< Farawa 36 >
1 Waɗannan su ne zuriyar Isuwa (wato, Edom).
These are the generations of Esau which is called Edo.
2 Isuwa ya ɗauko matansa daga cikin matan Kan’ana, ya ɗauko Ada’yar Elon mutumin Hitti, da Oholibama’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon Bahiwiye
Esau toke his wyues of the doughters of Canaan Ada the doughter of Elon an Hethite and Ahalibama the doughter of Ana which Ana was the sonne of Zibeon an heuyte
3 ya kuma auri Basemat’yar Ishmayel wadda take’yar’uwar Nebayiwot.
And Basmath Ismaels doughter and sister of Nebaioth.
4 Ada ta haifi wa Isuwa, Elifaz. Basemat kuma ta haifa masa Reyuwel.
And Ada bare vnto Esau Eliphas: and Basmath bare Reguel:
5 Oholibama kuwa ta haifa masa Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza, waɗanda aka haifa masa a Kan’ana.
And Ahalibama bare Ieus Iaelam and Rorah. These are the sonnes of Esau which were borne him in the lande of Canaan.
6 Isuwa ya ɗauki matansa da’ya’yansa maza da mata da kuma dukan membobin gidansa, ya kuma ɗauki shanunsa da dukan sauran dabbobinsa, da dukan dukiyarsa da ya samu a ƙasar Kan’ana zuwa wata ƙasa nesa da ɗan’uwansa Yaƙub.
And Esau toke his wyues his sonnes and doughters and all the soules of his house: his goodes and all his catell and all his substance which he had gott in the land of Canaan ad went in to a countre awaye from his brother Iacob:
7 Mallakarsu ta yi yawa ƙwarai da ba za su iya zauna tare ba; gama ƙasar da suke zaune a ciki ba za tă ishe su su biyu ba saboda dabbobinsu.
for their ryches was so moch that they coude not dwell together and that the land where in they were straungers coude not receaue the: because of their catell.
8 Saboda haka Isuwa (wato, Edom) ya zauna a ƙasar tuddai na Seyir.
Thus dwelt Esau in moute Seir which Esau is called Edo
9 Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom, a ƙasar tuddai na Seyir.
These are the generations of Esau father of the Edomytes in mounte Seir
10 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isuwa maza, Elifaz, ɗan Ada matar Isuwa, da Reyuwel ɗan Basemat matar Isuwa.
and these are the names of Esaus sonnes: Eliphas the sonne of Ada the wife of Esau ad Reguel the sonne of Basmath the wife of Esau also.
11 ’Ya’yan Elifaz maza su ne, Teman, Omar, Zefo, Gatam da Kenaz.
And the sonnes of Eliphas were. Theman Omar Zepho Gactham and kenas.
12 Elifaz ɗan Isuwa kuma yana da ƙwarƙwara mai suna Timna, wadda ta haifa masa Amalek. Waɗannan su ne jikokin Ada matar Isuwa.
And thimna was concubyne to Eliphas Esaus sonne and bare vnto Eliphas Amalech. And these be the sonnes of Ada Esaus wyfe.
13 ’Ya’yan Reyuwel maza su ne, Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
And these are the sonnes of Reguel: Nahath Serah Samma and Misa: these were the sonnes of Basmath Esaus wyfe.
14 ’Ya’yan Oholibama maza’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon, matar Isuwa, waɗanda ta haifa wa Isuwa su ne, Yewush, Yalam da Kora.
And these were the sonnes of Ahalibama Esaus wyfe the doughter of Ana sonne of Zebeo which she bare vnto Esau: Ieus Iealam and Korah.
15 Waɗannan su ne manya a cikin zuriyar Isuwa,’Ya’ya Elifaz maza ɗan farin Isuwa, Shugabannin su ne; Teman, Omar, Zefo, Kenaz,
These were dukes of the sonnes of Esau. The childern of Eliphas the first sone of Esau were these: duke Theman duke Omar duke Zepho duke Kenas
16 Kora, Gatam da kuma Amalek. Waɗannan ne manya da suka fito daga dangin Elifaz a Edom; su ne jikokin Ada.
duke Korah duke Gaetham and duke Amalech: these are ye dukes that came of Eliphas in the lande of Edom ad these were the sonnes of Ada.
17 ’Ya’yan Reyuwel maza, Shugabannin su ne; Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Reyuwel a Edom; su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
These were the childern of Requel. Esaus sonne: duke Nahath duke Serah duke Samma duke Misa. These are the dukes that came of Reguel in the lande of Edom ad these were the sonnes of Basmath Esaus wyfe.
18 ’Ya’yan Oholibama maza matar Isuwa, Shugabannin su ne; Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Oholibama’yar Ana matar Isuwa.
These were the childern of Ahalibama Esaus wife: duke Ieus duke Iaelam duke Korah these dukes came of Ahalibama ye doughter of Ana Esaus wife.
19 Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza (wato, Edom), waɗannan ne manyansu.
These are the childern of Esau and these are the dukes of them: which Esau is called Edom:
20 Waɗannan su ne’ya’yan Seyir Bahore maza, waɗanda suke zaune a yankin, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
These are the childern of Seir the Horite the in habitoure of the lande: Lothan Sobal Zibeon Ana
21 Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa,’ya’yan Seyir, maza, a ƙasar Edom.
Dison Eser and Disan. These are the dukes of ye horites the childern of Seir in the lande of Edom.
22 ’Ya’yan Lotan maza su ne, Hori da Homam. Timna’yar’uwar Lotan ce.
And the childern of Lothan were: Hori and Hemam. And Lothans sister was called Thimna.
23 ’Ya’yan Shobal maza su ne, Alwan, Manahat, Ebal, Shefo da Onam.
The childern of Sobal were these: Alvan Manahath Ebal Sepho and Onam.
24 ’Ya’yan Zibeyon maza su ne, Aiya da Ana. Wannan shi ne Ana wanda ya sami maɓulɓulan ruwan zafi a hamada yayinda yake kiwon jakuna na mahaifinsa Zibeyon.
These were the childern of Zibeo. Aia and ana this was yt Ana yt foude ye mules in ye wildernes as he fed his father Zibeons asses.
25 ’Ya’yan Ana su ne, Dishon da Oholibama’yar Ana.
The childern of Ana were these. Dison and Ahalibama ye doughter of Ana.
26 ’Ya’yan Dishon maza su ne, Hemdan, Eshban, Itran da Keran.
These are the childern of Dison. Hemdan Esban Iethran and Chera.
27 ’Ya’yan Ezer maza su ne, Bilhan, Za’aban da Akan.
The childern of Ezer were these Bilhan Seavan and Akan.
28 ’Ya’yan Dishan maza su ne, Uz da Aran.
The childern of Disan were: Vzand Aran.
29 Waɗannan su ne manyan Horiyawa, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
These are the dukes that came of Hori: duke Lothan duke Sobal duke Zibeo duke Ana
30 Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa, bisa ga ɓangarorinsu, a ƙasar Seyir.
duke Dison duke Ezer duke Disan. These be the dukes that came of Hory in their dukedos in the land of Seir.
31 Waɗannan su ne sarakunan da suka yi mulki a Edom kafin wani sarki mutumin Isra’ila yă yi mulki,
These are the kynges that reigned in the lande of Edom before there reigned any kynge amonge the childern of Israel.
32 Bela ɗan Beyor ya zama sarkin Edom. Sunan birninsa shi ne Dinhaba.
Bela the sonne of Beor reigned in Edomea and the name of his cyte was Dinhaba.
33 Sa’ad da Bela ya rasu, Yobab ɗan Zera daga Bozra ya gāje shi.
And when Bela dyed Iobab the sonne of Serah out of Bezara reigned in his steade.
34 Sa’ad da Yobab ya rasu, Husham daga ƙasar Temaniyawa ya gāje shi.
When Iobab was dead Husam of the lande of Themany reigned in his steade.
35 Sa’ad da Husham ya rasu, Hadad ɗan Bedad, wanda ya ci Midiyan da yaƙi a ƙasar Mowab, ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Awit.
And after the deth of Husam Hadad the sonne of Bedad which stewe the Madianytes in the feld of the Moabytes reigned in his steade and the name of his cyte was Avith.
36 Sa’ad da Hadad ya rasu, Samla daga Masreka ya gāje shi.
Whe Hadad was dead Samla of Masteka reigned in his steade.
37 Sa’ad da Samla ya rasu, Sha’ul daga Rehobot na ta kogi ya gāje shi.
Whe Samla was dead Saul of the ryver Rehoboth reigned in his steade.
38 Sa’ad da Sha’ul ya rasu, Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya gāje shi.
When Saul was dead Baalhanan the sonne of Achbor reigned in his steade.
39 Sa’ad da Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya rasu, Hadad ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Fau, kuma sunan matarsa Mehetabel ce’yar Matired, jikanyar Me-Zahab.
And after the deth of Baal Hanan the sonne of Achbor Hadad reigned in his steade and the name of his cyte was Pagu. And his wifes name Mehetabeel the doughter of matred the doughter of Mesaab.
40 Waɗannan su ne manya da suka fito daga zuriyar Isuwa, bisa ga danginsu, bisa kuma ga kabilansu da yankunansu. Sunayensu su ne, Timna, Alwa, Yetet.
These are the names of the dukes that came of Esau in their kynreddds places and names: Duke Thimma duke Alua duke Ietheth
41 Oholibama, Ela, Finon.
duke Ahalibama duke Ela duke Pinon
duke Kenas duke Theman duke Mibzar
43 Magdiyel da Iram. Waɗannan su ne manyan Edom bisa ga mazauninsu cikin ƙasar da suka zauna. Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom.
duke Magdiel duke Iram. These be the dukes of Edomea in their habitations in the lande of their possessions. This Esau is the father of the Edomytes.