< Farawa 35 >

1 Sa’an nan Allah ya ce wa Yaƙub, “Haura zuwa Betel ka yi zama a can, ka kuma gina bagade a can wa Allah wanda ya bayyana gare ka sa’ad da kake gudu daga ɗan’uwanka Isuwa.”
Et Dieu dit à Jacob: Lève-toi, monte à Béthel, et demeures-y, et fais-y un autel au Dieu qui t'apparut lorsque tu fuyais de devant Ésaü, ton frère.
2 Saboda haka Yaƙub ya ce wa gidansa da kuma dukan waɗanda suke tare da shi, “Ku zubar da baƙin allolin da kuke da su, ku tsarkake kanku, ku kuma canja tufafinku.
Alors Jacob dit à sa famille, et à tous ceux qui étaient avec lui: Otez les dieux étrangers qui sont au milieu de vous, et purifiez-vous, et changez de vêtements;
3 Sa’an nan ku zo, mu haura zuwa Betel, inda zan gina bagade wa Allah wanda ya amsa mini a ranar wahalata, wanda kuma ya kasance tare da ni a dukan inda na tafi.”
Et levons-nous, et montons à Béthel, et j'y ferai un autel au Dieu qui m'a répondu au jour de ma détresse, et qui a été avec moi pendant mon voyage.
4 Saboda haka suka ba Yaƙub dukan baƙin allolin da suke da su, da zoban da suke kunnuwansu, sai Yaƙub ya binne su a ƙarƙashin itacen oak a Shekem.
Alors ils donnèrent à Jacob tous les dieux étrangers qu'ils avaient, et les anneaux qui étaient à leurs oreilles; et Jacob les enterra sous le chêne qui était près de Sichem.
5 Sa’an nan suka kama hanya, tsoron Allah kuwa ya kama dukan garuruwan da suke kewayensu har babu wanda ya iya bin su.
Ensuite ils partirent. Et Dieu frappa de terreur les villes qui étaient autour d'eux; et ils ne poursuivirent point les fils de Jacob.
6 Yaƙub da dukan mutanen da suke tare da shi suka zo Luz (wato, Betel) a ƙasar Kan’ana.
Et Jacob vint à Luz, qui est au pays de Canaan (c'est Béthel), lui et tout le peuple qui était avec lui.
7 A can ya gina bagade, ya kuma kira wurin El Betel, gama a can ne Allah ya bayyana kansa gare shi sa’ad da yake gudu daga ɗan’uwansa.
Et il y bâtit un autel, et il appela ce lieu: El-Béthel (Dieu de Béthel); car c'est là que Dieu lui était apparu, lorsqu'il fuyait de devant son frère.
8 To, Debora, ungozomar Rebeka ta rasu aka kuma binne ta a ƙarƙashin itacen oak, ƙasa da Betel. Saboda haka aka kira wurin Allon Bakut.
Et Débora, nourrice de Rébecca, mourut; et elle fut ensevelie au-dessous de Béthel, sous le chêne, qu'on appela Allon-Bacuth (chêne des pleurs).
9 Bayan Yaƙub ya komo daga Faddan Aram, sai Allah ya bayyana gare shi, ya kuma albarkace shi.
Et Dieu apparut encore à Jacob, lorsqu'il venait de Paddan-Aram; et il le bénit.
10 Allah ya ce masa, “Sunanka Yaƙub ne, amma ba za a ƙara kira ka Yaƙub ba; sunanka zai zama Isra’ila.” Saboda haka ya ba shi suna Isra’ila.
Et Dieu lui dit: Ton nom est Jacob; tu ne seras plus appelé Jacob, mais Israël sera ton nom. Et il lui donna le nom d'Israël.
11 Sai Allah ya ce masa, “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi ta haihuwa, ka kuma riɓaɓɓanya. Al’umma da tarin al’ummai za su fito daga gare ka, sarakuna kuma za su fito daga jikinka.
Et Dieu lui dit: Je suis le Dieu Tout-Puissant: augmente et multiplie. Une nation, même une multitude de nations naîtront de toi; des rois sortiront de tes reins.
12 Ƙasar da na ba wa Ibrahim da Ishaku, zan kuma ba ka, zan kuma ba da wannan ƙasa ga zuriyarka a bayanka.”
Et je te donnerai le pays que j'ai donné à Abraham et à Isaac, et je donnerai ce pays à ta postérité après toi.
13 Sa’an nan Allah ya tashi sama daga gare shi a wurin da ya yi magana da shi.
Et Dieu remonta d'avec lui, du lieu où il lui avait parlé.
14 Yaƙub kuwa ya kafa al’amudin dutse a inda Allah ya yi magana da shi, ya zuba hadaya ta sha a kansa; ya kuma zuba mai a kansa.
Et Jacob dressa un monument au lieu où il lui avait parlé, un monument de pierre, et il fit dessus une aspersion, et y versa de l'huile.
15 Yaƙub ya kira inda Allah ya yi magana da shi, Betel.
Et Jacob appela le lieu où Dieu lui avait parlé, Béthel (maison de Dieu).
16 Sa’an nan suka tashi daga Betel. Yayinda suna da ɗan nisa da Efrat, sai Rahila ta fara naƙuda ta kuwa sha wahala sosai.
Et ils partirent de Béthel, et il y avait encore un espace de pays pour arriver à Éphrath, lorsque Rachel enfanta; et elle eut beaucoup de peine à accoucher.
17 Sa’ad da take cikin zafin haihuwa, sai macen da ta karɓi haihuwar ta ce mata, “Kada ki ji tsoro, gama yanzu kin sami wani ɗa.”
Et comme elle avait beaucoup de peine à accoucher, la sage-femme lui dit: Ne crains point, car tu as encore un fils.
18 Yayinda take jan numfashinta na ƙarshe, sai ta ba wa ɗanta suna Ben-Oni. Amma mahaifinsa ya kira shi Benyamin.
Et comme elle rendait l'âme, car elle mourut, elle le nomma Bénoni (fils de ma douleur); mais son père l'appela Benjamin (fils de la droite).
19 Ta haka Rahila ta rasu, aka kuma binne ta a hanya zuwa Efrata (wato, Betlehem).
Rachel mourut donc, et fut ensevelie au chemin d'Éphrath, qui est Bethléhem.
20 Yaƙub ya kafa al’amudi bisa kabarinta, al’amudin kabarin Rahila ke nan, wanda yake can har wa yau.
Et Jacob dressa un monument sur sa tombe; c'est le monument de la tombe de Rachel, qui subsiste encore aujourd'hui.
21 Isra’ila ya yi gaba, ya kafa tentinsa gaba da Migdal Eder.
Puis Israël partit, et il dressa sa tente au delà de Migdal-Eder (tour du troupeau).
22 Yayinda Isra’ila yana zama a wancan yanki, Ruben ya shiga ya kwana da Bilha ƙwarƙwarar mahaifinsa, Isra’ila kuwa ya ji labari. Yaƙub ya haifi’ya’ya maza goma sha biyu.
Et il arriva, pendant qu'Israël demeurait dans ce pays-là, que Ruben vint et coucha avec Bilha, concubine de son père; et Israël l'apprit. Or, Jacob avait douze fils.
23 ’Ya’yan Liyatu maza, Ruben shi ne ɗan fari na Yaƙub. Sauran su ne, Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar da Zebulun.
Les fils de Léa: Ruben, premier-né de Jacob, Siméon, Lévi, Juda, Issacar et Zabulon.
24 ’Ya’yan Rahila maza su ne, Yusuf da Benyamin.
Les fils de Rachel: Joseph et Benjamin.
25 ’Ya’yan Bilha maza, mai hidimar Rahila su ne, Dan da Naftali.
Les fils de Bilha, servante de Rachel: Dan et Nephthali.
26 ’Ya’yan Zilfa maza, mai hidimar Liyatu su ne, Gad da Asher. Waɗannan su ne’ya’yan Yaƙub maza, waɗanda aka haifa masa a Faddan Aram.
Et les fils de Zilpa, servante de Léa: Gad et Asser. Ce sont là les fils de Jacob, qui lui naquirent à Paddan-Aram.
27 Yaƙub ya dawo gida wurin mahaifinsa Ishaku a Mamre, kusa da Kiriyat Arba (wato, Hebron), inda Ibrahim da Ishaku suka zauna.
Et Jacob vint vers Isaac son père, à Mamré, à Kirjath-Arba, qui est Hébron, où avaient séjourné Abraham et Isaac.
28 Ishaku ya rayu shekaru ɗari da tamanin,
Et les jours d'Isaac furent de cent quatre-vingts ans.
29 sa’an nan ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuwa mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa da kyakkyawan tsufa da kuma cikakken shekaru.’Ya’yansa maza, Isuwa da Yaƙub suka binne shi.
Et Isaac expira et mourut, et fut recueilli vers ses peuples, âgé et rassasié de jours; et Ésaü et Jacob, ses fils, l'ensevelirent.

< Farawa 35 >