< Farawa 37 >
1 Yaƙub ya zauna a ƙasar da mahaifinsa ya zauna, wato, ƙasar Kan’ana.
UJakhobe wahlala elizweni lapho uyise laye ahlala kulo, ilizwe laseKhenani.
2 Wannan shi ne labarin zuriyar Yaƙub. Yusuf, saurayi ne mai shekara goma sha bakwai. Shi da’yan’uwansa, wato,’ya’yan Bilha maza da kuma’ya’yan Zilfa maza, matan mahaifinsa suna kiwon garkuna tare. Sai Yusuf ya kawo wa mahaifinsu rahoto marar kyau game da’yan’uwansa.
Lo ngumlando wosendo lukaJakhobe. UJosefa ijaha elalileminyaka elitshumi lesikhombisa, wayeselusa imihlambi yezimvu labanewabo, amadodana kaBhiliha lamadodana kaZilipha, abafazi bakayise, wasebaceba kuyise.
3 Isra’ila dai ya fi ƙaunar Yusuf fiye da kowanne a cikin sauran’ya’yansa maza, gama an haifa masa shi a cikin tsufansa. Sai ya yi masa riga mai gwanin kyau.
U-Israyeli wasuka wamthanda uJosefa ukwedlula wonke amanye amadodana akhe, ngoba wamzala eseluphele; yikho wamenzela ijazi eliceciswe kakhulu.
4 Sa’ad da’yan’uwansa suka ga cewa mahaifinsu ya fi ƙaunarsa fiye da kowanne daga cikinsu, sai suka ƙi jininsa, ba sa kuma maganar alheri da shi.
Kwathi abafowabo bebona ukuthi uyise wayemthanda ukwedlula bonke abanye bamzonda kabazange bamkhulumise ngothando.
5 Sai Yusuf ya yi mafarki, sa’ad da ya faɗa wa’yan’uwansa, suka ƙara ƙin jininsa.
UJosefa waphupha, wathi esebatshelile ngephupho lakhe bamzonda ngokwedlulisileyo.
6 Ya ce musu, “Ku saurari wannan mafarkin da na yi.
Wathi kubo, “Zwanini iphupho engibe lalo:
7 Muna daurin dammunan hatsi a gona, sai nan da nan damina ya tashi ya tsaya, yayinda dammunanku suka taru kewaye da nawa suka rusuna masa.”
besibopha izithungo zamabele sisemasimini lapho okuthe masinyane esami isithungo saphakama sema saqonda, kwathi ezenu izithungo zasigombolozela esami, zasikhothamela phansi.”
8 Sai’yan’uwansa suka ce masa, “Kana nufin za ka yi mulki a kanmu ke nan? Ko kuwa za ka zama sarki, a bisanmu?” Suka ƙara ƙin jininsa saboda mafarkinsa da kuma abin da ya faɗa.
Abanewabo bathi kuye. “Ufisa ukubusa phezu kwethu na? Ungasibusa ngempela na?” Basebemzonda ngamandla ngenxa yephupho lakhe lalokho ayekutshilo.
9 Sai Yusuf ya sāke yin wani mafarki, ya faɗa wa’yan’uwansa. Ya ce, “Ku saurara, na sāke yin wani mafarki, a wannan lokaci, na ga rana da wata da taurari goma sha ɗaya suna rusuna mini.”
Waphinda waba lelinye iphupho, walitshela abanewabo. Wathi, “Lalelani, ngibe lalo elinye iphupho, kuleli, ilanga lenyanga kanye lezinkanyezi ezilitshumi lanye bezingikhothamela phansi.”
10 Sa’ad da ya faɗa wa mahaifinsa da kuma’yan’uwansa, sai mahaifinsa ya kwaɓe shi ya ce, “Wanne irin mafarki ne haka da ka yi? Kana nufin ni da mahaifiyarka da’yan’uwanka za mu zo gabanka mu rusuna maka?”
Wathi eselitshele uyise njalo labanewabo uyise wamkhalimela wathi, “Liphupho bani leli oliphuphileyo? Utsho ukuthi unyoko lami labanewenu sizaguqa phansi emhlabathini sibili siguqela wena?”
11 ’Yan’uwansa suka yi kishinsa, amma mahaifinsa ya riƙe batun nan a zuciya.
Abanewabo babalomona ngaye, kodwa uyise wayigcina engqondweni yakhe indaba le.
12 To,’yan’uwansa suka tafi kiwon garkunan mahaifinsu kusa da Shekem.
Abanewabo basuka bahamba lemihlambi kayise emadlelweni eduze kweShekhemu.
13 Sai Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Kamar yadda ka sani,’yan’uwanka suna kiwon garkuna kusa da Shekem. Zo, in aike ka gare su.” Ya ce, “To.”
U-Israyeli wathi kuJosefa, “Njengoba usazi abanewenu basemadlelweni lemihlambi eduze kweShekhemu. Lalela-ke, ngifuna ukukuthuma kubo.” Waphendula wathi, “Kulungile.”
14 Saboda haka Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Jeka ka ga ko kome lafiya yake da’yan’uwanka da kuma garkunan, ka kawo mini labari.” Sa’an nan ya sallame shi daga Kwarin Hebron. Sa’ad da Yusuf ya kai Shekem,
Ngakho wasesithi kuye, “Hamba uyebona ingabe abafowenu bayaphila yini kanye lemihlambi, ukuze ubuye uzongazisa.” Lakanye wamvalelisa esuka esigodini saseHebhroni. UJosefa esefikile eShekhemu,
15 sai wani mutum ya same shi yana yawo a cikin jeji, sai mutumin ya tambaye shi ya ce, “Me kake nema?”
wafunyanwa yindoda ezula egangeni yambuza yathi, “Udingani?”
16 Yusuf ya amsa ya ce, “Ina neman’yan’uwana ne. Za ka iya faɗa mini inda suke kiwon garkunansu?”
Waphendula wathi, “Ngidinga abafowethu. Kambe ungangitshela ukuthi belusela ngaphi imihlambi yabo na?”
17 Mutumin ya amsa, “Sun yi gaba daga nan. Na ji su suna cewa, ‘Bari mu je Dotan.’” Saboda haka Yusuf ya bi bayan’yan’uwansa, ya kuwa same su kusa da Dotan.
Indoda yaphendula yathi, “Sebesukile lapha. Ngabezwa besithi, ‘Kasiyeni eDothani.’” Ngakho uJosefa wabalandela abafowabo wayabafumana eduze kweDothani.
18 Amma da suka gan shi daga nesa, kafin yă kai wurinsu, sai suka ƙulla su kashe shi.
Kodwa bambona esesekude, wathi engakafiki kubo, bakhanda icebo lokumbulala.
19 Suka ce wa juna, “Ga mai mafarkin nan can zuwa!
Batshelana bathi, “Nanguyana umphuphi lowana esiza.
20 Ku zo mu kashe shi mu kuma jefa shi a ɗaya daga cikin rijiyoyin nan, mu ce mugun naman jeji ya cinye shi. Mu ga yadda mafarkinsa zai cika.”
Zwanini, kasimbulaleni simphosele kwelinye lamagodi la besesisithi udliwe yisilo esesabekayo. Besesibona-ke ukuthi azaphelela ngaphi amaphupho akhe.”
21 Sa’ad da Ruben ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă cece shi daga hannuwansu. Ya ce, “Kada mu ɗauki ransa.
Kwathi uRubheni esekuzwile lokhu, wazama ukuthi amlamulele ezandleni zabo. Wathi, “Kasingacimi impilo yakhe.
22 Kada mu zub da wani jini. Mu dai jefa shi cikin wannan rijiya a nan cikin hamada, amma kada mu sa hannu a kansa.” Ruben ya faɗa wannan ne don yă cece shi daga gare su, yă kuma mai da shi ga mahaifinsa.
Lingachithi gazi. Mphoseleni emgodini lo lapha enkangala, kodwa lingambeki isandla.” URubheni watsho lokhu ukuze amlamulele kubo abesembuyisela kuyise.
23 Saboda haka sa’ad da Yusuf ya zo wurin’yan’uwansa, sai suka tuɓe masa rigarsa, rigan nan mai gwanin kyau da ya sa,
Ngakho kwathi uJosefa efika kubafowabo, bamhlubula ijazi lakhe, elalibalazwe kakuhle ayeligqokile,
24 suka kuma ɗauke shi suka jefa a cikin rijiya. To, rijiyar wofi ce, babu ruwa a ciki.
bamthatha bayamphosela emgodini. Umgodi lo wawungela lutho, kungelamanzi phakathi kwawo.
25 Da suka zauna don cin abinci, sai suka tā da idanu, suka ga ayarin mutanen Ishmayel suna zuwa daga Gileyad. An yi wa raƙumansu labtu da kayan yaji da na ƙanshi, suna kan hanyarsu za su Masar.
Bathi sebehlezi phansi ukuthi badle, bathi baphosa amehlo babona udwendwe lwama-Ishumayeli luvelela eGiliyadi. Amakamela abo ayethwaliswe iziyoliso, ibhami lemure, konke lokhu bekusa eGibhithe.
26 Yahuda ya ce wa’yan’uwansa, “Me zai amfane mu in muka kashe ɗan’uwanmu muka ɓoye jininsa?
UJuda wathi kubafowabo, “Sizazuzani nxa sibulala umfowethu sigqibele igazi lakhe na?
27 Ku zo, mu sayar da shi wa mutanen Ishmayelawan nan, kada mu sa hannuwanmu a kansa; ban da haka ma, shi ɗan’uwanmu ne, jiki da jininmu.” Sai’yan’uwansa suka yarda.
Zwanini, kasimthengiseni kuma-Ishumayeli thina singambeki sandla; kambe yena evele engumfowethu, eyinyama yethu legazi lethu.” Abafowabo bavuma.
28 Saboda haka sa’ad da Fataken Midiyawa suka iso, sai’yan’uwansa suka ja Yusuf daga rijiyar, suka sayar da shi a bakin shekel ashirin na azurfa wa mutanen Ishmayel, waɗanda suka ɗauke shi zuwa Masar.
Ngakho kwathi abathengisi bamaMidiyani besedlula abafowabo bamkhupha uJosefa emgodini bamthengisa ngamashekeli esiliva angamatshumi amabili kuma-Ishumayeli, amthatha aya laye eGibhithe.
29 Sa’ad da Ruben ya dawo wurin rijiyar, sai ya tarar cewa Yusuf ba ya can, sai ya kyakkece tufafinsa.
URubheni wathi esebuyela emgodini wafumana uJosefa engasekho, wasedabula izigqoko zakhe ngokudabuka.
30 Ya koma wurin’yan’uwansa ya ce, “Yaron ba ya can! Ina zan bi yanzu?”
Wabuyela kubafowabo wathi, “Umfana kasekho! Sengizakwenzanjani manje?”
31 Sai suka ɗauki rigar Yusuf, suka yanka akuya suka tsoma rigar a cikin jinin.
Basebethatha ijazi likaJosefa, babulala imbuzi basebegxamuza ijazi lelo egazini.
32 Suka ɗauki rigan nan mai gwanin kyau, suka kawo wa mahaifinsu suka ce, “Mun sami wannan. Ka bincika shi ka gani ko rigar ɗanka ne.”
Balithatha ijazi lokuceciswa babuyela lalo kuyise bathi, “Silidobhile. Ake ulikhangele kuhle kumbe lijazi lendodana yakho.”
33 Ya gane shi, sai ya ce, “Rigar ɗana ne! Waɗansu mugayen namun jeji sun cinye shi. Tabbatacce an yayyaga Yusuf.”
Lakanye walibona liyilo wathi, “Lijazi lendodana yami. Udliwe yisilo esesabekayo. Ngempela uJosefa usedlithizwe waba yizicucu.”
34 Sa’an nan Yaƙub ya kyakkece tufafinsa, ya sa tufafin makoki, ya kuma yi makoki domin ɗansa kwanaki masu yawa.
UJakhobe wasedabula izigqoko zakhe, wagqoka ezamasaka walilela indodana yakhe okwensuku ezinengi.
35 Dukan’ya’yansa maza da mata, suka zo don su ta’azantar da shi, amma ya ƙi yă ta’azantu. Ya ce, “A’a, cikin makoki zan gangara zuwa kabari wurin ɗana.” Saboda haka, mahaifin Yusuf ya yi kuka saboda shi. (Sheol )
Wonke amadodana akhe lamadodakazi beza ukuzamduduza, kodwa kavumanga ukududuzeka. Wathi, “Hatshi, ngizakuya ethuneni ngilila nginje, ngiye endodaneni yami.” Uyise wamkhalela kanjalo. (Sheol )
36 Ana cikin haka, Midiyawa suka sayar da Yusuf a Masar wa Fotifar, ɗaya daga cikin shugabannin’yan gadin fadar Fir’auna.
Kusenjalo, amaMidiyani amthengisa uJosefa eGibhithe kuPhothifa, omunye wezikhulu zikaFaro, owayengumlawuli wabalindi.