< Farawa 37 >

1 Yaƙub ya zauna a ƙasar da mahaifinsa ya zauna, wato, ƙasar Kan’ana.
Jacob continued to live in the Canaan region where his father had lived previously.
2 Wannan shi ne labarin zuriyar Yaƙub. Yusuf, saurayi ne mai shekara goma sha bakwai. Shi da’yan’uwansa, wato,’ya’yan Bilha maza da kuma’ya’yan Zilfa maza, matan mahaifinsa suna kiwon garkuna tare. Sai Yusuf ya kawo wa mahaifinsu rahoto marar kyau game da’yan’uwansa.
(This is/I will now tell you) what happened to Jacob’s family. When his son Joseph was 17 years old, he was taking care of the flocks of sheep and goats with some of his older brothers. They were sons of his father’s (concubines/female slaves that he had taken to be his secondary wives). Joseph sometimes told his father about bad things that his brothers were doing.
3 Isra’ila dai ya fi ƙaunar Yusuf fiye da kowanne a cikin sauran’ya’yansa maza, gama an haifa masa shi a cikin tsufansa. Sai ya yi masa riga mai gwanin kyau.
Jacob loved Joseph more than he loved any of his other children, because Joseph had been born when Jacob was an old man. Jacob made for Joseph a long pretty robe that had long sleeves.
4 Sa’ad da’yan’uwansa suka ga cewa mahaifinsu ya fi ƙaunarsa fiye da kowanne daga cikinsu, sai suka ƙi jininsa, ba sa kuma maganar alheri da shi.
When Joseph’s older brothers realized that their father loved him more than he loved any of them, they hated him. They never spoke kindly to him.
5 Sai Yusuf ya yi mafarki, sa’ad da ya faɗa wa’yan’uwansa, suka ƙara ƙin jininsa.
One night Joseph had a dream. He told his brothers about the dream.
6 Ya ce musu, “Ku saurari wannan mafarkin da na yi.
He said to them, “Listen to the dream I had!
7 Muna daurin dammunan hatsi a gona, sai nan da nan damina ya tashi ya tsaya, yayinda dammunanku suka taru kewaye da nawa suka rusuna masa.”
In the dream, we were tying up bundles of wheat in the field. Suddenly my bundle stood up straight, and surprisingly, your bundles gathered around my bundle and bowed down to it!”
8 Sai’yan’uwansa suka ce masa, “Kana nufin za ka yi mulki a kanmu ke nan? Ko kuwa za ka zama sarki, a bisanmu?” Suka ƙara ƙin jininsa saboda mafarkinsa da kuma abin da ya faɗa.
His brothers said to him, “Do you think that some day you will rule over us? Are you [saying that some day] you are going to be our king?” [RHQ] They hated him even more than before because of what he had told them about his dream.
9 Sai Yusuf ya sāke yin wani mafarki, ya faɗa wa’yan’uwansa. Ya ce, “Ku saurara, na sāke yin wani mafarki, a wannan lokaci, na ga rana da wata da taurari goma sha ɗaya suna rusuna mini.”
Later he had another dream, and again he told his older brothers about it. He said, “Listen to this! I had another dream. In this dream, the sun and moon and eleven stars were bowing down to me!”
10 Sa’ad da ya faɗa wa mahaifinsa da kuma’yan’uwansa, sai mahaifinsa ya kwaɓe shi ya ce, “Wanne irin mafarki ne haka da ka yi? Kana nufin ni da mahaifiyarka da’yan’uwanka za mu zo gabanka mu rusuna maka?”
He also told his father about it. His father rebuked him, saying “What are you suggesting by that dream [RHQ]? Do you think it means that your mother and I and your older brothers will some day bow down to the ground in front of you?” [RHQ]
11 ’Yan’uwansa suka yi kishinsa, amma mahaifinsa ya riƙe batun nan a zuciya.
Joseph’s older brothers were furious/angry with him, but his father just kept thinking about what the dream meant.
12 To,’yan’uwansa suka tafi kiwon garkunan mahaifinsu kusa da Shekem.
One day Joseph’s older brothers went to take care of their father’s sheep and goats that were eating grass near Shechem.
13 Sai Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Kamar yadda ka sani,’yan’uwanka suna kiwon garkuna kusa da Shekem. Zo, in aike ka gare su.” Ya ce, “To.”
Some time later, Jacob said to Joseph, “Your brothers are taking care of the sheep and goats near Shechem [RHQ]. I am going to send you there to see them.” Joseph replied, “Okay.”
14 Saboda haka Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Jeka ka ga ko kome lafiya yake da’yan’uwanka da kuma garkunan, ka kawo mini labari.” Sa’an nan ya sallame shi daga Kwarin Hebron. Sa’ad da Yusuf ya kai Shekem,
Jacob said, “Go and see if they are doing okay, and if the flocks are doing okay. Then come back and give me a report.” So Jacob sent Joseph from [the valley where they were living], the valley where Hebron is located, [to go north] to find his brothers. When Joseph arrived near Shechem [city],
15 sai wani mutum ya same shi yana yawo a cikin jeji, sai mutumin ya tambaye shi ya ce, “Me kake nema?”
while he was wandering around in the fields looking/searching for his brothers, a man saw him and asked him, “Whom are you looking/searching for?”
16 Yusuf ya amsa ya ce, “Ina neman’yan’uwana ne. Za ka iya faɗa mini inda suke kiwon garkunansu?”
Joseph replied, “I am looking for my older brothers. Can you tell me where they are taking care of their sheep and goats?”
17 Mutumin ya amsa, “Sun yi gaba daga nan. Na ji su suna cewa, ‘Bari mu je Dotan.’” Saboda haka Yusuf ya bi bayan’yan’uwansa, ya kuwa same su kusa da Dotan.
The man replied, “They are not here any more. I heard one of them saying, ‘Let’s take the sheep and goats and go to Dothan [town].’” So Joseph left there and went north, and found his older brothers near Dothan.
18 Amma da suka gan shi daga nesa, kafin yă kai wurinsu, sai suka ƙulla su kashe shi.
But they saw him when he was still far away, and they decided to kill him.
19 Suka ce wa juna, “Ga mai mafarkin nan can zuwa!
They said to each other [things like], “Here comes that dreamer!”
20 Ku zo mu kashe shi mu kuma jefa shi a ɗaya daga cikin rijiyoyin nan, mu ce mugun naman jeji ya cinye shi. Mu ga yadda mafarkinsa zai cika.”
and “Hey, let’s kill him, and then throw his body into one of the pits/cisterns. Then we will tell people that a ferocious/wild animal attacked and killed him and ate him. And then we will (find out whether his dreams come true/make sure that his dreams do not come true)!”
21 Sa’ad da Ruben ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă cece shi daga hannuwansu. Ya ce, “Kada mu ɗauki ransa.
Reuben heard what they were saying, so he tried to persuade them not to kill [MTY] Joseph. He said, “No, we should not kill him.
22 Kada mu zub da wani jini. Mu dai jefa shi cikin wannan rijiya a nan cikin hamada, amma kada mu sa hannu a kansa.” Ruben ya faɗa wannan ne don yă cece shi daga gare su, yă kuma mai da shi ga mahaifinsa.
Do not even shed his blood! We can throw him into this pit/cistern in the desert, but we should not harm him [MTY].” He said that, and then left them, planning to rescue Joseph later and take him back to his father.
23 Saboda haka sa’ad da Yusuf ya zo wurin’yan’uwansa, sai suka tuɓe masa rigarsa, rigan nan mai gwanin kyau da ya sa,
So when Joseph arrived where his older brothers were, they seized him and ripped off his pretty robe with long sleeves.
24 suka kuma ɗauke shi suka jefa a cikin rijiya. To, rijiyar wofi ce, babu ruwa a ciki.
Then they took him and threw him into the pit/cistern. But the pit/cistern was dry; there was no water in it.
25 Da suka zauna don cin abinci, sai suka tā da idanu, suka ga ayarin mutanen Ishmayel suna zuwa daga Gileyad. An yi wa raƙumansu labtu da kayan yaji da na ƙanshi, suna kan hanyarsu za su Masar.
After they sat down to eat some food, they looked up and saw a (caravan/group [of traders]), descendants of Ishmael, coming from the Gilead area. Their camels were loaded with bags of spices and nice-smelling resins. They were going down to Egypt to sell those things there.
26 Yahuda ya ce wa’yan’uwansa, “Me zai amfane mu in muka kashe ɗan’uwanmu muka ɓoye jininsa?
Judah said to his [older and younger] brothers, “If we kill our younger brother and hide his body, (what will we gain?/we will not gain anything!) [RHQ]
27 Ku zo, mu sayar da shi wa mutanen Ishmayelawan nan, kada mu sa hannuwanmu a kansa; ban da haka ma, shi ɗan’uwanmu ne, jiki da jininmu.” Sai’yan’uwansa suka yarda.
So, instead of harming him, let’s sell him to these men who are descendants of Ishmael. Don’t forget, he is our own younger brother!” So they all agreed to do that.
28 Saboda haka sa’ad da Fataken Midiyawa suka iso, sai’yan’uwansa suka ja Yusuf daga rijiyar, suka sayar da shi a bakin shekel ashirin na azurfa wa mutanen Ishmayel, waɗanda suka ɗauke shi zuwa Masar.
When those traders from the Midian area came near, Joseph’s brothers pulled him up out of the pit/cistern. Then they sold him to the men from Midian for 20 pieces of silver. The traders then took Joseph to Egypt.
29 Sa’ad da Ruben ya dawo wurin rijiyar, sai ya tarar cewa Yusuf ba ya can, sai ya kyakkece tufafinsa.
When Reuben returned to the pit/cistern, he saw that his younger brother was not there. He was so grieved that he tore his clothes.
30 Ya koma wurin’yan’uwansa ya ce, “Yaron ba ya can! Ina zan bi yanzu?”
He went back to his [younger] brothers and said, “The boy is not in the pit/cistern! What can I do now?” [RHQ]
31 Sai suka ɗauki rigar Yusuf, suka yanka akuya suka tsoma rigar a cikin jinin.
[Joseph’s brothers did not dare to tell their father what they had done. So, they decided to invent a story about what had happened]. They got Joseph’s robe. Then they killed a goat and dipped the robe in the goat’s blood.
32 Suka ɗauki rigan nan mai gwanin kyau, suka kawo wa mahaifinsu suka ce, “Mun sami wannan. Ka bincika shi ka gani ko rigar ɗanka ne.”
They took that pretty robe back to their father and said, “We found this robe! Look at it. Is it your son’s robe?”
33 Ya gane shi, sai ya ce, “Rigar ɗana ne! Waɗansu mugayen namun jeji sun cinye shi. Tabbatacce an yayyaga Yusuf.”
He recognized it, and he said, “Yes, it is my son’s robe! Some ferocious/wild animal must have attacked and killed him! I am sure that the animal has torn Joseph to pieces!”
34 Sa’an nan Yaƙub ya kyakkece tufafinsa, ya sa tufafin makoki, ya kuma yi makoki domin ɗansa kwanaki masu yawa.
Jacob was so grieved that he tore his clothes. He put on (sackcloth/clothes that people wear when they are mourning for someone who has died). He mourned/cried for his son for many days.
35 Dukan’ya’yansa maza da mata, suka zo don su ta’azantar da shi, amma ya ƙi yă ta’azantu. Ya ce, “A’a, cikin makoki zan gangara zuwa kabari wurin ɗana.” Saboda haka, mahaifin Yusuf ya yi kuka saboda shi. (Sheol h7585)
All of his children came to try to comfort him, but he did not pay attention to what they said. He said, “No, I will still be mourning/crying when I die and go to be with my son.” So Joseph’s father continued to cry because of what had happened to his son. (Sheol h7585)
36 Ana cikin haka, Midiyawa suka sayar da Yusuf a Masar wa Fotifar, ɗaya daga cikin shugabannin’yan gadin fadar Fir’auna.
In the meantime, the men/traders from Midian took Joseph to Egypt and sold him to Potiphar, who was one of the king’s officials. He was the captain of the soldiers who protected the king.

< Farawa 37 >