< Farawa 36 >

1 Waɗannan su ne zuriyar Isuwa (wato, Edom).
Or ce sont ici les générations d'Esaü, qui [est] Edom.
2 Isuwa ya ɗauko matansa daga cikin matan Kan’ana, ya ɗauko Ada’yar Elon mutumin Hitti, da Oholibama’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon Bahiwiye
Esaü prit ses femmes d'entre les filles de Canaan: savoir Hada fille d'Elon Héthien, et Aholibama fille de Hana, [petite-]fille de Tsibhon Hévien.
3 ya kuma auri Basemat’yar Ishmayel wadda take’yar’uwar Nebayiwot.
Il prit aussi Basmath fille d'Ismaël, sœur de Nébajoth.
4 Ada ta haifi wa Isuwa, Elifaz. Basemat kuma ta haifa masa Reyuwel.
Et Hada enfanta à Esaü Eliphaz; et Basmath enfanta Réhuel.
5 Oholibama kuwa ta haifa masa Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza, waɗanda aka haifa masa a Kan’ana.
Et Aholibama enfanta Jéhus, et Jahlam, et Korah. Ce sont là les enfants d'Esaü, qui lui naquirent au pays de Canaan.
6 Isuwa ya ɗauki matansa da’ya’yansa maza da mata da kuma dukan membobin gidansa, ya kuma ɗauki shanunsa da dukan sauran dabbobinsa, da dukan dukiyarsa da ya samu a ƙasar Kan’ana zuwa wata ƙasa nesa da ɗan’uwansa Yaƙub.
Et Esaü prit ses femmes et ses fils, et ses filles, et toutes les personnes de sa maison, tous ses troupeaux, et ses bêtes, et tout le bien qu'il avait acquis au pays de Canaan, et il s'en alla en un autre pays, loin de Jacob son frère.
7 Mallakarsu ta yi yawa ƙwarai da ba za su iya zauna tare ba; gama ƙasar da suke zaune a ciki ba za tă ishe su su biyu ba saboda dabbobinsu.
Car leurs biens étaient si grands, qu'ils n'auraient pas pu demeurer ensemble; et le pays où ils demeuraient comme étrangers, ne les eût pas pu contenir à cause de leurs troupeaux.
8 Saboda haka Isuwa (wato, Edom) ya zauna a ƙasar tuddai na Seyir.
Ainsi Esaü habita en la montagne de Séhir; Esaü est Edom.
9 Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom, a ƙasar tuddai na Seyir.
Et ce sont ici les générations d'Esaü, père d'Edom, en la montagne de Séhir.
10 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isuwa maza, Elifaz, ɗan Ada matar Isuwa, da Reyuwel ɗan Basemat matar Isuwa.
Ce sont ici les noms des enfants d'Esaü: Eliphaz fils de Hada, femme d'Esaü; Réhuel fils de Basmath, femme d'Esaü.
11 ’Ya’yan Elifaz maza su ne, Teman, Omar, Zefo, Gatam da Kenaz.
Et les enfants d'Eliphaz, furent Téman, Omar, Tsépho, Gahtam et Kénaz.
12 Elifaz ɗan Isuwa kuma yana da ƙwarƙwara mai suna Timna, wadda ta haifa masa Amalek. Waɗannan su ne jikokin Ada matar Isuwa.
Et Timnaph fut concubine d'Eliphaz, fils d'Esaü, et elle enfanta Hamalec à Eliphaz. Ce sont là les enfants de Hada femme d'Esaü.
13 ’Ya’yan Reyuwel maza su ne, Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
Et ce sont ici les enfants de Réhuel: Nahath, Zérah, Samma, et Miza. Ceux-ci furent enfants de Basmath femme d'Esaü.
14 ’Ya’yan Oholibama maza’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon, matar Isuwa, waɗanda ta haifa wa Isuwa su ne, Yewush, Yalam da Kora.
Et ceux-ci furent les enfants d'Aholibama, fille de Hana, [petite-]fille de Tsibhon, et femme d'Esaü, qui enfanta à Esaü Jéhus, Jahlam, et Korah.
15 Waɗannan su ne manya a cikin zuriyar Isuwa,’Ya’ya Elifaz maza ɗan farin Isuwa, Shugabannin su ne; Teman, Omar, Zefo, Kenaz,
Ce sont ici les Ducs des enfants d'Esaü. Des enfants d'Eliphaz premier-né d'Esaü, le Duc Téman, le Duc Omar, le Duc Tsépho, le Duc Kénaz,
16 Kora, Gatam da kuma Amalek. Waɗannan ne manya da suka fito daga dangin Elifaz a Edom; su ne jikokin Ada.
Le Duc Korah, le Duc Gahtam, le Duc Hamalec. Ce sont là les Ducs d'Eliphaz au pays d'Edom, qui furent enfants de Hada.
17 ’Ya’yan Reyuwel maza, Shugabannin su ne; Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Reyuwel a Edom; su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
Et ce sont ici ceux des enfants de Réhuel fils d'Esaü: le Duc Nahath, le Duc Zérah, le Duc Samma, et le Duc Miza. Ce sont là les Ducs [sortis] de Réhuel au pays d'Edom, qui furent enfants de Basmath femme d'Esaü.
18 ’Ya’yan Oholibama maza matar Isuwa, Shugabannin su ne; Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Oholibama’yar Ana matar Isuwa.
Et ce sont ici ceux des enfants d'Aholibama femme d'Esaü: le Duc Jéhus, le Duc Jahlam, le Duc Korah; qui sont les Ducs [sortis] d'Aholibama fille de Hana, femme d'Esaü.
19 Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza (wato, Edom), waɗannan ne manyansu.
Ce sont là les enfants d'Esaü, qui est Edom, et ce [sont] là leurs Ducs.
20 Waɗannan su ne’ya’yan Seyir Bahore maza, waɗanda suke zaune a yankin, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
Ce sont ici les enfants de Séhir Horien, qui avaient habité au pays, Lotan, Sobal, Tsibhon, et Hana.
21 Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa,’ya’yan Seyir, maza, a ƙasar Edom.
Dison, Etser, et Disan; qui sont les Ducs des Horiens, enfants de Séhir au pays d'Edom.
22 ’Ya’yan Lotan maza su ne, Hori da Homam. Timna’yar’uwar Lotan ce.
Et les enfants de Lotan, furent Hori et Héman; et Timnah était sœur de Lotan.
23 ’Ya’yan Shobal maza su ne, Alwan, Manahat, Ebal, Shefo da Onam.
Et ce sont ici les enfants de Sobal: Halvan, Manahath, Hébal, Sépho, et Onam.
24 ’Ya’yan Zibeyon maza su ne, Aiya da Ana. Wannan shi ne Ana wanda ya sami maɓulɓulan ruwan zafi a hamada yayinda yake kiwon jakuna na mahaifinsa Zibeyon.
Et ce sont ici les enfants de Tsibhon: Aja et Hana. Cet Hana est celui qui trouva les mulets au désert, quand il paissait les ânes de Tsibhon son père.
25 ’Ya’yan Ana su ne, Dishon da Oholibama’yar Ana.
Et ce sont ici les enfants de Hana: Disan, et Aholibama fille de Hana.
26 ’Ya’yan Dishon maza su ne, Hemdan, Eshban, Itran da Keran.
Et ce sont ici les enfants de Disan: Hemdan, Esban, Jithran, et Kéran.
27 ’Ya’yan Ezer maza su ne, Bilhan, Za’aban da Akan.
Et ce sont ici les enfants d'Etser: Bilhan, Zahavan, et Hakan.
28 ’Ya’yan Dishan maza su ne, Uz da Aran.
Et ce sont ici les enfants de Disan: Huts et Aran.
29 Waɗannan su ne manyan Horiyawa, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
Ce sont ici les Ducs des Horiens: le Duc Lotan, le Duc Sobal, le Duc Tsibhon, le Duc Hana.
30 Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa, bisa ga ɓangarorinsu, a ƙasar Seyir.
Le Duc Dison, le Duc Etser, le Duc Disan. Ce sont là les Ducs des Horiens, selon que leurs Ducs étaient [établis] au pays de Séhir.
31 Waɗannan su ne sarakunan da suka yi mulki a Edom kafin wani sarki mutumin Isra’ila yă yi mulki,
Et ce sont ici les Rois qui ont régné au pays d'Edom, avant qu'aucun Roi régnât sur les enfants d'Israël.
32 Bela ɗan Beyor ya zama sarkin Edom. Sunan birninsa shi ne Dinhaba.
Bélah, fils de Béhor, régna en Edom, et le nom de sa ville était Dinhaba.
33 Sa’ad da Bela ya rasu, Yobab ɗan Zera daga Bozra ya gāje shi.
Et Bélah mourut, et Jobab fils de Zérah de Botsra, régna en sa place.
34 Sa’ad da Yobab ya rasu, Husham daga ƙasar Temaniyawa ya gāje shi.
Et Jobab mourut, et Husam du pays des Témanites, régna en sa place.
35 Sa’ad da Husham ya rasu, Hadad ɗan Bedad, wanda ya ci Midiyan da yaƙi a ƙasar Mowab, ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Awit.
Et Husam mourut, et Hadad fils de Bédad régna en sa place, qui défit Madian au territoire de Moab; et le nom de sa ville était Havith.
36 Sa’ad da Hadad ya rasu, Samla daga Masreka ya gāje shi.
Et Hadad mourut, et Samla de Masréka régna en sa place.
37 Sa’ad da Samla ya rasu, Sha’ul daga Rehobot na ta kogi ya gāje shi.
Et Samla mourut, et Saül de Réhoboth du fleuve, régna en sa place.
38 Sa’ad da Sha’ul ya rasu, Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya gāje shi.
Et Saül mourut, et Bahal-hanan fils de Hacbor régna en sa place.
39 Sa’ad da Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya rasu, Hadad ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Fau, kuma sunan matarsa Mehetabel ce’yar Matired, jikanyar Me-Zahab.
Et Bahal-hanan fils de Hacbor mourut, et Hadar régna en sa place; et le nom de sa ville [était] Pahu; et le nom de sa femme Méhétabéel, fille de Matred, [petite-]fille de Mézahab.
40 Waɗannan su ne manya da suka fito daga zuriyar Isuwa, bisa ga danginsu, bisa kuma ga kabilansu da yankunansu. Sunayensu su ne, Timna, Alwa, Yetet.
Et ce sont ici les noms des Ducs d'Esaü selon leurs familles, selon leurs lieux, selon leurs noms: le Duc Timnah, le Duc Halva, le Duc Jéteth.
41 Oholibama, Ela, Finon.
Le Duc Aholibama, le Duc Ela, le Duc Pinon.
42 Kenaz, Teman, Mibzar.
Le Duc Kénaz, le Duc Téman, le Duc Mibtsar,
43 Magdiyel da Iram. Waɗannan su ne manyan Edom bisa ga mazauninsu cikin ƙasar da suka zauna. Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom.
Le Duc Magdiel, et le Duc Hiram. Ce sont là les Ducs d'Edom selon leurs demeures du pays de leur possession. C'est Esaü le père d'Edom.

< Farawa 36 >