< Farawa 36 >

1 Waɗannan su ne zuriyar Isuwa (wato, Edom).
Now these [are] the generations of Esau, who [is] Edom.
2 Isuwa ya ɗauko matansa daga cikin matan Kan’ana, ya ɗauko Ada’yar Elon mutumin Hitti, da Oholibama’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon Bahiwiye
Esau took his wives of the daughters of Canaan; Adah the daughter of Elon the Hittite, and Aholibamah the daughter of Anah the daughter of Zibeon the Hivite;
3 ya kuma auri Basemat’yar Ishmayel wadda take’yar’uwar Nebayiwot.
And Bashemath Ishmael’s daughter, sister of Nebajoth.
4 Ada ta haifi wa Isuwa, Elifaz. Basemat kuma ta haifa masa Reyuwel.
And Adah bare to Esau Eliphaz; and Bashemath bare Reuel;
5 Oholibama kuwa ta haifa masa Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza, waɗanda aka haifa masa a Kan’ana.
And Aholibamah bare Jeush, and Jaalam, and Korah: these [are] the sons of Esau, which were born unto him in the land of Canaan.
6 Isuwa ya ɗauki matansa da’ya’yansa maza da mata da kuma dukan membobin gidansa, ya kuma ɗauki shanunsa da dukan sauran dabbobinsa, da dukan dukiyarsa da ya samu a ƙasar Kan’ana zuwa wata ƙasa nesa da ɗan’uwansa Yaƙub.
And Esau took his wives, and his sons, and his daughters, and all the persons of his house, and his cattle, and all his beasts, and all his substance, which he had got in the land of Canaan; and went into the country from the face of his brother Jacob.
7 Mallakarsu ta yi yawa ƙwarai da ba za su iya zauna tare ba; gama ƙasar da suke zaune a ciki ba za tă ishe su su biyu ba saboda dabbobinsu.
For their riches were more than that they might dwell together; and the land wherein they were strangers could not bear them because of their cattle.
8 Saboda haka Isuwa (wato, Edom) ya zauna a ƙasar tuddai na Seyir.
Thus dwelt Esau in mount Seir: Esau [is] Edom.
9 Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom, a ƙasar tuddai na Seyir.
And these [are] the generations of Esau the father of the Edomites in mount Seir:
10 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isuwa maza, Elifaz, ɗan Ada matar Isuwa, da Reyuwel ɗan Basemat matar Isuwa.
These [are] the names of Esau’s sons; Eliphaz the son of Adah the wife of Esau, Reuel the son of Bashemath the wife of Esau.
11 ’Ya’yan Elifaz maza su ne, Teman, Omar, Zefo, Gatam da Kenaz.
And the sons of Eliphaz were Teman, Omar, Zepho, and Gatam, and Kenaz.
12 Elifaz ɗan Isuwa kuma yana da ƙwarƙwara mai suna Timna, wadda ta haifa masa Amalek. Waɗannan su ne jikokin Ada matar Isuwa.
And Timna was concubine to Eliphaz Esau’s son; and she bare to Eliphaz Amalek: these [were] the sons of Adah Esau’s wife.
13 ’Ya’yan Reyuwel maza su ne, Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
And these [are] the sons of Reuel; Nahath, and Zerah, Shammah, and Mizzah: these were the sons of Bashemath Esau’s wife.
14 ’Ya’yan Oholibama maza’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon, matar Isuwa, waɗanda ta haifa wa Isuwa su ne, Yewush, Yalam da Kora.
And these were the sons of Aholibamah, the daughter of Anah the daughter of Zibeon, Esau’s wife: and she bare to Esau Jeush, and Jaalam, and Korah.
15 Waɗannan su ne manya a cikin zuriyar Isuwa,’Ya’ya Elifaz maza ɗan farin Isuwa, Shugabannin su ne; Teman, Omar, Zefo, Kenaz,
These [were] dukes of the sons of Esau: the sons of Eliphaz the firstborn [son] of Esau; duke Teman, duke Omar, duke Zepho, duke Kenaz,
16 Kora, Gatam da kuma Amalek. Waɗannan ne manya da suka fito daga dangin Elifaz a Edom; su ne jikokin Ada.
Duke Korah, duke Gatam, [and] duke Amalek: these [are] the dukes [that came] of Eliphaz in the land of Edom; these [were] the sons of Adah.
17 ’Ya’yan Reyuwel maza, Shugabannin su ne; Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Reyuwel a Edom; su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
And these [are] the sons of Reuel Esau’s son; duke Nahath, duke Zerah, duke Shammah, duke Mizzah: these [are] the dukes [that came] of Reuel in the land of Edom; these [are] the sons of Bashemath Esau’s wife.
18 ’Ya’yan Oholibama maza matar Isuwa, Shugabannin su ne; Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Oholibama’yar Ana matar Isuwa.
And these [are] the sons of Aholibamah Esau’s wife; duke Jeush, duke Jaalam, duke Korah: these [were] the dukes [that came] of Aholibamah the daughter of Anah, Esau’s wife.
19 Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza (wato, Edom), waɗannan ne manyansu.
These [are] the sons of Esau, who [is] Edom, and these [are] their dukes.
20 Waɗannan su ne’ya’yan Seyir Bahore maza, waɗanda suke zaune a yankin, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
These [are] the sons of Seir the Horite, who inhabited the land; Lotan, and Shobal, and Zibeon, and Anah,
21 Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa,’ya’yan Seyir, maza, a ƙasar Edom.
And Dishon, and Ezer, and Dishan: these [are] the dukes of the Horites, the children of Seir in the land of Edom.
22 ’Ya’yan Lotan maza su ne, Hori da Homam. Timna’yar’uwar Lotan ce.
And the children of Lotan were Hori and Hemam; and Lotan’s sister [was] Timna.
23 ’Ya’yan Shobal maza su ne, Alwan, Manahat, Ebal, Shefo da Onam.
And the children of Shobal [were] these; Alvan, and Manahath, and Ebal, Shepho, and Onam.
24 ’Ya’yan Zibeyon maza su ne, Aiya da Ana. Wannan shi ne Ana wanda ya sami maɓulɓulan ruwan zafi a hamada yayinda yake kiwon jakuna na mahaifinsa Zibeyon.
And these [are] the children of Zibeon; both Ajah, and Anah: this [was that] Anah that found the mules in the wilderness, as he fed the asses of Zibeon his father.
25 ’Ya’yan Ana su ne, Dishon da Oholibama’yar Ana.
And the children of Anah [were] these; Dishon, and Aholibamah the daughter of Anah.
26 ’Ya’yan Dishon maza su ne, Hemdan, Eshban, Itran da Keran.
And these [are] the children of Dishon; Hemdan, and Eshban, and Ithran, and Cheran.
27 ’Ya’yan Ezer maza su ne, Bilhan, Za’aban da Akan.
The children of Ezer [are] these; Bilhan, and Zaavan, and Akan.
28 ’Ya’yan Dishan maza su ne, Uz da Aran.
The children of Dishan [are] these; Uz, and Aran.
29 Waɗannan su ne manyan Horiyawa, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
These [are] the dukes [that came] of the Horites; duke Lotan, duke Shobal, duke Zibeon, duke Anah,
30 Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa, bisa ga ɓangarorinsu, a ƙasar Seyir.
Duke Dishon, duke Ezer, duke Dishan: these [are] the dukes [that came] of Hori, among their dukes in the land of Seir.
31 Waɗannan su ne sarakunan da suka yi mulki a Edom kafin wani sarki mutumin Isra’ila yă yi mulki,
And these [are] the kings that reigned in the land of Edom, before there reigned any king over the children of Israel.
32 Bela ɗan Beyor ya zama sarkin Edom. Sunan birninsa shi ne Dinhaba.
And Bela the son of Beor reigned in Edom: and the name of his city [was] Dinhabah.
33 Sa’ad da Bela ya rasu, Yobab ɗan Zera daga Bozra ya gāje shi.
And Bela died, and Jobab the son of Zerah of Bozrah reigned in his stead.
34 Sa’ad da Yobab ya rasu, Husham daga ƙasar Temaniyawa ya gāje shi.
And Jobab died, and Husham of the land of Temani reigned in his stead.
35 Sa’ad da Husham ya rasu, Hadad ɗan Bedad, wanda ya ci Midiyan da yaƙi a ƙasar Mowab, ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Awit.
And Husham died, and Hadad the son of Bedad, who smote Midian in the field of Moab, reigned in his stead: and the name of his city [was] Avith.
36 Sa’ad da Hadad ya rasu, Samla daga Masreka ya gāje shi.
And Hadad died, and Samlah of Masrekah reigned in his stead.
37 Sa’ad da Samla ya rasu, Sha’ul daga Rehobot na ta kogi ya gāje shi.
And Samlah died, and Saul of Rehoboth [by] the river reigned in his stead.
38 Sa’ad da Sha’ul ya rasu, Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya gāje shi.
And Saul died, and Baal-hanan the son of Achbor reigned in his stead.
39 Sa’ad da Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya rasu, Hadad ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Fau, kuma sunan matarsa Mehetabel ce’yar Matired, jikanyar Me-Zahab.
And Baal-hanan the son of Achbor died, and Hadar reigned in his stead: and the name of his city [was] Pau; and his wife’s name [was] Mehetabel, the daughter of Matred, the daughter of Mezahab.
40 Waɗannan su ne manya da suka fito daga zuriyar Isuwa, bisa ga danginsu, bisa kuma ga kabilansu da yankunansu. Sunayensu su ne, Timna, Alwa, Yetet.
And these [are] the names of the dukes [that came] of Esau, according to their families, after their places, by their names; duke Timnah, duke Alvah, duke Jetheth,
41 Oholibama, Ela, Finon.
Duke Aholibamah, duke Elah, duke Pinon,
42 Kenaz, Teman, Mibzar.
Duke Kenaz, duke Teman, duke Mibzar,
43 Magdiyel da Iram. Waɗannan su ne manyan Edom bisa ga mazauninsu cikin ƙasar da suka zauna. Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom.
Duke Magdiel, duke Iram: these [be] the dukes of Edom, according to their habitations in the land of their possession: he [is] Esau the father of the Edomites.

< Farawa 36 >