< Farawa 35 >

1 Sa’an nan Allah ya ce wa Yaƙub, “Haura zuwa Betel ka yi zama a can, ka kuma gina bagade a can wa Allah wanda ya bayyana gare ka sa’ad da kake gudu daga ɗan’uwanka Isuwa.”
OLELO mai la ke Akua ia Iakoba, E ku ae oe, e pii aku i Betela, ilaila e noho ai: ilaila oe e hana'i i kuahu no ke Akua i ikea e oe i kou wa i mahuka ai mai ka maka o kou kaikuaana o Esau.
2 Saboda haka Yaƙub ya ce wa gidansa da kuma dukan waɗanda suke tare da shi, “Ku zubar da baƙin allolin da kuke da su, ku tsarkake kanku, ku kuma canja tufafinku.
Alaila, i aku la o Iakoba i ko ka hale ona, a i ka poe a pau me ia, E haalele oukou i na akua e iwaena o oukou, e huikala ia oukou iho, a e aahu iho i na kapa hou:
3 Sa’an nan ku zo, mu haura zuwa Betel, inda zan gina bagade wa Allah wanda ya amsa mini a ranar wahalata, wanda kuma ya kasance tare da ni a dukan inda na tafi.”
A e ku ae kakou, e pii aku i Betela; malaila au e hana'i i kuahu no ke Akua nana au i maliu mai i ka la o ko'u popilikia, a i hele pu me au i kuu ala i hele ai.
4 Saboda haka suka ba Yaƙub dukan baƙin allolin da suke da su, da zoban da suke kunnuwansu, sai Yaƙub ya binne su a ƙarƙashin itacen oak a Shekem.
Haawi mai la lakou ia Iakoba i na akua e ma ko lakou lima, a me na apo ma na pepeiao o lakou: a huna iho la o Iakoba ia mau mea malalo o ka laau oka aia ma Sekema.
5 Sa’an nan suka kama hanya, tsoron Allah kuwa ya kama dukan garuruwan da suke kewayensu har babu wanda ya iya bin su.
Hele aku la lakou: a kau mai la ka weliweli mai ke Akua mai maluna o na kulanakauhale ma kela aoao a keia aoao o lakou, a alualu ole mai la lakou i na keiki o Iakoba.
6 Yaƙub da dukan mutanen da suke tare da shi suka zo Luz (wato, Betel) a ƙasar Kan’ana.
A hiki aku la o Iakoba ia Luza, oia hoi o Betela, ma ka aina o Kanaana, oia a me na kanaka a pau me ia.
7 A can ya gina bagade, ya kuma kira wurin El Betel, gama a can ne Allah ya bayyana kansa gare shi sa’ad da yake gudu daga ɗan’uwansa.
Hana iho la ia i kuahu malaila, a kapa iho la ia wahi o i Ele-betela: no ka mea, ilaila ke Akua i ikea ai e ia i kona wa i mahuka ai mai ka maka aku o kona kaikuaana.
8 To, Debora, ungozomar Rebeka ta rasu aka kuma binne ta a ƙarƙashin itacen oak, ƙasa da Betel. Saboda haka aka kira wurin Allon Bakut.
Make iho la o Debora o ke kahu no Rebeka, a ua kanuia oia malalo o Betela malalo o kekahi laau oka: a ua kapaia ka inoa o ia wahi, o i Alona-bakuta.
9 Bayan Yaƙub ya komo daga Faddan Aram, sai Allah ya bayyana gare shi, ya kuma albarkace shi.
Ikea hou ke Akua e Iakoba, i kona hoi ana mai, noloko mai o Padanarama, a hoomaikai mai la ia ia.
10 Allah ya ce masa, “Sunanka Yaƙub ne, amma ba za a ƙara kira ka Yaƙub ba; sunanka zai zama Isra’ila.” Saboda haka ya ba shi suna Isra’ila.
I mai la ke Akua ia ia, O Iakoba kou inoa: aole e hea hou ia kou inoa o Iakoba, aka, o Iseraela kou inoa: a kapa iho la oia i kona inoa o Iseraela.
11 Sai Allah ya ce masa, “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi ta haihuwa, ka kuma riɓaɓɓanya. Al’umma da tarin al’ummai za su fito daga gare ka, sarakuna kuma za su fito daga jikinka.
I mai la ke Akua ia ia, Owau no ke Akua Mana: a e hoohua ae oe, a e mahuahua; nau mai no kekahi lahuikanaka, a me na lahuikanaka; a e puka mai auanei na alii mailoko mai o kou puhaka;
12 Ƙasar da na ba wa Ibrahim da Ishaku, zan kuma ba ka, zan kuma ba da wannan ƙasa ga zuriyarka a bayanka.”
A o ka aina a'u i haawi aku ai no Aberahama, a no Isaaka, e haawi aku hoi au nou, a no kau poe mamo mahope ou ka'u e haawi aku ai i ka aina.
13 Sa’an nan Allah ya tashi sama daga gare shi a wurin da ya yi magana da shi.
A pii aku la ke Akua iluna mai ona aku la, ma kahi ana i kamailio pu ai me ia.
14 Yaƙub kuwa ya kafa al’amudin dutse a inda Allah ya yi magana da shi, ya zuba hadaya ta sha a kansa; ya kuma zuba mai a kansa.
Hooku ae la o Iakoba i eho ma kahi ana i kamailio mai ai me ia, he eho pohaku: a ninini iho la ia i ka mohaiinu maluna; a ninini iho la hoi oia i ka aila maluna.
15 Yaƙub ya kira inda Allah ya yi magana da shi, Betel.
Kapa iho la o Iakoba i ka aina o kahi a ke Akua i olelo mai ai me ia, o Betela.
16 Sa’an nan suka tashi daga Betel. Yayinda suna da ɗan nisa da Efrat, sai Rahila ta fara naƙuda ta kuwa sha wahala sosai.
Hele aku la lakou mai Betela aku, a ua kokoke e hiki i Eperata, haakohi iho la o Rahela, a puua iho i ka hanau keiki ana.
17 Sa’ad da take cikin zafin haihuwa, sai macen da ta karɓi haihuwar ta ce mata, “Kada ki ji tsoro, gama yanzu kin sami wani ɗa.”
A i kona puua ana, i aku la ka pale keiki ia ia, Mai makau oe, e loaa auanei ia oe keia keiki no hoi.
18 Yayinda take jan numfashinta na ƙarshe, sai ta ba wa ɗanta suna Ben-Oni. Amma mahaifinsa ya kira shi Benyamin.
A i ka wa e kaili ana kona ea, (no ka mea, make no oia, ) kapa iho la ia i kona inoa, i Benoni: aka, kapa aka la kona makuakane ia ia, o Beniamina.
19 Ta haka Rahila ta rasu, aka kuma binne ta a hanya zuwa Efrata (wato, Betlehem).
Make iho la o Rahela, a kanuia oia ma ke alanui e hele ai i Eperata, oia o Betelehema.
20 Yaƙub ya kafa al’amudi bisa kabarinta, al’amudin kabarin Rahila ke nan, wanda yake can har wa yau.
Hooku ae la o Iseraela, i pohaku eho maluna o kona he, oia ka eho no ka he o Rahela, a hiki i keia manawa.
21 Isra’ila ya yi gaba, ya kafa tentinsa gaba da Migdal Eder.
Hele aku la o Iseraela, a kukulu iho la i kona halelewa ma o aku o ka halekiai o Edara.
22 Yayinda Isra’ila yana zama a wancan yanki, Ruben ya shiga ya kwana da Bilha ƙwarƙwarar mahaifinsa, Isra’ila kuwa ya ji labari. Yaƙub ya haifi’ya’ya maza goma sha biyu.
A i ka noho ana o Iseraela ma ia aina, hele aka la o Reubena, a moe pu iho la me Bileha me ka haiawahine a kona makuakane; a lohe ae la o Iseraela. O na keikikane a Iakoba he umikumamalua:
23 ’Ya’yan Liyatu maza, Ruben shi ne ɗan fari na Yaƙub. Sauran su ne, Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar da Zebulun.
O na keikikane a Lea; o Reubena ka makahiapo a Iakoba, o Simeona, o Levi, o Iuda, o Isakara, a o Zebuluna.
24 ’Ya’yan Rahila maza su ne, Yusuf da Benyamin.
O na keikikane a Rahela; o Iosepa, a o Beniamina.
25 ’Ya’yan Bilha maza, mai hidimar Rahila su ne, Dan da Naftali.
O na keikikane a Bileha, a ke kauwawahine a Rahela; o Dana, a o Napetali.
26 ’Ya’yan Zilfa maza, mai hidimar Liyatu su ne, Gad da Asher. Waɗannan su ne’ya’yan Yaƙub maza, waɗanda aka haifa masa a Faddan Aram.
O na keikikane a Zilepa, a ke kauwawahine a Lea; o Gada a o Asera. O lakou na keikikane a Iakoba, i hanau nana ma Padanarama.
27 Yaƙub ya dawo gida wurin mahaifinsa Ishaku a Mamre, kusa da Kiriyat Arba (wato, Hebron), inda Ibrahim da Ishaku suka zauna.
Hele aku la o Iakoba i kona makuakane ia Isaaka ma Mamere, ma ke kulanakauhale o Areba, (oia o Heberona, ) kahi i noho ai o Aberahama a me Isaaka.
28 Ishaku ya rayu shekaru ɗari da tamanin,
A o na la o Isaaka, hookahi haneri makahiki a me kanawalu.
29 sa’an nan ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuwa mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa da kyakkyawan tsufa da kuma cikakken shekaru.’Ya’yansa maza, Isuwa da Yaƙub suka binne shi.
Kuu aku la o Isaaka i ka uhane, a make iho la, a ua huiia'ku ia me kona poe kanaka: ua elemakule ia, a nui loa kona mau la: na kana mau keikikane na Esau ma laua o Iakoba oia i kanu.

< Farawa 35 >