< Farawa 37 >

1 Yaƙub ya zauna a ƙasar da mahaifinsa ya zauna, wato, ƙasar Kan’ana.
And Jacob dwelt in the land of his father's sojourning, in the land of Canaan.
2 Wannan shi ne labarin zuriyar Yaƙub. Yusuf, saurayi ne mai shekara goma sha bakwai. Shi da’yan’uwansa, wato,’ya’yan Bilha maza da kuma’ya’yan Zilfa maza, matan mahaifinsa suna kiwon garkuna tare. Sai Yusuf ya kawo wa mahaifinsu rahoto marar kyau game da’yan’uwansa.
These are the generations of Jacob. Joseph, being seventeen years old, was feeding the flock with his brothers; and he was as a lad with the sons of Bilhah, and with the sons of Zilpah, his father's wives; and Joseph brought evil reports of them unto his father.
3 Isra’ila dai ya fi ƙaunar Yusuf fiye da kowanne a cikin sauran’ya’yansa maza, gama an haifa masa shi a cikin tsufansa. Sai ya yi masa riga mai gwanin kyau.
Now Israel loved Joseph more than all his children, because he was the son of his old age; and he made him a coat of many colors.
4 Sa’ad da’yan’uwansa suka ga cewa mahaifinsu ya fi ƙaunarsa fiye da kowanne daga cikinsu, sai suka ƙi jininsa, ba sa kuma maganar alheri da shi.
And when his brothers saw that their father loved him more than all his brothers, they hated him, and could not speak peaceably unto him.
5 Sai Yusuf ya yi mafarki, sa’ad da ya faɗa wa’yan’uwansa, suka ƙara ƙin jininsa.
And Joseph dreamed a dream, and he told it to his brothers: and they hated him yet the more.
6 Ya ce musu, “Ku saurari wannan mafarkin da na yi.
And he said unto them, Hear, I pray you, this dream which I have dreamed.
7 Muna daurin dammunan hatsi a gona, sai nan da nan damina ya tashi ya tsaya, yayinda dammunanku suka taru kewaye da nawa suka rusuna masa.”
And, behold, we were binding sheaves in the field, and, lo, my sheaf arose, and also remained standing upright; and, behold, your sheaves placed themselves round about, and made obeisance to my sheaf.
8 Sai’yan’uwansa suka ce masa, “Kana nufin za ka yi mulki a kanmu ke nan? Ko kuwa za ka zama sarki, a bisanmu?” Suka ƙara ƙin jininsa saboda mafarkinsa da kuma abin da ya faɗa.
And his brothers said to him, Shalt thou indeed reign over us? or shalt thou indeed have dominion over us? And they hated him yet the more for his dreams, and for his words.
9 Sai Yusuf ya sāke yin wani mafarki, ya faɗa wa’yan’uwansa. Ya ce, “Ku saurara, na sāke yin wani mafarki, a wannan lokaci, na ga rana da wata da taurari goma sha ɗaya suna rusuna mini.”
And he dreamed yet another dream, and told it to his brothers; and he said, Behold, I have dreamed a dream more; and, behold, the sun and the moon and eleven stars made obeisance to me.
10 Sa’ad da ya faɗa wa mahaifinsa da kuma’yan’uwansa, sai mahaifinsa ya kwaɓe shi ya ce, “Wanne irin mafarki ne haka da ka yi? Kana nufin ni da mahaifiyarka da’yan’uwanka za mu zo gabanka mu rusuna maka?”
And he told it to his father, and to his brothers; and his father rebuked him, and said unto him, What is this dream that thou hast dreamed? Shall we indeed come, I and thy mother, and thy brothers, to bow down ourselves to thee to the earth.
11 ’Yan’uwansa suka yi kishinsa, amma mahaifinsa ya riƙe batun nan a zuciya.
And his brothers envied him; but his father noted the matter [in his mind].
12 To,’yan’uwansa suka tafi kiwon garkunan mahaifinsu kusa da Shekem.
And his brothers went to feed their father's flocks in Shechem.
13 Sai Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Kamar yadda ka sani,’yan’uwanka suna kiwon garkuna kusa da Shekem. Zo, in aike ka gare su.” Ya ce, “To.”
And Israel said unto Joseph, Do not thy brothers feed [the flocks] in Shechem? come, and I will send thee unto them. And he said to him, Here am I.
14 Saboda haka Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Jeka ka ga ko kome lafiya yake da’yan’uwanka da kuma garkunan, ka kawo mini labari.” Sa’an nan ya sallame shi daga Kwarin Hebron. Sa’ad da Yusuf ya kai Shekem,
And he said to him, Go, I pray thee, see whether it be well with thy brothers, and well with the flocks; and bring me word again. So he sent him from the vale of Hebron, and he came to Shechem.
15 sai wani mutum ya same shi yana yawo a cikin jeji, sai mutumin ya tambaye shi ya ce, “Me kake nema?”
And a certain man found him, and, behold, he was wandering astray in the field; and the man asked him, saying, What seekest thou?
16 Yusuf ya amsa ya ce, “Ina neman’yan’uwana ne. Za ka iya faɗa mini inda suke kiwon garkunansu?”
And he said, I seek my brothers; tell me, I pray thee, where they are feeding their flocks?
17 Mutumin ya amsa, “Sun yi gaba daga nan. Na ji su suna cewa, ‘Bari mu je Dotan.’” Saboda haka Yusuf ya bi bayan’yan’uwansa, ya kuwa same su kusa da Dotan.
And the man said, They are departed hence; for I heard them say, Let us go to Dothan. And Joseph went after his brothers, and found them in Dothan.
18 Amma da suka gan shi daga nesa, kafin yă kai wurinsu, sai suka ƙulla su kashe shi.
And when they saw him afar off, even before he came near unto them, they conspired against him to slay him.
19 Suka ce wa juna, “Ga mai mafarkin nan can zuwa!
And they said one to another, Behold, here comes this man of dreams.
20 Ku zo mu kashe shi mu kuma jefa shi a ɗaya daga cikin rijiyoyin nan, mu ce mugun naman jeji ya cinye shi. Mu ga yadda mafarkinsa zai cika.”
And now, come and let us slay him, and cast him into one of the pits, and we will say, Some evil beast hath devoured him: and we shall see what will become of his dreams.
21 Sa’ad da Ruben ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă cece shi daga hannuwansu. Ya ce, “Kada mu ɗauki ransa.
And when Reuben heard it, he delivered him out of their hand; and he said, Let us not put him to death.
22 Kada mu zub da wani jini. Mu dai jefa shi cikin wannan rijiya a nan cikin hamada, amma kada mu sa hannu a kansa.” Ruben ya faɗa wannan ne don yă cece shi daga gare su, yă kuma mai da shi ga mahaifinsa.
And Reuben said unto them, Do not shed blood; but cast him into this pit that is in the wilderness, but do not lay hand upon him; —in order that he might deliver him out of their hand, to bring him back again to his father.
23 Saboda haka sa’ad da Yusuf ya zo wurin’yan’uwansa, sai suka tuɓe masa rigarsa, rigan nan mai gwanin kyau da ya sa,
And it came to pass, when Joseph was come unto his brothers, that they stript Joseph of his coat, the coat of many colors that was on him;
24 suka kuma ɗauke shi suka jefa a cikin rijiya. To, rijiyar wofi ce, babu ruwa a ciki.
And they took him, and cast him into the pit; and the pit was empty; there was no water in it.
25 Da suka zauna don cin abinci, sai suka tā da idanu, suka ga ayarin mutanen Ishmayel suna zuwa daga Gileyad. An yi wa raƙumansu labtu da kayan yaji da na ƙanshi, suna kan hanyarsu za su Masar.
And they sat down to eat bread: and they lifted up their eyes and looked, and, behold, a company of Ishmaelites was coming from Gilead; and their camels were bearing spicery, and balm, and lotus, going to carry it down to Egypt.
26 Yahuda ya ce wa’yan’uwansa, “Me zai amfane mu in muka kashe ɗan’uwanmu muka ɓoye jininsa?
And Judah said unto his brothers, What profit will it be if we slay our brother, and conceal his blood?
27 Ku zo, mu sayar da shi wa mutanen Ishmayelawan nan, kada mu sa hannuwanmu a kansa; ban da haka ma, shi ɗan’uwanmu ne, jiki da jininmu.” Sai’yan’uwansa suka yarda.
Come, and let us sell him to the Ishmaelites, but let our hand not be upon him; for he is our brother, our flesh. And his brothers hearkened to him.
28 Saboda haka sa’ad da Fataken Midiyawa suka iso, sai’yan’uwansa suka ja Yusuf daga rijiyar, suka sayar da shi a bakin shekel ashirin na azurfa wa mutanen Ishmayel, waɗanda suka ɗauke shi zuwa Masar.
And when the Midianitish men, merchants, passed by, they drew and lifted up Joseph out of the pit, and sold Joseph to the Ishmaelites for twenty pieces of silver: and they brought Joseph into Egypt.
29 Sa’ad da Ruben ya dawo wurin rijiyar, sai ya tarar cewa Yusuf ba ya can, sai ya kyakkece tufafinsa.
And when Reuben returned unto the pit, and, behold, Joseph was not in the pit, he rent his clothes.
30 Ya koma wurin’yan’uwansa ya ce, “Yaron ba ya can! Ina zan bi yanzu?”
And he returned unto his brothers, and said, The child is not there; and I, whither shall I go?
31 Sai suka ɗauki rigar Yusuf, suka yanka akuya suka tsoma rigar a cikin jinin.
And they took Joseph's coat, and killed a he-goat, and dipped the coat in the blood;
32 Suka ɗauki rigan nan mai gwanin kyau, suka kawo wa mahaifinsu suka ce, “Mun sami wannan. Ka bincika shi ka gani ko rigar ɗanka ne.”
And they sent the coat of many colors, and they brought it to their father, and said, This have we found: acknowledge, we pray thee, whether it be thy son's coat or not.
33 Ya gane shi, sai ya ce, “Rigar ɗana ne! Waɗansu mugayen namun jeji sun cinye shi. Tabbatacce an yayyaga Yusuf.”
And he recognized it, and said, it is my son's coat; an evil beast hath devoured him; Joseph is surely torn in pieces.
34 Sa’an nan Yaƙub ya kyakkece tufafinsa, ya sa tufafin makoki, ya kuma yi makoki domin ɗansa kwanaki masu yawa.
And Jacob rent his clothes, and put sackcloth upon his loins, and mourned for his son many days.
35 Dukan’ya’yansa maza da mata, suka zo don su ta’azantar da shi, amma ya ƙi yă ta’azantu. Ya ce, “A’a, cikin makoki zan gangara zuwa kabari wurin ɗana.” Saboda haka, mahaifin Yusuf ya yi kuka saboda shi. (Sheol h7585)
And all his sons and all his daughters rose up to comfort him; but he refused to be comforted; and he said, For I must go down unto my son, mourning, into the grave; thus his father wept for him. (Sheol h7585)
36 Ana cikin haka, Midiyawa suka sayar da Yusuf a Masar wa Fotifar, ɗaya daga cikin shugabannin’yan gadin fadar Fir’auna.
And the Midianites sold him into Egypt unto Potiphar, an officer of Pharaoh's, the captain of the guards.

< Farawa 37 >