< Farawa 36 >
1 Waɗannan su ne zuriyar Isuwa (wato, Edom).
And these [are] [the] accounts of Esau that [is] Edom.
2 Isuwa ya ɗauko matansa daga cikin matan Kan’ana, ya ɗauko Ada’yar Elon mutumin Hitti, da Oholibama’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon Bahiwiye
Esau he took wives his from [the] daughters of Canaan Adah [the] daughter of Elon the Hittite and Oholibamah [the] daughter of Anah [the] daughter of Zibeon the Hivite.
3 ya kuma auri Basemat’yar Ishmayel wadda take’yar’uwar Nebayiwot.
And Basemath [the] daughter of Ishmael [the] sister of Nebaioth.
4 Ada ta haifi wa Isuwa, Elifaz. Basemat kuma ta haifa masa Reyuwel.
And she bore Adah to Esau Eliphaz and Basemath she bore Reuel.
5 Oholibama kuwa ta haifa masa Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza, waɗanda aka haifa masa a Kan’ana.
And Oholibamah she bore (Jeush *Q(K)*) and Jalam and Korah these [were] [the] sons of Esau who they were born to him in [the] land of Canaan.
6 Isuwa ya ɗauki matansa da’ya’yansa maza da mata da kuma dukan membobin gidansa, ya kuma ɗauki shanunsa da dukan sauran dabbobinsa, da dukan dukiyarsa da ya samu a ƙasar Kan’ana zuwa wata ƙasa nesa da ɗan’uwansa Yaƙub.
And he took Esau wives his and sons his and daughters his and all [the] people of household his and livestock his and all animal[s] his and all possession[s] his which he had accumulated in [the] land of Canaan and he went to a land [away] from before Jacob brother his.
7 Mallakarsu ta yi yawa ƙwarai da ba za su iya zauna tare ba; gama ƙasar da suke zaune a ciki ba za tă ishe su su biyu ba saboda dabbobinsu.
For it was possession[s] their [too] much for dwelling together and not it was able [the] land of sojournings their to support them because of livestock their.
8 Saboda haka Isuwa (wato, Edom) ya zauna a ƙasar tuddai na Seyir.
And he dwelt Esau in [the] hill country of Seir Esau that [is] Edom.
9 Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom, a ƙasar tuddai na Seyir.
And these [are] [the] accounts of Esau [the] ancestor of Edom in [the] hill country of Seir.
10 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isuwa maza, Elifaz, ɗan Ada matar Isuwa, da Reyuwel ɗan Basemat matar Isuwa.
These [are] [the] names of [the] sons of Esau Eliphaz [the] son of Adah [the] wife of Esau Reuel [the] son of Basemath [the] wife of Esau.
11 ’Ya’yan Elifaz maza su ne, Teman, Omar, Zefo, Gatam da Kenaz.
And they were [the] sons of Eliphaz Teman Omar Zepho and Gatam and Kenaz.
12 Elifaz ɗan Isuwa kuma yana da ƙwarƙwara mai suna Timna, wadda ta haifa masa Amalek. Waɗannan su ne jikokin Ada matar Isuwa.
And Timna - she was a concubine of Eliphaz [the] son of Esau and she bore to Eliphaz Amalek these [were] [the] sons of Adah [the] wife of Esau.
13 ’Ya’yan Reyuwel maza su ne, Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
And these [were] [the] sons of Reuel Nahath and Zerah Shammah and Mizzah these they were [the] sons of Basemath [the] wife of Esau.
14 ’Ya’yan Oholibama maza’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon, matar Isuwa, waɗanda ta haifa wa Isuwa su ne, Yewush, Yalam da Kora.
And these they were [the] sons of Oholibamah [the] daughter of Anah [the] daughter of Zibeon [the] wife of Esau and she bore to Esau (Jeush *Q(K)*) and Jalam and Korah.
15 Waɗannan su ne manya a cikin zuriyar Isuwa,’Ya’ya Elifaz maza ɗan farin Isuwa, Shugabannin su ne; Teman, Omar, Zefo, Kenaz,
These [were] [the] chiefs of [the] sons of Esau [the] sons of Eliphaz [the] firstborn of Esau chief Teman chief Omar chief Zepho chief Kenaz.
16 Kora, Gatam da kuma Amalek. Waɗannan ne manya da suka fito daga dangin Elifaz a Edom; su ne jikokin Ada.
Chief Korah chief Gatam chief Amalek these [were] [the] chiefs of Eliphaz in [the] land of Edom these [were] [the] sons of Adah.
17 ’Ya’yan Reyuwel maza, Shugabannin su ne; Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Reyuwel a Edom; su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
And these [were] [the] sons of Reuel [the] son of Esau chief Nahath chief Zerah chief Shammah chief Mizzah these [were] [the] chiefs of Reuel in [the] land of Edom these [were] [the] sons of Basemath [the] wife of Esau.
18 ’Ya’yan Oholibama maza matar Isuwa, Shugabannin su ne; Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Oholibama’yar Ana matar Isuwa.
And these [were] [the] sons of Oholibamah [the] wife of Esau chief Jeush chief Jalam chief Korah these [were] [the] chiefs of Oholibamah [the] daughter of Anah [the] wife of Esau.
19 Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza (wato, Edom), waɗannan ne manyansu.
These [were] [the] sons of Esau and these [were] chiefs their that [is] Edom.
20 Waɗannan su ne’ya’yan Seyir Bahore maza, waɗanda suke zaune a yankin, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
These [were] [the] sons of Seir the Horite [the] inhabitants of the land Lotan and Shobal and Zibeon and Anah.
21 Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa,’ya’yan Seyir, maza, a ƙasar Edom.
And Dishon and Ezer and Dishan these [were] [the] chiefs of the Horite[s] [the] sons of Seir in [the] land of Edom.
22 ’Ya’yan Lotan maza su ne, Hori da Homam. Timna’yar’uwar Lotan ce.
And they were [the] sons of Lotan Hori and Hemam and [the] sister of Lotan [was] Timna.
23 ’Ya’yan Shobal maza su ne, Alwan, Manahat, Ebal, Shefo da Onam.
And these [were] [the] sons of Shobal Alvan and Manahath and Ebal Shepho and Onam.
24 ’Ya’yan Zibeyon maza su ne, Aiya da Ana. Wannan shi ne Ana wanda ya sami maɓulɓulan ruwan zafi a hamada yayinda yake kiwon jakuna na mahaifinsa Zibeyon.
And these [were] [the] sons of Zibeon and Aiah and Anah he [was] Anah who he found the hot springs in the wilderness when was pasturing he the donkeys of Zibeon father his.
25 ’Ya’yan Ana su ne, Dishon da Oholibama’yar Ana.
And these [were] [the] children of Anah Dishon and Oholibamah [the] daughter of Anah.
26 ’Ya’yan Dishon maza su ne, Hemdan, Eshban, Itran da Keran.
And these [were] [the] sons of Dishan Hemdan and Eshban and Ithran and Keran.
27 ’Ya’yan Ezer maza su ne, Bilhan, Za’aban da Akan.
These [were] [the] sons of Ezer Bilhan and Zaavan and Akan.
28 ’Ya’yan Dishan maza su ne, Uz da Aran.
These [were] [the] sons of Dishan Uz and Aran.
29 Waɗannan su ne manyan Horiyawa, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
These [were] [the] chiefs of the Horite[s] chief Lotan chief Shobal chief Zibeon chief Anah.
30 Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa, bisa ga ɓangarorinsu, a ƙasar Seyir.
Chief Dishon chief Ezer chief Dishan these [were] [the] chiefs of the Horite[s] to chiefs their in [the] land of Seir.
31 Waɗannan su ne sarakunan da suka yi mulki a Edom kafin wani sarki mutumin Isra’ila yă yi mulki,
And these [were] the kings who they reigned in [the] land of Edom before reigned a king of [the] people of Israel.
32 Bela ɗan Beyor ya zama sarkin Edom. Sunan birninsa shi ne Dinhaba.
And he reigned in Edom Bela [the] son of Beor and [the] name of city his [was] Dinhabah.
33 Sa’ad da Bela ya rasu, Yobab ɗan Zera daga Bozra ya gāje shi.
And he died Bela and he reigned in place of him Jobab [the] son of Zerah from Bozrah.
34 Sa’ad da Yobab ya rasu, Husham daga ƙasar Temaniyawa ya gāje shi.
And he died Jobab and he reigned in place of him Husham from [the] land of the Temanite[s].
35 Sa’ad da Husham ya rasu, Hadad ɗan Bedad, wanda ya ci Midiyan da yaƙi a ƙasar Mowab, ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Awit.
And he died Husham and he reigned in place of him Hadad [the] son of Bedad who defeated Midian in [the] region of Moab and [the] name of city his [was] Avith.
36 Sa’ad da Hadad ya rasu, Samla daga Masreka ya gāje shi.
And he died Hadad and he reigned in place of him Samlah from Masrekah.
37 Sa’ad da Samla ya rasu, Sha’ul daga Rehobot na ta kogi ya gāje shi.
And he died Samlah and he reigned in place of him Shaul from Rehoboth the River.
38 Sa’ad da Sha’ul ya rasu, Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya gāje shi.
And he died Shaul and he reigned in place of him Baal-Hanan [the] son of Achbor.
39 Sa’ad da Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya rasu, Hadad ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Fau, kuma sunan matarsa Mehetabel ce’yar Matired, jikanyar Me-Zahab.
And he died Baal-Hanan [the] son of Achbor and he reigned in place of him Hadar and [the] name of city his [was] Pau and [the] name of wife his [was] Mehetabel [the] daughter of Matred [the] daughter of Me-Zahab.
40 Waɗannan su ne manya da suka fito daga zuriyar Isuwa, bisa ga danginsu, bisa kuma ga kabilansu da yankunansu. Sunayensu su ne, Timna, Alwa, Yetet.
And these [were] [the] names of [the] chiefs of Esau to clans their to places their by names their chief Timna chief Alvah chief Jetheth.
41 Oholibama, Ela, Finon.
Chief Oholibamah chief Elah chief Pinon.
Chief Kenaz chief Teman chief Mibzar.
43 Magdiyel da Iram. Waɗannan su ne manyan Edom bisa ga mazauninsu cikin ƙasar da suka zauna. Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom.
Chief Magdiel chief Iram these - [were] [the] chiefs of Edom to dwelling places their in [the] land of possession their that [was] Esau [the] ancestor of Edom.