a bakin hanya a Enayim?” Sai suka ce, “Ba a taɓa kasance da karuwar haikali a nan ba.”
Than asked he the men of the same place saynge: where is the whoore that satt at Enaim in the waye? And they sayde: there was no whoore here.
22 Saboda haka sai ya koma zuwa wurin Yahuda ya ce, “Ban same ta ba. Ban da haka ma, mutanen da suke zama a can, sun ce, ‘Ba a taɓa kasance da wata karuwar haikali a nan ba.’”
And he came to Iuda agayne saynge: I can not fynde her and also the men of the place sayde: that there was no whoore there.
23 Sa’an nan Yahuda ya ce, “Bari tă riƙe kayan kiɗa garin nema mu zama abin dariya. Ni kam, na aika da tunkiyar amma ba a same ta ba.”
And Iuda sayde: let her take it to her lest we be shamed: for I sente the kydd and thou coudest not fynde her.
24 Bayan misalin wata uku sai aka faɗa wa Yahuda cewa, “Tamar, surukarka ta yi laifin karuwanci, a sakamakon haka yanzu ta yi ciki.” Yahuda ya ce, “A fid da ita, a ƙone!”
And it came to passe that after. iij. monethes one tolde Iuda saynge: Thamar thy doughter in lawe hath played the whoore and with playnge the whoore is become great with childe. And Iuda sayde: brynge her forth ad let her be brente.
25 Yayinda ake fitar da ita, sai ta aika saƙo zuwa wurin surukinta, ta ce, “Mutumin da yake da waɗannan kayan ne ya yi mini ciki.” Ta kuma ƙara da cewa, “Duba ko za ka gane da hatimin nan, da abin ɗamaran nan, da kuma sandan nan, ko na wane ne?”
And when they brought her forth she sent to her father in lawe saynge: by the ma vnto whome these thinges pertayne am I with childe. And sayd also: loke whose are this seall necklace and staffe.
26 Yahuda ya gane su, sai ya ce, “Ai, ta fi ni gaskiya, da yake ban ba da ita ga ɗana Shela ba.” Bai kuwa ƙara kwana da ita ba.
And Iuda knewe them saynge: she is more rightwes tha I because I gaue her not to Sela my sone. But he laye with her nomore.
27 Sa’ad da lokaci ya yi da za tă haihu, ashe, tagwaye’yan maza ne suke cikinta.
When tyme was come that she shulde be delyuered beholde there was. ij. twynnes in hyr wobe.
28 Yayinda take haihuwa, ɗaya daga cikinsu ya fid da hannunsa; sai ungonzomar ta ɗauki jan zare ta ɗaura a hannun, ta ce, “Wannan ne ya fito da farko.”
And as she traveled the one put out his hande and the mydwife toke and bownde a reed threde aboute it saynge: this wyll come out fyrst.
29 Amma sa’ad da ya janye hannunsa, sai ɗan’uwansa ya fito, sai ta ce, “Wato, haka ne ka keta ka fito!” Sai aka ba shi suna Ferez.
But he plucked his hande backe agayne and his brother came out. And she sayde: wherfore hast thou rent a rent vppon the? and called him Pharez.
30 Sa’an nan ɗan’uwansa wanda yake da jan zare a hannunsa ya fito, aka kuma ba shi suna Zera.
And afterward came out his brother that had the reade threde about his hade which was called Zarah.

< Farawa 38 >