< Farawa 36 >

1 Waɗannan su ne zuriyar Isuwa (wato, Edom).
Voici les générations d’Esaü; c’est le même qu’Edom.
2 Isuwa ya ɗauko matansa daga cikin matan Kan’ana, ya ɗauko Ada’yar Elon mutumin Hitti, da Oholibama’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon Bahiwiye
Esaü prit pour femmes d’entre les filles des Chananéens: Ada, fille d’Elon l’Hétéen, et Oolibama, fille d’Ana, fille elle-même de Sébéon l’Hévéen;
3 ya kuma auri Basemat’yar Ishmayel wadda take’yar’uwar Nebayiwot.
Et aussi Bazemath, fille d’Ismaël, sœur de Nabaïoth.
4 Ada ta haifi wa Isuwa, Elifaz. Basemat kuma ta haifa masa Reyuwel.
Ada enfanta Eliphaz; Bazemath enfanta Rahuel;
5 Oholibama kuwa ta haifa masa Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza, waɗanda aka haifa masa a Kan’ana.
Oolibama enfanta Jéhus, Ihélon et Coré. Ce sont là les fils d’Esaü, qui lui naquirent dans la terre de Chanaan.
6 Isuwa ya ɗauki matansa da’ya’yansa maza da mata da kuma dukan membobin gidansa, ya kuma ɗauki shanunsa da dukan sauran dabbobinsa, da dukan dukiyarsa da ya samu a ƙasar Kan’ana zuwa wata ƙasa nesa da ɗan’uwansa Yaƙub.
Or Esaü prit ses femmes, ses fils, ses filles et toutes les âmes de sa maison, ses richesses, ses bestiaux et tout ce qu’il pouvait avoir dans la terre de Chanaan, et il s’en alla dans une autre contrée, et s’éloigna de son frère Jacob.
7 Mallakarsu ta yi yawa ƙwarai da ba za su iya zauna tare ba; gama ƙasar da suke zaune a ciki ba za tă ishe su su biyu ba saboda dabbobinsu.
Car ils étaient extrêmement riches, et ils ne pouvaient habiter ensemble; et la terre de leur pèlerinage ne leur suffisait pas, à cause de la multitude de leurs troupeaux.
8 Saboda haka Isuwa (wato, Edom) ya zauna a ƙasar tuddai na Seyir.
Ainsi Esaü habita sur la montagne de Séir: Esaü est le même qu’Edom.
9 Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom, a ƙasar tuddai na Seyir.
Or, voici les générations d’Esaü père des Iduméens sur la montagne de Séir;
10 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isuwa maza, Elifaz, ɗan Ada matar Isuwa, da Reyuwel ɗan Basemat matar Isuwa.
Et voici les noms de ses fils: Eliphaz, fils d’Ada, femme d’Esaü, Rahuel aussi, fils de Bazemath sa femme.
11 ’Ya’yan Elifaz maza su ne, Teman, Omar, Zefo, Gatam da Kenaz.
Et les fils d’Eliphaz furent Théman, Omar, Sépho, Gatham et Cénez.
12 Elifaz ɗan Isuwa kuma yana da ƙwarƙwara mai suna Timna, wadda ta haifa masa Amalek. Waɗannan su ne jikokin Ada matar Isuwa.
Il y avait encore Thamna, seconde femme d’Eliphaz, fils d’Esaü, laquelle lui enfanta Amalech: ce sont là les fils d’Ada, femme d’Esaü;
13 ’Ya’yan Reyuwel maza su ne, Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
Mais les fils de Rahuel: Nathat et Zara, Samma et Meza: ce sont là les fils de Bazemath, femme d’Esaü.
14 ’Ya’yan Oholibama maza’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon, matar Isuwa, waɗanda ta haifa wa Isuwa su ne, Yewush, Yalam da Kora.
Il y avait aussi les fils d’Oolibama (fille d’Ana, fille elle-même de Sébéon), femme d’Esaü, qu’elle lui enfanta: Jéhus, Ihélon et Coré.
15 Waɗannan su ne manya a cikin zuriyar Isuwa,’Ya’ya Elifaz maza ɗan farin Isuwa, Shugabannin su ne; Teman, Omar, Zefo, Kenaz,
Voici les chefs des fils d’Esaü: les fils d’Eliphaz, premier-né d’Esaü: le chef Théman, le chef Omar, le chef Sépho, le chef Cénez,
16 Kora, Gatam da kuma Amalek. Waɗannan ne manya da suka fito daga dangin Elifaz a Edom; su ne jikokin Ada.
Le chef Coré, le chef Gatham, le chef Amalech. Ce sont là les fils d’Eliphaz, dans le pays d’Edom, et ce sont les fils d’Ada.
17 ’Ya’yan Reyuwel maza, Shugabannin su ne; Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Reyuwel a Edom; su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
Et voici les fils de Rahuel fils d’Esaü: le chef Nahath, le chef Zara, le chef Samma, le chef Meza: ce sont là les chefs issus de Rahuel dans le pays d’Edom; et ce sont les fils de Bazemath, femme d’Esaü.
18 ’Ya’yan Oholibama maza matar Isuwa, Shugabannin su ne; Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Oholibama’yar Ana matar Isuwa.
Mais voici les fils d’Oolibama, femme d’Esaü: le chef Jéhus, le chef Ihélon, le chef Coré: ce sont là les chefs issus d’Oolibama, femme d’Esaü, fille d’Ana.
19 Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza (wato, Edom), waɗannan ne manyansu.
Ce sont là les enfants d’Esaü, et ce sont là leurs chefs: Esaü est le même qu’Edom.
20 Waɗannan su ne’ya’yan Seyir Bahore maza, waɗanda suke zaune a yankin, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
Voici les fils de Séir Horréen, habitants de ce pays: Lotan, Sobal, Sébéon, Ana,
21 Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa,’ya’yan Seyir, maza, a ƙasar Edom.
Dison, Eser et Disan: ce sont là les chefs Horréens, fils de Séir, dans le pays d’Edom.
22 ’Ya’yan Lotan maza su ne, Hori da Homam. Timna’yar’uwar Lotan ce.
Mais les fils de Lotan furent Hori et Héman: or, la sœur de Lotan était Thamna.
23 ’Ya’yan Shobal maza su ne, Alwan, Manahat, Ebal, Shefo da Onam.
Voici les fils de Sobal: Alvan, Manahat, Ebal, Sépho et Onam.
24 ’Ya’yan Zibeyon maza su ne, Aiya da Ana. Wannan shi ne Ana wanda ya sami maɓulɓulan ruwan zafi a hamada yayinda yake kiwon jakuna na mahaifinsa Zibeyon.
Et voici les fils de Sébéon: Aïa et Ana. Celui-ci est Ana, qui trouva les eaux chaudes dans le désert, pendant qu’il paissait les ânes de Sébéon son père;
25 ’Ya’yan Ana su ne, Dishon da Oholibama’yar Ana.
Il eut pour fils Dison, et pour fille Oolibama.
26 ’Ya’yan Dishon maza su ne, Hemdan, Eshban, Itran da Keran.
Or, voici les fils de Dison: Hamdan, Eséban, Jéthram et Charan;
27 ’Ya’yan Ezer maza su ne, Bilhan, Za’aban da Akan.
Et les fils d’Eser: Balaan, Zavan et Achan.
28 ’Ya’yan Dishan maza su ne, Uz da Aran.
Mais Disan eut pour fils Hus et Aram.
29 Waɗannan su ne manyan Horiyawa, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
Voici les chefs des Horréens: le chef Lotan, le chef Sobal, le chef Sébéon, le chef Ana,
30 Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa, bisa ga ɓangarorinsu, a ƙasar Seyir.
Le chef Dison, le chef Eser et le chef Disan: ce sont là les chefs qui ont commandé dans le pays de Séir.
31 Waɗannan su ne sarakunan da suka yi mulki a Edom kafin wani sarki mutumin Isra’ila yă yi mulki,
Mais les rois qui régnèrent dans le pays d’Edom, avant que les enfants d’Israël eussent un roi, furent ceux-ci:
32 Bela ɗan Beyor ya zama sarkin Edom. Sunan birninsa shi ne Dinhaba.
Béla, fils de Béor, et le nom de sa ville était Denaba.
33 Sa’ad da Bela ya rasu, Yobab ɗan Zera daga Bozra ya gāje shi.
Mais Béla mourut, et à sa place régna Jobab, fils de Zara de Bosra.
34 Sa’ad da Yobab ya rasu, Husham daga ƙasar Temaniyawa ya gāje shi.
Et quand Jobab mourut, à sa place régna Husam du pays des Thémanites.
35 Sa’ad da Husham ya rasu, Hadad ɗan Bedad, wanda ya ci Midiyan da yaƙi a ƙasar Mowab, ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Awit.
Celui-ci mort aussi, régna à sa place Adad, fils de Badad, qui battit Madian dans les champs de Moab; et le nom de sa ville était Avith.
36 Sa’ad da Hadad ya rasu, Samla daga Masreka ya gāje shi.
Et quand Adad mourut, régna à sa place Semla de Masréca.
37 Sa’ad da Samla ya rasu, Sha’ul daga Rehobot na ta kogi ya gāje shi.
Celui-ci mort aussi, régna à sa place Saül, du fleuve de Rohoboth.
38 Sa’ad da Sha’ul ya rasu, Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya gāje shi.
Et quand celui-ci mourut, Balanan, fils d’Achobor, succéda au royaume.
39 Sa’ad da Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya rasu, Hadad ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Fau, kuma sunan matarsa Mehetabel ce’yar Matired, jikanyar Me-Zahab.
Celui-ci mort aussi, régna à sa place Adar; et le nom de sa ville était Phaü; et sa femme s’appelait Méétabel, fille de Matred, fille elle-même de Mézaab.
40 Waɗannan su ne manya da suka fito daga zuriyar Isuwa, bisa ga danginsu, bisa kuma ga kabilansu da yankunansu. Sunayensu su ne, Timna, Alwa, Yetet.
Voici donc les noms des chefs issus d’Esaü, selon leurs familles et leurs demeures et leurs noms: le chef Thamna, le chef Alva, le chef Jétheth,
41 Oholibama, Ela, Finon.
Le chef Oolibama, le chef Ela, le chef Phinon,
42 Kenaz, Teman, Mibzar.
Le chef Cénez, le chef Théman, le chef Mabsar,
43 Magdiyel da Iram. Waɗannan su ne manyan Edom bisa ga mazauninsu cikin ƙasar da suka zauna. Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom.
Le chef Magdiel, le chef Hiram: ce sont là les chefs issus d’Edom, qui habitaient dans le pays de leur domination: Edom est le même qu’Esaü père des Iduméens.

< Farawa 36 >